Chapter 15
Chapter 15
yi tana "Abban Nusrah ka manta bani da tsarki ban gama haila ba" A madadin ya saketa sai ya Kara jawo ta, ya cigaba da shafa ta take hankalin ta ya tashi,dan taga nutsuwa yake so ya samu da ita,dan iya sanin ta idan har tana jini ko tab'ata baya yi har sai tayi wanka dan ko a bukace yake baya wani bari ayi Masa dabaru yafiso ya samu nutsuwa da kyau. Abinda ya daga Mata hankali yasa ta fara Neman k'ok'awa dashi bai Wuce kicin kicin cire mata wando da ya fara ba da Kuma iya karfin sa hakane yasa Sajeeda ta saki sallati da k'arfi ta fara k'ok'arin hana shi tana "Abban Nusrah kana cikin hayyacin ka kuwa?Ina jini zaka nemeni"? Bai ko saurareta ba ya fara k'ok'arin shigarta Yana dab da shigarta ta gartsa masa cizo ya saketa da sauri ta ture shi ta mik'e tana "Kabiru wai Mai yake damun ka"? Mai ke faruwa ne"? Kabiru bana gane maka kabiru da ba haka kake ba daga haduwar ka da abokin ka ka canza gabad'aya Kabiru ka fadamin Mai ya canza ka,dare daya ka fara tunanin nemana ta baya, Kabiru ka daina sallah akan lokaci,yanzu Kabiru Ina jini kazo zaka nemeni,Kabiru muna bacci ka saci jiki ka fita, Kabiru ka fara bani tsoro wai Mai ya same ka haka a Ina ka kwaso wadanan sababin dabiun?abinda ba ka yi kana saurayi ba sai a yanzu da ka manyanta zaka yi"? Ta fashe da kuka dan a yanzu Kabiru tsoro yake bata. Ta Kuma rasa dame zata danganta wanan halayen daya tsiro mata dashi Kabiru kuwa wani irin kallo yake mata na takaici abinda dai baya so yayi Sajeeda zata tilasta masa tayi akan dole zai yi abinda yake tsoron tunda duk abinda akace yayi bai samu hadin kai daga wajen Sajeeda ba. Mik'ewa yayi ya shige bandaki ya daura alawalar sai yake jin sa ma kamar ba musulmi ba yau kwana biyar kenan bai yi sallah ba hakan na matukar damun shi amma idan ya tuna mugun kudin da zai yi sai yaji dan kwana bakwai dai ba wani Abu bane. Haka ya fito batare da ta kalli Sajeeda dake gefen gado tana kuka ba ya fice daga d'akin yayi waje. Ko da ya fita nesa da gidan ya samu waje ya zauna. Bai tab'a fargabar garin Allah ya waye kamar yau ba,baisan ya zai yi da kurman cewar da Annur zai yi ba idan ya tuna duk Yesmeen ta jawo mi shi sai yaji wani mugun tsanar ta. Gari ya fara haske ya hango Saifullahi da Faisal sun fito daga gidan da gudu suna waige waige. Ya riga yasan me ke faruwa ba abinda zai daga musu wanan hankalin sai rashin maganar Annur. Take yaji kirjinsa ya masa nauyi jiki ba kwari ya nufi gidan a daidai lokacin da su Saifullahi Suka hango shi Suka yi wajen sa da gudu suna isowa Suka fara magana a tare "Abba Annur baya iya magana maganar kurame yake"? Sallati ya saki da karfi duk da yasan da kurmancewar amma tabbatuwar kurmancewar ya Kara daga mi shi hankali yayi cikin gidan da gudu. A Palo ya tarar da Sajeeda nata ihun sallati tana jijiga Annur da hawaye ke zubo masa Yana ta k'ok'arin magana amma ba Mai gane mai yake cewa. Kabiru na zuwa ya jawo Annur Yana "Annur Mai ya same ka ya maganar ka ta dawo ta kurame" Annur ya kara maganar kurame Kabiru ya sure shi Yana "su tashi su tafi asibiti su Saifullahi har da hawayen su Sajeeda da Yesmeen kuwa sai kuka suke. Haka Kabiru da