Chapter 2
Chapter 2
na yafa a fuskata sam bana so ta fahimci Ina cikin damuwa,dan nasan sai ta fini ma shiga cikin damuwar, kallonta da nake fuskar kanwata nake gani a fuskarta Margayiya Nuratu damuwar da nake ciki yasa naji hawaye na zubo min. "Umma kuka kike"? Share hawayena nayi Ina "ba kuka nake ba Yesmeen na tuna kanwata ne kawai Allah ya gafartawa Nuratu" "Bata amsa ba illa idon ta da naga ya ciko da kwalla shekara goma kenan da rasuwar kanwata da ta kasance mahaifiyar Yesmeen. Ruk'onta ya dawo hannuna Ina balain kaunar yesmeen tamkar yanda nake kaunar yayan cikina, Yesmeen ta Kara siye zuciyata ne daga lokacin da rukon ta ya dawo hannuna,tana da bala'in biyayya da hankali duk wani abu data san ina so bata Wasa dashi bata da burin daya wuce taga ta faranta min ko Yaya ta gani a cikin damuwa itama tayi ta damuwa kenan. Ko yanzu ma nasan ba lailai taci abinci ba sabida ta gani a cikin damuwa. "Jeki d'auko mana abinci mu ci dan nasan baki ci abinci ba. Tura abincin kawai nake ba wai dan Ina gane dandanon sa ba,na daure na hadiye damuwar da nake ciki dan Kar na Kara dagawa Yesmeen hankali. Koda muka gama cin abincin daki na shige na cewa Yesmeen zan dan kwanta dan itace take yin aikace aikacen gidan Kamar yanda ta Saba kafin Nusrah tayi Aure tare suke aikace aikacen gidan,dan su biyu ne kawai Mata kannen Nusrah duka maza ne,Saifullahi Fahad Hamza da Annur. Sosai na tsinci kaina a cikin damuwa dan tunda nake da Abban Nusrah bai tab'a fita Yana fushi dani ba dan muna samun sabani zamu shirya,duk da Yana da zuciya nasan hanyar da nake bi na shawo kansa,amma jiya abinda ya b'ullo min dashi ya girmama tunanina bazan tab'a iya barin sa ya neme ni ta baya ba sai kace wasu jahilai. Karfe goma Sha daya ya shigo gidan fuskarsa a bala'in hade ina zaune a palo Ina jiran dawowar sa dan har yara duk sun yi Bacci. Ko sallama bai yi ba ballantana ya kalli Inda nake, d'aki ya shige batare da ya amsa sannu da zuwan da nake masa ba. Da ido na bi bayan sa Ina Kara mamakin fushin da ya ke dani na rashin gaskiya har ga Allah mamaki da al ajabi nake ,mik'ewa nayi na d'auko farantin da na jera abincinsa na bi shi d'akin. Ko da na shiga a gefen gado na gan sa a zaune yana duba wani abu kamar a takarda ban dai san mai yake dubawa ba" Na ajiye farantin a gefen teburin dake gefen gadon Ina "Abban Nusrah Sannu da dawowa" Bai dago ba ya cigaba da duba takardar Hannun sa "Abban Nusrah mai na maka kake fushi dani?a iya sanina ba abinda na maka Abban Nusrah wani bak'on al amari ka zo min dashi wanda ni nasan kasan haramun ne,dagani har Kai ba yara bane,ga ta hanyar da Allah ya hallata ma ka neme ni ka samu nutsuwa dani,amma dare daya Abban Nusrah kace zaka neme ni ta baya ta Inda Allah ya haramta kaga dan na k'i bin umarnin ka bai Kamata kayi fushi dani ba dan babu biyayya a sabawa Allah,bansan waye ya baka wanan gurguwar shawarar ba,iya sanina duk wayanda kake mu'ammalla dasu ba mutanen banza bane bansan waye ya ce ma ka gwada ta baya zaka ji dadi ba,taya wajen da ake kashi yayi dadi Ni dai kayi hakuri zan iya k'ok'arina dan na gamsar da Kai amma ban da ta baya" Sai a lokacin ya dago