Chapter 67
Chapter 67
bakin Hali ba,dan lokacin da muke Yara indai na samu Abu ko nuratu haka zatayi ta fushi tana bakin ciki,akwai ranar da naci na biyu a islamiya mahaifinmu ya bani kyautar sabon littafi da fensir,daddare duk muna kwance ba bacci nake ba a kwance nake dan ba wuta da wuri Mu ke kwanciya Ina kwance da Nuratu a katifar dake kasa sai naga ta sauko daga kan gadon ta nufi wajen kayana har zan tashi zauna na fasa sai gashi ta bude akwatin karfen da kayana yake ciki,ta d'auko littafin ta yaga ta karya fensir din ta maida min akwati,har na girma na kasa manta abinda tamin da sai da na girma na gane bakin ciki yasa tamun haka, Haka idan muka samo kyautar abu ni da Nuratu sai ta yaga,ko auren Abban Nusrah da nayi murna take saboda tasan ba Mai kudi bane mijinta yafi shi hali, maganar Abban Nusrah ya katse min tunanin da na tafi,Sajeeda ki sha kunun Mana" "Tun dazu nake fama da ita ta Sha tak'i sha Kuma saboda ita na dama kunun nan" "Ko dai zafine da kunun"? Girgiza kai Yaya Abu ta hau yi tana "Ina fa kunun yaga zafi" Sai ta Kai cokalin bakinta ta fito da harshenta ta dandana tana ba zafi" Sai a lokacin ta tuna dandana kunun tayi ta Kuma hadiye,ta mike da azabar sauri ta fara sallati tana tari da k'arfi tana kakalo amai tayi waje da gudu, Lumshe idona kawai nayi Ina yiwa Annabi sallati,da kanta ta dandana kunun da take so ta kasheni dash,sai Kuma na fashe da kuka dana tabbatar da kasheni dai Yaya Abu ke San yi Abban nusrah kuwa ya bita bakin kofa Yana mata sannu ya dawo wajen da ta zauna ya Kara d'aukar kunun Yana "Ina ga tsarkewa tayi tashi ki Sha kunun Sajeeda ko wani abun kikeso kici"? Ido na zuba Masa Ina Addu'a Allah yasa shi ma ya Sha kunun wallahi da zan ga abinda zai kashe Abban Nusrah Dadi zanji,kunun ya kawo bakina yaga na Kara kau da kaina sai ya ajiye kunun Yana "ko Tea Zaki sha,Wai bakya gajiya da kuka ne Sajeeda dan Allah ki bar kukan nan karki jawowa kanki wani matsala bari na hada miki shayi Ina ga kunun ne bakya so. Ya mik'e yayi waje. Kabiru. Yana fita yayi hanyar kitchen Yana Shiga yaga Yaya Abu nata kakarin amai, gefen ta Kuma ga gwangwanin Madara ta bud'e ta lafta a kofi, Shi kuwa cikin mamaki ya karasa wajen ta Yana "Yaya Abu lafiya kuwa mai ya kawo Miki amai Kuma"? Yaya Abu kuwa hannu kawai take turawa bakinta tana kakarin amai,gudun Kar Kabiru ya zargeta yasa ta zuba ruwa a madarar ta kafa Kai ta shanye. Sai da ta shanye ta kalli Kabiru dake ta jera Mata sannu tana "Wallahi bana San kazanta wari na shaka shine naji zuciyata na tashi" "A cikin kunun warin yake"? "Aaa Ina Kai kunun bakina na shako warin" "Ai da kin fara gyarata kafin ki bata abincin naga yau ma ai warin da sauki Sannu bari na dama mata shayi Kamar kunun ne bata so" Yaya Abu bata iya magana ba saboda cikin ta da taji Yana murda mata da ciwo, Ta Kara dama wani madarar a daddafe tayi d'akin ta dan d'akin ta daban aka ware Mata,Yesmeen ma na da nata d'akin. Tana shigewa daki ta daga Kai ta kwankwade madarar ta kwanta rub da ciki tana "da kaina nake neman kashe kaina banda rashin hankali da b'atar basira mai ya kaini dandana kunun duk wanan kabirun ne ma ya rudani naje na dandana Ta Kara cije lebbenta saboda sosai taji cikinta