Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 82

Chapter 82

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,231 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kashe Sajeeda ne?akan me zan kasheta,ka fito kace ka gaji da zamana a gidanka ba sai ka hada damin sharri ba dan wani ne ya shigo yake san cutar da ita ka Kuma leka kasan gadon kagani dan wallahi an ja kafata bari na leka kagani" Kabiru kallonta kawai yake a lokacin da ta fara k'ok'arin tsugunnawa dan ta leka kasan gadon. Yesmeen hankalinta idan yayi Dubu sai da ya tashi da taji abinda Yaya Abu tace d'auke numfashinta tayi ta cire hannunta dake cikin ledar da ta nannade jikinta dashi a hankali,ta mik'a hannun Yaya Abu na lekawa ta kwasheta da mari, Yaya Abu ta saki ihu tayi waje da balain gudu. Kabiru kuwa ya mik'e tsaye da sauri ya ja da baya Yana kallon kasan gadon dan yaji karar saukar Marin. Tabbas da mutum a kasan gadon dan kamar motsi ma yake ji a kasan gadon. Har lokacin ihu Abu ke tsallawa tana Aljanine a kasan gadon Kabiru kuwa da shi ma jikinsa ya fara rawa ya fara neman abunda zai haska kasan gadon da kuma sandar da zai bugawa koma waye ganin bai ga komai a d'akin ba yasa yayi kasa da murya Yana "Sajeeda da gaskiya Abu akwai mutum a kasan gadon nan bari na dauko wayata na haska na d'auko sanda ta watakila barawone Ina zuwa"? Yayi hanyar waje da sauri,Yesmeen kuwa ta fito daga kasan gadon da ledar a nannade a jikinta ta shige zif din Sajeeda cikin zafin nama tana hada wani irin gumi,k'yarma kawai take saboda tsoro. Kabiru na fita ya ci Karo da yaya Abu da ta dafe kumatunta tana cigaba da ihun "ka leka kagani Kabiru wallahi akwai mutum ko aljan a kasan gadon,motsin da najiyo daga d'akina yasa ni fitowa dan na dubata wallahi ka leka kagani" "Shhhh to ki bar ihu mana haka Ina zuwa" Ya haye sama da sauri ba jimawa ya sauko da wayarsa da ya Kunna tocilan daya hannun sa rik'e da sandar labule yayi d'akin Sajeedan a hankali Yaya Abu da jinta bai dawo sosai ba tabi bayansa itama. Nesa da gadon ya tsugunna ya hau haska gadon sai dai bai ga alamar komai ba. Yaya Abu kuwa ta gwallo ido tana "baka ga komai ba"? Kabiru bai kulata ba ya cigaba da haskawa ganin bai ga komai ba yasa ya mik'e tsaye ya ajiye wayarsa a gaban mudubi da sandar hannun sa ya nufi Kan gadon ya d'auki Sajeeda da har lokacin take kuka ya ajiyeta a Kan 2 Seater dake cikin d'akin ya daga katifar sama. Yaya Abu dake bakin kofa ta saki ihu tana "Wallahi Aljanine ya rike min kafa ya taska min mari innalillahi wa Inna ilaihi rajiun" Kabiru kuwa shi kansa sai da kansa ya daure da mamaki dan tabbas yaji karar Marin da aka yiwa Yaya Abu ta kasan gadon ya Kuma ji motsi amma sai gashi ba kowa a kasan gadon. Yadda yaga Yaya Abu na cigaba da ihu a tsorace har su Annur dake d'akin su sai da suka fito yasa yacewa Yaya abu "Dan Allah ki bar ihun nan haka Kinga dai ba kowa a kasan gadon kila Aljanine ya ga zaki yi ba daidai ba ya cafo kafarki ya waska Miki mari, daga yau Sajeeda bazata Kara kwana a d'akin nan ba sama zan maidata dan Kamar zamanta a d'akin nan hatsarine" Daga haka ya saki gadon ya nufi wajen Sajeeda da ta zaro ido tana gurnani Yaya Abu da ta mugun tsorota dan ta gama yarda Aljanine ya ja kafarta ya waska mata mari ta shige dakinta da sauri ta kulle ta