Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 48

Chapter 48

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,215 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kula da ita" "Ban yarda ba Sajeeda wanan wane irin rashin hankali ne kina nufin Saboda Yesmeen Zan daina kwana a d'akin nan ko a yanzu da Kika ga na wuce dakina kema kinsan b'ata min rai kika yi Yesmeen din nono take sha da Zaki kawota dakinan kina nufin idan ta kwana a dakinta tana so tayi fitsarin su Yaya abu bazasu iya taimaka mata ba kenan Mai yasa baki da lissafi ne ni mijinki kikeso ki kora daga dakinki saboda Yesmeen toh baki isa ba yanzu nan zata koma d'akin ta" Daga haka Kabiru ya nufi wajen gadon a fusace ya bubuga kafar Yesmeen da jikinta ke balain rawa,yana "Ke tashi ki tafi dakinki ki kwanta" "Da wane idon zata tafi d'akin ta Abban Nusrah ka barta ta kwana daga gobe sai ta cigaba da kwana a d'akin ta" "Yadda Kika kawota haka zaki maida ta Sajeeda ke tashi tashi" Yesmeen bud'e idon ta tayi tana kallon sama ta fara lalube Sajeeda ta karasa wajen ta ta mik'ar da ita sukayi hanyar waje. Kabiru Yana ganin sun fita ya zauna a gefen gadon taya da hankalin sa zai bar Yesmeen ta ringa kwana da Sajeeda a daki daya,har a yanzu da Yesmeen ta makance bai ji ya samu kwanciyar hankali ba tunda zata iya magana kila watarana zata iya tona masa asiri,shi yasa tun farko yaso ma ace b'atar da ita yayi,har gwara ace kurmancewa ma tayi da makancewar dan yasan duk masifarta bata isa magana ba sai dai ta ringa bin mutane da ido, barin Yesmeen ma a raye ya zame masa barazana dole yasan nayi tunda a yanzu ba gani take ba. Sajeeda Daga gigicewar dana ga Abban Nusrah yayi da ganin Yesmeen a dakina na tabbatar da akwai abinda ke faruwa duk yadda akayi sirrin da Yesmeen ke b'oyewa Yana da nasaba da Abban Nusrah, daga yadda naga jikin Yesmeen na rawa tana kuka nasan cewar al amarin babba ne har mai zai saka Yesmeen tayi karyar makancewa mai hakan ke nufi da Abban Nusrah zai kasheta idan ya gano tana gani,ji nayi inama Ina da wajen da zan kebbe da yesmeen ta fadamin abinda take boye min tunani na ya kasa bani daidai,Koda na buga k'ofar d'akin Yesmeen dak'yar Yaya Abu tazo ta bud'e tana masifar katse mata baccin da muka yi ta cigaba da dama zuba min ido tayi taga iya gudun ruwana so nake na nuna mata zata iya cutar da Yesmeen shi yasa na Kai ta dakina,to nasani Yesmeen itama yarta ce kamar yadda nake takamar Yata ce,nidai bance mata komai ba har sai da kwantar da Yesmeen Ina Jin wani iri dan ni nasan tana gani amma na biye mata akan bata ganin a goben nan sai ta fada min abinda take b'oye min Koda na koma d'aki kwanciya kawai nayi dan nasan bacci bazai tab'a d'aukana ba haka na wayi gari Ina sake saken Mai Yesmeen ke b'oye min matsuwa kawai nayi gari ya waye Abban Nusrah ya fita Yesmeen ta fadamin abinda ke faruwa. Abban Nusrah kuwa bansamu ya fita ba aranar sai Sha biyu na Rana. Duk da mugun zazzabin da ya rufeni da kaikaiyin daya dameni haka na d'auko Yesmeen daga d'akin ta na Kai ta dakina dan bana so su Yaya abu su gane mai ke faruwa. Muna Shiga d'akin Yesmeen ta daina kallon sama ta zub'e a kasa ta hau gaisheni. Ban amsa ba na kulle k'ofar dakina Ina "Yesmeen jiya banyi bacci ba saboda na matsu ki fadamin abinda kike boye min yanzu