na karta mata duk da sai da tayi amai,bata tab'a tunanin haka maganin ke da mugun karfi ba,ai wanan da Sajeedan ta sha da asirin ta ya tonu an gano ita ta saka mata magani a kunu,ya zama Dole ma ta Nemo Wanda bai Kai wanan k'arfi ba,ta dade tana Addu'a Sajeeda ta saukaka mata ta tafi da kanta batare da ta karasa ta ba,tunda ta gano irin arzikin da Kabiru yake dashi ta fara kwadaituwa da san itama ta dandana arzikin,ganin Kuma Sajeeda na fama da rashin lafiya yasa ta fara tunanin idan har Sajeeda ta mutu zata iya auren Kabirun ta mori arzikin sa sai ta fake da ta aure shi ne dan ta kula da yaran da wanan kudurin nata ta fara yiwa Sajeeda fatan mutuwa,har mamaki take yadda take ganin Sajeeda na raye dan ba karamin jin jiki sajeedan ke ba,daya hannun kuma ta ringa dan shishigewa kabirun tana caba ado,Sajeeda sam bata dace ma da arzikin Kabiru ba ita ta dace da arzikin, sai dai duk kwalliya da girkin da take yi bata ga alamar Kabiru na ganewa ba watakila dan Yana ganin Sajeeda shi yasa bazai tab'a kawo tunanin aurenta a zuciyarsa hakane yasa ta fara tunanin hanyar da zata bi ta karasa Sajeedan da kafar ta daya ke duniya daya a lahira,tana tsaka da tunanin abun yi Kabiru ya tareta da zancen zai Kara Aure,a ranar ko bacci bata yi ba idan har ta bari yayi auren hakan na nufin bazai tab'a aurenta ba idan kuwa tayi gaggawan kau da Sajeeda dole ma yayi tunanin auren ta,sai gashi Sajeeda bata Sha maganin ba ta Kare a dandana maganin da bata San Yana da mugun karfi ba,dan Mai gadin gidan tasa ya siyo mata maganin,dole ta Kara siyo wani,dan wanan yayi k'arfi da yawa tunda har a yanzu cikinta ciwo yake. Tasan indai ta kau da Sajeeda ba mai kawo zargin ba mutuwar Allah da Annabi tayi ba,tunda dama ta dade tana fama,Kiran da ya shigo wayarta ne ya katse mata tunanin da take tana d'auko wayar ta ga Gwaggo ce ke kiranta,mai da wayar tayi ta ajiye dan yanzu Gwaggo ta fara matsa Mata da waya akan Sajeeda kusan kullum sai ta kirata ta tambayeta ya jikin Sajeeda. Sajeeda Abban Nusrah bai Dade da fita ba sai gashi ya dawo da kofin shayi a hannun sa har lokacin kuka nake,wa zai yarda wai uban yayana ne ya maidani haka saboda yayi kudi,wa zai yarda yayata da ta saki nono ta bani itace ke san ganin ta kasheni saboda kawai ta auri mijina da take ganin yayi kudin da bata san ta hanyar da ya samu kudin ba, duk na jikina ke san cutar dani wane irin zamani ne wanan da Allah ya kawo mu,wai yayata ita take San ta kasheni,nata a yanzu sai naji yafi tsaya min a rai,na Abban Nusrah bai girgizani kamar yadda na Yaya Abu ya girgizani ba,dan dama shi namiji bashi da tabbas,ita Kuma Yaya Abu fa Yar uwata ce ta jini,da yanzu mutuwa tayi,auren Abban Nusrah zatayi ba tare da taji komai a zuciyarta ba,nasan shi ma Abban Nusrah tsaf zai aureta tunda da sauranta,waya sani ma ko ma suna soyayyar yanzu,bansani ba tunda nasan Abban Nusrah Yana cikin maza masu karfin shaawa. Muryar Abban Nusrah ya katse min maganar zucin da nake Yana "ki bude bakin ki na Baki shayin Sajeeda Ina saurine zan fita ana jirana idan na dawo akwai maganar da zamu yi" Kau da kaina nayi dan shi ma yanzu ba yarda nayi dashi ba, kila shi ma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111