zauna a gefen gado jikinta na wani irin rawa ta yarda yadda Nuratu ke da Aljannu Sajeeda ma na dashi,dan tunda ta kuduri niyyar kashe Sajeeda ta daina cin abincinta idan har ba Aljannun ta ne suka fada mata ta saka magani a abincin ba ba yadda za'ayi tak'i ci,yau da ta so amfani da pillo Kuma Aljanin ya ruko mata kafa, tsoronta ma kar Aljanin ya biyota daki ya kasheta tunda ya b'ace daga kasan gadon. Wani irin zabura tayi ta nufi kofarta ta bude tana kalle kalle,har zata doshi d'akin Yesmeen ta fasa dan dakin Yesmeen ma ya mata nisa nasu Annur ne a gefenta. Ta fada dakinsu da sauri ta rufo k'ofar duk suna zaune da Alama basu koma bacci ba ta haye gadonsu ta kudunduna ta rufe idonta,tabbas Sajeeda nada Aljannu babu tantama da alama burin da taci na auren Kabiru ba zai tab'a yuwa ba dan dak'yar Aljannun ta su barta ta zauna lafiya idan ta ma samu nassarar kashe Sajeedan yanzu ma sajeedar tsoron ta take ji,a kwancen da take ta tafi tunanin suna Yara lokacin da ta addabi Nuratu mahaifiyar Yesmeen da Sajeeda,ranar da ta Zo ta hada musu sharri a kan su suka cinye abincin Babansu mahaifiyar su ta zane su,a ranar Nuratu Aljanunta suka tashi ta shaketa da bango har gobe da tabon a wuyanta shi yasa Sam basa shiri da Nuratu har kowa ya Kama gabansa har Kuma suka manyanta bata manta shakar ba dan farcenta ta soka mata a wuya,kila irinsa ne da Sajeeda, tsoro ne ya Kara rufeta,ta cije lebbenta tana hararo Asarar da zatayi na rasa arzikin da ta ciwa buri,tuna yadda taga Kabiru dazu da yaje d'akin Sajeeda ya saka ta mik'ewa zaune,mamakin yadda Kabiru zai nemi Sajeeda da gabanta ke fidda ruwa kawai take,da yanzu bata je d'akin ba haka zai nemi Sajeeda kila shi ma ya kwaso cutar yazo ya zuba mata idan da ta samu nassarar kau da Sajeedar, tuni taji tsigar jikinta na tashi har yawu na taruwa a bakinta dole Kabiru yaso Kara Aure,idan har shaawa na iya sawa ya nemi Sajeeda da Babu abin mora a jikinta,haka tayi ta juye juye tana tunanin kila ma Yana can Yana neman Sajeeda tunda ya haye da ita sama,zata san yadda zata yagi rabonta kawai amma bazata tab'a iya auren Kabiru ba Koda Sajeeda ta mutu sai dai idan roba zai ringa sawa. Yesmeen a hankali ta fito daga sip din ta jike da gumi Kamar an watsa mata ruwa,har yanzu jikinta bai dainawa rawa ba,dan ta hararo kalar shaka da dukan da zata Sha a wajen Yaya Abu da Kabiru ya ganta a kasan gadon,ita kanta bata san yadda tunanin wanka mata mari yazo Mata zuciya ba,cikin sand'a ta fito daga d'akin dan ba motsin da take ji,ta kalli matattakalr bene tana tunanin halin da Sajeeda ke ciki, hankalin ta ya tashi da sama da Kabiru ya maida Sajeeda dole tasan yadda zasu gudu a kurkusa,a yanzu ma so take ta samu wayar Hamza tunda shi yasan tana gani ta Kira Nusrah a waya ta fada mata halin da ake ciki,ko ta Kira Gwaggo idan har basu samu guduwa ba dan yau da gobe idan asirinta na rufuwa na karyar makanta watarana dole asirinta ya tonu,yau ma Allah ne ya tsallakar da ita. Har zata haye sama ta tuna hatsarin da ke cikin hawa saman, Kabiru na iya Kamata. Haka ta koma d'akinta,ta watsa ruwa ta daura alwala mai kyau,ta saka wani sabon doguwar rigarta da wata kanwar mahaifin ta ta taba Aiko Mata tsaraba tana balain san rigar shi yasa ta kasa

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});