dai Abban ku baya nan ki kwantar da hankalin ki ki fadamin duk abinda kike b'oye min. Yesmeen hawaye kawai take ta kasa bud'e baki tayi magana ranar da Kabiru ya fita da ita ya Kai ta wani waje ya nuna Mata wuka kawai take tunani. Bata San mutuwa. Zuwa yanzu Sajeeda ji tayi Yesmeen na neman kaita bango dan dauriya kawai take ita tasan mai take ji a jikinta yanzu wani irin kuraje ne suka feso Mata a gabanta har wajen cinyarta,da abinda ta wayi gari kenan. Ganin tana ta zubar hawaye yasa ta daka Mata wani irin tsawa tana "kimin magana Yesmeen mai kike boye min"? "Umma idan har na fada miki wlh mutuwa zanyi" "Waye zai kasheki"? "Abban ne zai kasheni umma idan kina kaunata karki tilasta min na fada Miki abinda zai zamo ajalina" Yesmeen tace tana rushewa da kuka da ta Shiga uku ta bar magiyar na barta dan Allah bazata iya fadamin ba idan ta fadamin Abban Nusrah kasheta zai yi Jikina rawa kawai yake Ina Jin iska na min wahalar shaka dan maganganun ta sun Kara tayar mun da hankali jingina nayi da jikin gadon dan ba karamin rawa jikina keyi ba Sai da na Dade Ina sallati kafin na dawo daidai na kalli Yesmeen da ke ta rushe kuka,tana bani hakuri Bata fadamin ba Amma nasan abinda Yesmeen ke b'oye min zai iya zamowa ajalina,watakila Abban Nusrah fyade yayi wa Yesmeen shi yasa take tsoron fadamin tunanin nan da nayi yasa naji na fara hada gumi kirjina na bugu fiye da misali. A hankali na bud'e bakina da naji ya min nauyi na kalli Yesmeen Ina "Yesmeen Abban ku fyade ya Miki shine yace idan Kika bari nasani kasheki zaiyi"? Girgiza min Kai ta fara yi tana rantsuwa ba fyade ya mata ba nace "toh har menene da idan kika fada min Abban ku zai kashe ki,idan har kina tsoron zan fada Masa ko na nuna masa nasani toh na miki alkawari bazan tab'a fada masa ba" "Umma ko baki fada masa ba zai san na fada Miki" "Ta yaya zai sani Yesmeen idan har bani na fada Masa ba ko ke da kika sani,Yesmeen dan girman Allah ki fadamin na samu nutsuwa bari na durkusa miki ko Zaki fadamin" Na fara k'ok'arin saukowa daga Kan gadon Tayi saurin rikeni tana girgiza kai ta fara magana cikin kuka tana "Umma ban shirya rasa raina ba ban shirya rasaki ba idan har na fada miki Ina ganin bankwana zakiyi da farinciki sai kin nemi nutsuwarki kin rasa umma bana san abinda zai daga Miki hankali umma karki min dole zan fada miki Abu daya Zaki gano komai da kanki" "Fadamin Yesmeen Ina jinki" "Umma kiringa tashi karfe biyun dare idan baki ga Abba a daki ba ki fita waje ki duba shi,ki daina bacci Mai nauyi umma da kan ki za ki gano abinda yake faruwa,ko a yanzu nasan ba lailai na tsira da Raina ba kila Abba yaji wanan maganar da nake miki umma abinda nake gudun dai shi zai faru" A haukace na kaiwa Yesmeen damka a kafadarta dan ji nayi kaina na Neman fashewa dan bansan mai take nufi ba "Yesmeen ki fadamin bazan iya jira ba yanzu zaki fadamin ko a yanzu nan na Kira Abban ku nace masa kina gani kin fada min abinda yake b'oyewa" Yesmeen kallona kawai take hawaye na gudu a fuskarta kamar yadda hawaye ke gudu a fuskata numfashina na sama da kasa Sunkuyar da kanta tayi har lokacin hannuna na damke da kafadunta. Girgiza ta da na sake yi yasa ta dago cikin wani irin murya tace "Umma Abba da Kare naga Yana

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});