Sajeeda suka Kai Annur asibiti akayi ta kashe kudi ana duba Annur aga Mai ya jawo masa kurmancewar. Sai da suka Shafe sati biyu suna jigila Kabiru duk da yasan silar kurmancewar Annur haka ya ringa kashe kudi har sai da aka tabbatar musu da Annur dai ya kurmance baa san mai ya kurmantar dashi ba. Sajeeda kuwa da nasiha da komai ta fara dawowa daidai dan kurmancewar Autan ta ya matukar daga mata hankali. Sai a yanzu ta fara tuno kalar mafarkin da Annur ya ringa fada.mata yanayi kwana biyu kafin kurmancewar sa. A yanzu ta fara yarda akwai matsala a tattare dasu amma bata San Ina matsalar take ba, kurmancewar Annur ya Kara tayar mata da hankali tuni ta zama wani shiru shiru ba ita kadai ba har yaran,Yesmeen kuwa haka zatayi ta kuka idan taga annur nasan magana amma ba Mai ganewa karshen ta sai dai a d'auko Masa takarda yayi rubutu. Kabiru kuwa bayan komai ya lafa bisa umarnin shugaban su dan gudun zargi wata daya bayan komai ya lafa ya cigaba da Abubuwan da aka ce yayi. Duk dare sai yayi tsirara yayi wanka da wani ruwan da ke cikin randa a d'akin bayan gidan daya ajiye Abubuwan sa dan ya samu ya fesawa Yesmeen turaren mantuwa ita Kuma Sajeeda tunda aka Masa aiki akan ta mugun tsoron sa take ji bata iya ma kallon sa ballantana ta tsallake umarnin sa a daidai wanan lokacin ya Kamata ya cima burinsa a wajenta sai dai shugaban su ya hana a yau zai gama mataki na biyun karshe. Na karshen yafi kowane wahala zuciyar sa cike take da tsoro amma idan ya tuno daular da zai samu sai yaga zai daure yayi. Yesmeen Duk dare sai taji motsin Kabiru a bayan d'akin ta Yana Abubuwan sa duk da kashedin da ya zuba Mata bayan Wanda ya mata daya shigo dakinta daddare har makaranta ya bita ya Kara kiranta gefe ya Sha alwashin duk ranar da sirrin sa ya fita sai ya kashe ta dan yasan ba wacce tasan mai yake ciki duk duniyar nan sai ita kadai har wuka ya zaro ya nuna Mata. Ya Kuma yi mata gargadi Kar ta sake ta taba nuna Jin tsoron sa a gaban mutane. A cikin dan wayon ta ta gano tsafi Kabiru ke yi dan ya samu kudi,har ta Kuma fara zargin Yana da hannu a kurmancewar Annur amma bata Isa ta fadawa kowa ba sabida tana so ta tsira da ranta. Rabon ta da baccin dare har ta manta dan idan biyu tayi zata ji ya fito ya fara Abubuwan sa zuciyarta tayi ta raya Mata ta leka shi tana Hana kanta da kyar har mamakin irin baccin da Sajeeda keyi take da duk fitar da yake Bata Jin motsin shi ballantana ta farka. haka zata yi zugum tana tsoron motsawa ma Kar yace ta leko shi. A wanan gab'ar ba abinda take bukata sama da Addu'a. Haka zata kawo baho cikin d'akin da buta,idan ya fara abubuwan sa sai ta mik'e a hankali ta daura alwala ta fara sallah da addu'oi tana rokon Allah kariyarsa a garesu gabad'aya. A yau ma tana Jin sa a bayan d'akin Yana tayi sai taji Kamar ta leka shi sai ta fasa. Ba Kuma kunya washegari zai yi ta Abubuwan sa kamar bashi ba har ya ringa jan su da Hira. A yau duk suna zaune a palo wajen biyar na yamma Kabiru ya dawo gidan da wani katon Kare baki wuluk. Idan akwai abinda Sajeeda ke tsoro a rayuwarta bai Wuce Kare ba Kabiru sai da ya Kai Karen
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111