Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 86

Chapter 86

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,232 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ya cire ,sai hada zufa yake,har zai koma d'akin Sajeeda Saboda yaga halin da Yaya Asmau ke ciki sai Kuma ya fasa yayi d'akin Yesmeen dan gani yake zata iya guduwa taje ta tona Masa asiri,gwara Yaya Asmau ta sume yasan ba inda zata iya zuwa. Yana Shiga d'akin Yesmeen yayi wajen bandakin ta ya hau tura k'ofar bandakin yaji a rufe,ya hau bugawa Yana "Ki bud'e min k'ofar Nan Yesmeen" "Wallahi bazan bud'e ba Abba a bandakin nan zan ta zama har sai na samu mai zuwa ya taimaka min" "Yesmeen idan Kika bari na b'alle k'ofar nan na shigo na rantse da Allah sai na kasheki ki bud'e min k'ofar magana Zan Miki ba abinda Zan miki indai kin tabbata baki taba fadawa kowa sirrina ba" "Ban tab'a fadawa kowa ba Abba amma bazan bud'e k'ofar nan ba,Kuma wallahi Abba ko ka balle k'ofar nan ka shigo kafin ka kasheni sai na tona maka asiri,tamkar mahaifina na d'auke ka amma shine kake so ka cutar dani ka lalata min rayuwa Abba duk akan neman duniya ka cire rigar imanin ka ka cutar da umma iya nan bai isheka ka hau farautar rayuwata ta karfin tuwo sai ka ga bayana saboda nasan sirrinka,Abba gaggawan Mai kake yi mai kake nema a gidan duniya da har zaka yanki ticket din da zai maka katanga da samun Rahamar Allah ka manta da duk kudin mutum sai ya mutu,ka manta da duk abinda mutum ya tara a gidan duniya yake barin sa,ka manta da bawa baya mutuwa sai ya cinye rabon da Allah ya tsaga zai samu,Abba kayi gaggawa wanan kudin da akansa ka kauce hanya dama naka ne Allah ya rubuta sai kayi kudin,wuyanta ka cigaba da hakuri har zuwa lokacin da Allah zai Buda maka ka samu,amma gajen hakuri ya sa kaje ka jefa kanka a hallaka,umma da bata maka komai ba ka lalata mata rayuwa,yau idan ka Fadi ka mutu Kai kadai zaa binne a kabarinka ba ko cokali da zaa bika dashi,zaman duniya na dan lokacine lahira kuwa dindindin ne, duk wani abu da kayi a gidan duniya wallahi sai kayi wa Allah bayani,Ina ka Kai ilimin ka Abba duk akan duniya da kasan ba Wanda ya tab'a dawwama a cikinta duk Inda ka Kai ga tara dukiya ka sabawa Allah wallahi dole sai ka koma gare shi ka masa bayanin yadda ka tara dukiyar da ka Tara ta hanyar zalintar bayin sa" Kabiru wani irin duka ya kaiwa k'ofar Yana "Yesmeen ni kike fadawa maganganu yau ni na Zama sa'anki kike so ki nuna bani da ilimi"? "Abba gaskiya na fada maka ba magana nake fada maka ba ka tubarwa Allah tun wuri kafin lokaci ya kure maka amma wallahi indai ka dage sai ka cutar dani Abba Koda kayi nassarar kasheni Zan ta rokon Allah a kabarina akan ya tona maka asiri ya bankada sirrinka kowa yasani" naushi ya kaiwa k'ofar Yana Jin kirjinsa kamar ya fado saboda yadda yaji maganganun ta na kona shi da ace zai iya balla k'ofar wallahi ba abinda zai hana ya raba Yesmeen da ranta yaso ace ita ya bugawa kwalbar palon gashi yanzu hankalinsa ya rabu gida biyu ga yana tsoron ya tafi d'akin Sajeeda wajen Yaya Asmau gashi Yana tsoron idan ya tafi Yesmeen ta fito,tunanin kulle dakin da mukulli ne ya fado masa ya bar bakin k'ofar da sauri yayi hanyar k'ofar Yana zuwa ya zare mukullin ya fita waje ya kulle,ya tafi da mukullin dan a yau sai