Chapter 48
Chapter 48
kula da ita" "Ban yarda ba Sajeeda wanan wane irin rashin hankali ne kina nufin Saboda Yesmeen Zan daina kwana a d'akin nan ko a yanzu da Kika ga na wuce dakina kema kinsan b'ata min rai kika yi Yesmeen din nono take sha da Zaki kawota dakinan kina nufin idan ta kwana a dakinta tana so tayi fitsarin su Yaya abu bazasu iya taimaka mata ba kenan Mai yasa baki da lissafi ne ni mijinki kikeso ki kora daga dakinki saboda Yesmeen toh baki isa ba yanzu nan zata koma d'akin ta" Daga haka Kabiru ya nufi wajen gadon a fusace ya bubuga kafar Yesmeen da jikinta ke balain rawa,yana "Ke tashi ki tafi dakinki ki kwanta" "Da wane idon zata tafi d'akin ta Abban Nusrah ka barta ta kwana daga gobe sai ta cigaba da kwana a d'akin ta" "Yadda Kika kawota haka zaki maida ta Sajeeda ke tashi tashi" Yesmeen bud'e idon ta tayi tana kallon sama ta fara lalube Sajeeda ta karasa wajen ta ta mik'ar da ita sukayi hanyar waje. Kabiru Yana ganin sun fita ya zauna a gefen gadon taya da hankalin sa zai bar Yesmeen ta ringa kwana da Sajeeda a daki daya,har a yanzu da Yesmeen ta makance bai ji ya samu kwanciyar hankali ba tunda zata iya magana kila watarana zata iya tona masa asiri,shi yasa tun farko yaso ma ace b'atar da ita yayi,har gwara ace kurmancewa ma tayi da makancewar dan yasan duk masifarta bata isa magana ba sai dai ta ringa bin mutane da ido, barin Yesmeen ma a raye ya zame masa barazana dole yasan nayi tunda a yanzu ba gani take ba. Sajeeda Daga gigicewar dana ga Abban Nusrah yayi da ganin Yesmeen a dakina na tabbatar da akwai abinda ke faruwa duk yadda akayi sirrin da Yesmeen ke b'oyewa Yana da nasaba da Abban Nusrah, daga yadda naga jikin Yesmeen na rawa tana kuka nasan cewar al amarin babba ne har mai zai saka Yesmeen tayi karyar makancewa mai hakan ke nufi da Abban Nusrah zai kasheta idan ya gano tana gani,ji nayi inama Ina da wajen da zan kebbe da yesmeen ta fadamin abinda take boye min tunani na ya kasa bani daidai,Koda na buga k'ofar d'akin Yesmeen dak'yar Yaya Abu tazo ta bud'e tana masifar katse mata baccin da muka yi ta cigaba da dama zuba min ido tayi taga iya gudun ruwana so nake na nuna mata zata iya cutar da Yesmeen shi yasa na Kai ta dakina,to nasani Yesmeen itama yarta ce kamar yadda nake takamar Yata ce,nidai bance mata komai ba har sai da kwantar da Yesmeen Ina Jin wani iri dan ni nasan tana gani amma na biye mata akan bata ganin a goben nan sai ta fada min abinda take b'oye min Koda na koma d'aki kwanciya kawai nayi dan nasan bacci bazai tab'a d'aukana ba haka na wayi gari Ina sake saken Mai Yesmeen ke b'oye min matsuwa kawai nayi gari ya waye Abban Nusrah ya fita Yesmeen ta fadamin abinda ke faruwa. Abban Nusrah kuwa bansamu ya fita ba aranar sai Sha biyu na Rana. Duk da mugun zazzabin da ya rufeni da kaikaiyin daya dameni haka na d'auko Yesmeen daga d'akin ta na Kai ta dakina dan bana so su Yaya abu su gane mai ke faruwa. Muna Shiga d'akin Yesmeen ta daina kallon sama ta zub'e a kasa ta hau gaisheni. Ban amsa ba na kulle k'ofar dakina Ina "Yesmeen jiya banyi bacci ba saboda na matsu ki fadamin abinda kike boye min yanzu dai Abban ku baya nan ki kwantar da hankalin ki ki fadamin duk abinda kike