Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 25

Chapter 25

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,214 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Daren ta na farko,na rasa mai ke damuna. Koda ya fara shafani ji nake kamar na ture shi,amma sai naji na kasa,Koda yazo samun nutsuwar sai naji jikina na mugun rawa sai na dan hade jikina hakane yasa ya bud'e idonsa Yana kallona Sai hawaye ya hau zubo min ta gefen idona bansan dalili ba "Lafiya Sajeeda"? "Bana Jin dadi Abban Nusrah dan Allah ka bari zuwa gobe" "Bazan iya ba Sajeeda a Matse nake kiyi hakuri Koda ya shigeni sai naji kamar ba jikin sa ba dan wani irin sanyi naji gabana ya d'auka Kamar Kankara har ya samu nutsuwar. Bangane wa kaina ba. A kwance kawai nake amma jikina ba daidai yake ba. Ko da aka Kira Sallah Asuba kasa ma daga hannu na nayi ballantana na tashi nayi wankan tsarki. Ina kallon Kabiru ya Shiga bandaki yayi wanka ya fito sai daya saka Kaya ya juyo Yana "ya nagan ki a kwance bazaki yi wankan bane"? Magana ma wahala take min sai da ya Kara jefo min tambaya na bud'e bakina dak'yar Ina "Abban Nusrah jikina gabad'aya ba kwari magana ma dak'yar nake yi wlh bana Jin dadin jikina" Matsowa yayi kusa dani ya hau tab'a jikina Yana "Kuma naji jikin ki ba zazzabi ki bari idan gari ya waye sai na Kai ki asibiti a duba ki, yanzu ki daure ki tashi" Ya fara k'ok'arin mikar dani zaune. Dak'yar na zaunan kafin ma na tashi sai da nayi dagaske dan sai nake jin kamar an cire wani abu a jikina iska kamar zai daukeni. Har bandaki ya rakani sai da yaga na fara wankan ya tafi massallaci. A daddafe nayi Sallah dan jiri kawai ke dibana. Kabiru. Koda ya fita bayan gida yayi da sauri dan jikinsa wani irin kaikaiyi yake masa daga yin wanka d'akin da yake ajiye Abubuwan da aka bashi ya bud'e ya d'auko wani ruwa ya wanke gabansa dan shi zai taimaka masa gaban nasa ya daina kaikaiyi. Yana kuwa zuba ruwan gaban nasa ya rage kaikaiyi. Yau zuciyar sa cike take da farin ciki bayan duk wahalar daya Sha dai yau ya samu cikar burin sa gabad'aya abubuwa duk da ya Kamata yayi ya Shiga sahun masu mugun kudi yayi,abinda ya rage masa shine cikar burin sa akan Yesmeen dan Yesmeen babbar matsala ce a rayuwar sa, bai sani ba ko Aljannun da babarta ta bar Mata gado ke taimaka mata, dan jiya yayi matukar mamaki da tazo tana buga musu kofa,sama da sati biyu da ya saka Mata dutsen a cikin fitilar dakinta amma tak'i kunnawa ballantana ta daina gani, yaso ya kau da ita gabadaya amma shugaban su yace bazai Yu ba sai dai a makantar da ita din. A yau ba gobe ba sai ya tilasta wa Yesmeen kunna fitilar d'akin ta. A tsakar gidan yayi sallarsa a gurguje dan haka kawai yaji baya kaunar zuwa massallaci sallar ma yinta kawai yake. Yana iddar wa ya nufi wajen da Karen ke kwance ya d'auki gawan Karen ya saka a buhu Kamar yadda aka umarce shi dan Karen dama mutuwa zai yi idan dai ya samu cikar burinsa,da ace bai mutu ba sai ya rasa arzikin da yake ta nema ya Kuma yi rasa jinin sa guda daya wanda shine babban tashin hankalinsa ace Wai yau ya wayi gari ya rasa jinin sa yana da dogon buri a Kan yayansa ko a yanzu visa zai nemawa Saifullahi da Faisal su tafi waje karatu Kamar yadda duka yayan Rabiu suke kasar waje. Duk da yasan Sajeeda ba lailai taji dadin arzikin sa ba haka zai dage ya faranta Mata,yaso a cikin kwanciyar