ya kalleni ya ajiye takarda a gefen pillo Yana "Sajeeda duk abinda nake yi Ina sane tsawon zamana dake Ina ga baki tab'a ganin na neme ki ta baya ba,gwaji ne kawai nake so nayi naji abinda ake ji ba wani abu ba,amma tunda kin nuna bakya so shikenan ba zan Kara nema ba,na dauka duk abinda nake so matsawar bai fi karfin ki ba Zaki iya min" "Wanan yafi karfina ne Kabiru shi yasa bazan iya ba abinda akace haramun ne ban ga dalilin da zai saka kace zaka gwada ba mu fa ba Yara bane idan muna raye ma wani shekara zaka gan mu da jika" "Ya isa haka Sajeeda Kinga na Kara neman naki ne yanzu"!? Shiru nayi Ina kallon sa yaja siririn tsaki ya kwanta ya juya min baya. Nace masa ga abincin sa yace bazai ci ba. Wasa Wasa mijina ya fara fushi dani dan naki bari ya nemeni ta baya Wanda zuwa yanzu lamarin nasa ya fara bani tsoro ko Yaya na shawo kansa asan na faranta Masa rai, a madadin yayi ta hanya da ya dace sai naga Yana neman tura jikinsa bayana. Halin nan daya bijiro min dashi ya matukar daga min hankali dan kullum cikin fada mu ke. Gashi mu ba Yara ba ballantana nace wani Zan nemi shawarar sa Wanda ni nasan mu ya Kamata ma mu ringa hana wasu ba dai mu ba. Ko a yanzu da ido nake bin sa har ya gama shiryawa bai ce min komai ba ya fice daga dakin na sauke ajiyar zuciya ina tunanin mafita Kiran Nusrah daya shigo wayata ya katse min tunanin da nake. Ina dagawa muka gaisa kamar yanda muka saba Inda take sanar min zuwan ta anjima na ajiye mata dambu na saki murmushi Ina sai ta zo. Na Mik'e nayi waje dan na fadawa Yesmeen zuwan Nusrah duk da nasan kila ma sun yi waya. Ina fitowa naga Abban Nusrah a zaune a doguwar kujera duk a tunanina Yama fita ashe fitowa yayi ya zauna a palon. Yesmeen kuma na tsugunne a gabansa tana hada mi shi shayi. Fitowa ta yasa ta dago tana "Umma Ina kwana" Zama nayi a gefen shi fuskata d'auke da faraa na hau amsa gaisuwar ta ko kad'an bana so yarana su fahimci wani abu. Tana gama hada masa ta mike tana bari ta d'auko kofi ta hado min shayin na girgiza mata kai akan ta bar shi sai anjima. KABIR Da ido ya bi Yesmeen din har ta shige d'aki ya d'auki shayin ya fara kurba a hankali har ya shanye Yana Jin idon Sajeeda a kansa. Yana dire kofin ya mik'e yayi waje batare da ya tsaya Jin mai Sajeeda ke cewa ba. Yana fita ya haye machine din sa bai zame ko'ina ba sai wani hadadden gida da fadar haduwar sa bata Baki ne. Mai gadi ya riga da ya gane shi hakane yasa ya bude masa ya shige da machine dinsa kansa tsaye ya nufi d'akin saukar baki dake farfajiyar gidan. Kamar yanda yayi tsamani a zaune ya tarar da Alhaji Rabiu a cikin dakakiyar shaddarsa dake ta kyalli kamar madubi. Sai da Kabiru ya sama wa kansa wajen zama. Alhaji Rabiu yace "An dace kuwa"? Sai da Kabiru ya sauke ajiyar zuciya yace "wlh ba'a dace ba duk ta inda kake tunanin zan biyo mata na biyo mata wlh tak'i bani hadin kai" Murmushi Alhaji Rabiu ya saki Yana "Na fa san irin su haka suke da balain taurin kai Amma idan tasan wata ai bata San wata ba ka tashi muje wajen shugaba mu masa bayani" Ya mik'e Yana k'ok'arin yin hanyar waje. Kabiru yayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111