b'oye min. Yesmeen hawaye kawai take ta kasa bud'e baki tayi magana ranar da Kabiru ya fita da ita ya Kai ta wani waje ya nuna Mata wuka kawai take tunani. Bata San mutuwa. Zuwa yanzu Sajeeda ji tayi Yesmeen na neman kaita bango dan dauriya kawai take ita tasan mai take ji a jikinta yanzu wani irin kuraje ne suka feso Mata a gabanta har wajen cinyarta,da abinda ta wayi gari kenan. Ganin tana ta zubar hawaye yasa ta daka Mata wani irin tsawa tana "kimin magana Yesmeen mai kike boye min"? "Umma idan har na fada miki wlh mutuwa zanyi" "Waye zai kasheki"? "Abban ne zai kasheni umma idan kina kaunata karki tilasta min na fada Miki abinda zai zamo ajalina" Yesmeen tace tana rushewa da kuka da ta Shiga uku ta bar magiyar na barta dan Allah bazata iya fadamin ba idan ta fadamin Abban Nusrah kasheta zai yi Jikina rawa kawai yake Ina Jin iska na min wahalar shaka dan maganganun ta sun Kara tayar mun da hankali jingina nayi da jikin gadon dan ba karamin rawa jikina keyi ba Sai da na Dade Ina sallati kafin na dawo daidai na kalli Yesmeen da ke ta rushe kuka,tana bani hakuri Bata fadamin ba Amma nasan abinda Yesmeen ke b'oye min zai iya zamowa ajalina,watakila Abban Nusrah fyade yayi wa Yesmeen shi yasa take tsoron fadamin tunanin nan da nayi yasa naji na fara hada gumi kirjina na bugu fiye da misali. A hankali na bud'e bakina da naji ya min nauyi na kalli Yesmeen Ina "Yesmeen Abban ku fyade ya Miki shine yace idan Kika bari nasani kasheki zaiyi"? Girgiza min Kai ta fara yi tana rantsuwa ba fyade ya mata ba nace "toh har menene da idan kika fada min Abban ku zai kashe ki,idan har kina tsoron zan fada Masa ko na nuna masa nasani toh na miki alkawari bazan tab'a fada masa ba" "Umma ko baki fada masa ba zai san na fada Miki" "Ta yaya zai sani Yesmeen idan har bani na fada Masa ba ko ke da kika sani,Yesmeen dan girman Allah ki fadamin na samu nutsuwa bari na durkusa miki ko Zaki fadamin" Na fara k'ok'arin saukowa daga Kan gadon Tayi saurin rikeni tana girgiza kai ta fara magana cikin kuka tana "Umma ban shirya rasa raina ba ban shirya rasaki ba idan har na fada miki Ina ganin bankwana zakiyi da farinciki sai kin nemi nutsuwarki kin rasa umma bana san abinda zai daga Miki hankali umma karki min dole zan fada miki Abu daya Zaki gano komai da kanki" "Fadamin Yesmeen Ina jinki" "Umma kiringa tashi karfe biyun dare idan baki ga Abba a daki ba ki fita waje ki duba shi,ki daina bacci Mai nauyi umma da kan ki za ki gano abinda yake faruwa,ko a yanzu nasan ba lailai na tsira da Raina ba kila Abba yaji wanan maganar da nake miki umma abinda nake gudun dai shi zai faru" A haukace na kaiwa Yesmeen damka a kafadarta dan ji nayi kaina na Neman fashewa dan bansan mai take nufi ba "Yesmeen ki fadamin bazan iya jira ba yanzu zaki fadamin ko a yanzu nan na Kira Abban ku nace masa kina gani kin fada min abinda yake b'oyewa" Yesmeen kallona kawai take hawaye na gudu a fuskarta kamar yadda hawaye ke gudu a fuskata numfashina na sama da kasa Sunkuyar da kanta tayi har lokacin hannuna na damke da kafadunta. Girgiza ta da na sake yi yasa ta dago cikin wani irin murya tace "Umma Abba da Kare naga Yana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111