hankali yayi arzikin nan,bai so ya tab'a lafiyarta ba bashi da yadda zaiyi ne dan Yana matukar bukatar kudin idan ya tuna halin da aka ce masa zata Shiga duk sai ya rasa me ke Masa Dadi,kasan zuciyarsa sai yayi taji kamar bai mata adalci ba idan Kuma ya tuna shawarwarin da Rabiu ya bashi sai yaji ya rage damuwa. Koda ya koma ciki A dakin Sajeeda ya tarar da Yesmeen tana ta zubawa Sajeeda sannu idon ta ya Kada yayi jajjur saboda kukan da tayi. Ya riga da yasan halin da Sajeeda zata Shiga kasan zuciyarsa ji yake dama Yesmeen ce da yaji Dadi. Wayance wa yayi ya nufi wajen Sajeeda yana "Wai jikin ne Sajeeda"? Kai kawai ta iya gyada masa dan ita kadai tasan halin da take ciki. Yesmeen kuwa kukan tausayin Sajeeda kawai take dan tana ganin Kabiru ya fita ta Shiga d'akin Sajeeda dan hankalin ta ya kasa kwanciya so take kawai taga Sajeedan Sai dai tana shiga d'akin Sajeeda ta mik'o mata hannu tana "Yesmeen kuzo ku kaini asibiti bani da lafiya" Yesmeen da saurinta ta Isa wajen Sajeeda ta hau Mata sannu tana tambayar ta Mai ke Mata ciwo,idan har cutar da Sajeeda yayi tana da laifi nata laifin ma yafi yawa sai a yanzu take matukar nadama da bata fadawa Sajeeda abinda ke faruwa ba gashi Kabiru yayi nassara wajen cutar da ita. Kabiru kuwa cikin nuna tsananin damuwarsa ya d'auko mukulin motarsa Yana Sajeeda ta tashi su tafi asibiti. Da taimakon Yesmeen Sajeeda ta shirya Suka tafi asibitin,Yesmeen taso ta raka su Kabiru ya hana akan ta zauna ta kula da gidan Tunda Suka tafi Yesmeen ta rasa me ke mata Dadi. Kan ta balain ciwo yake mata saboda rashin bacci hakane yasa ta dan kwanta kafin su kabirun su dawo dan ta gama aikin ta. Tana kwanciya bacci yayi awon gaba da ita ta hau mafarki Mafarki A kwancen da take taga Rabiu ya shigo d'akin ya taka kujera ya cire glass din fitilar d'akin ta ya saka wani abu amulmule kamar ball ya maida glass din ya rufe ya sauko ya tafi. Ita dai tana kwance tana ta mamakin abinda yazo ya saka a fitilar. Mik'ewa tayi ta nufi wajen makunin ta kunna fitilar dan sai take ganin kamar kwan fitilar ya canza. Ta na kunnawa glass din ya fashe Mata a ido,ta fara ihun idonta haka tayi ta tsalle a mafarkin tana Jin radadi a idonta. A firgice ta tashi daga bacci a lokacin da taji an Kira sunan ta da k'arfi ta bud'e idonta taga ashe mafarki take daga kwanciyar ta ashe. magriba tayi. Kabiru ta gani a bakin k'ofar ya mugun hade rai Ta mik'e da sauri tana "Abba kun dawo ya jikin umma?" "Ya kike Zama a cikin duhu zo ki kunna fitilar nan dan d'akin ki yayi duhu da yawa... Assalamualaikum Barkanmu da wannan lokacin AUNTY ZEE TAKU CE ,Ina uwar gida Amarya da yanmata albishir gareku BONONZA; BONONZA;BONONZA; Nazo maku da SAHIHIN MAGANIN CIRE TUMBI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI,KINCI GAYU ANA TAMBAYARKI YAUSHE ZAKI HAIHU TUMBI YA HANAKI ADO DA KWALLIYA SHA KURUMINKI NAZO MAKI DA MAGANI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI ZAN DANDANA MAKU SHI AKAN RABIN KUDINSHI DAGA NAN ZUWA SATI DAYA 7K DUK ROBA DAYA KI BIYA 3500 KI MALLAKI NAKI NAN DA SATI DAYA ZAI KOMA 7K MAGANIN BREAST WANDA ZAICIKO MAKI DA TUWON NONO DAN ALLAH KIJARABA ZAKIZO KINA GODIYA DAN DUK WADDA TA GWADA SAITA DAWO MANYAN MATA SUKE GYARA KAMAR YANDA KUKASANI 8K YAKE ZANKARA TALLATA MAKU SHI KI BIYA 4K

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});