ya kashe Yesmeen bari ya fara tunanin yadda zai yi da Yaya Asmau. D'akin Sajeeda ya koma Yana Shiga yaga Yaya Asmau har lokacin a sume bata farfado ba,har ga Allah bazai so Yaya Asmau ta mutu ba,a rayuwa idan akwai wacce ya tab'a yiwa shaawar mutuwa Kuma yake Jin zai iya kasheta da hannun sa Yesmeen ce. Hannunsa wani irin rawa yake dan Yama kasa rik'e wayar sai da ta Fadi wajen sau uku kafin ya iya nemo lambar Rabiu ya hau kiransa yana share zufa gabad'aya ya rasa mai ke Masa dadi, gashi a yau ake so ya nemi mace ta baya Rabiu na dagawa ya fara magana Yana "Rabiu na Shiga uku asirina ya tonu,Yar uwar sajeeda tazo ta kamani a d'akin Yesmeen, gashi na buga Mata kwalba na rasa yadda zanyi da ita Rabiu mai yasa banida saa ne duk wani Abu idan zanyi sai an samu matsala?kasan kuwa Yesmeen tana gani Ina zuwa dakinta tace tana kallona duk tsawon lokacin nan da na dauka ta makance ashe tana gani,duk abinda nakeyi akan idonta ne? Kaga yadda yarinya nan ta fadamin maganganu Rabiu a fadawa shugaba ya kashe min yesmeen yanzu a taimaka min,ta Sha alwashin sai ta tona min asiri idan har na nemi na cutar da ita har wani barazana take min,duk wahalar nan da nake Sha ake saka ni abu Ashe yarinya Nan ce ke warware min komai,gashi yanzu Yar uwar Sajeeda tazo ta rintsani a d'akin ta tsirara itama ta dage zata tona min asiri Rabiuu na Shiga uku yanzu ya zanyi? "Yanzu Ina Yesmeen da Yar uwar Sajeedan?? "Yesmeen ta kulle kanta a bandaki ita Kuma Yar uwar sajeeda gata nan a sume a gabana na rasa yadda zanyi Rabiu" "Toh ka kwantar da hankalin ka ni banga abin tashin hankali anan ba sai kayi ta Abu kamar namiji ba dai duk ka dagawa kanka hankali bane saboda Kar asirinka ya tonu, to ka kwantar da hankalin ka asirinka bazai tonu ba,akwai Wanda yasan Yar uwar sajeeda tazo gidanka"? "Bansan zata zo ba ba Wanda yamin waya kawai ganin ta nayi ba Kuma kowa a gidan dan yayar Sajeeda da yaran sun tafi wajen Yata da nace maka ta haihu ni kadai ne a gidan sai Yesmeen da Sajeeda dake sama" "Da kyau yanzu ka samu ka nemi Yesmeen"? "Ina ban nemeta ba Rabiu gashi kasan shugaba yamin gargadi Kar a samu matsala wanan wane irin masifa ne Rabiu tunda na shiga kungiyar nan ban Kara samun kwanciyar hankali ba,kudin ma na kasa cin sa cikin kwanciyar hankali" "Yayi wuri ka fara tunanin yin nadama, tun farko da mun sani an kashe wanan yarinya da bana Jin zaa samu wanan matsalar toh idan har za'a saka ka aiki ta ganka ai dole ya warware ayi ta baka wani kayi,yanzu shawarar da zan baka ba kace Yar uwar sajeeda ta sume ba,ka nemeta ta bayan ka goge jikinta da kyallen nan ka murde Mata wuya kawai daddare kaje ka Yar da ita,ka kashe wayarta saboda Kar a zargi ta iso gidanka,ka fito ka sallami mai gadi,idan ka gama da Yar uwar Sajeedan sai ka balle k'ofar bandakin ka fito da yarinya nan ka daureta ka kawo mana ita kungiya ayi amfani da jininta kawai" Girgiza Kai Kabiru ya fara yi cikin tashin hankali Yana "Rabiu bazan iya kashe ta ba gwara dai na nemetan inyaso ayi mata abun da zata samu tabin hankali yadda bazata tona min asiri ba wallahi bazan iya kasheta ba Kar abin yamin yawa" "Bakada hankali Kabiru ga abinda zakayi nan cikin sauki asirinka ya rufu idan ta warke fa idan Suka dage da Addu'a ka nemeta ta bayan Ina jiye maka wallahi idan baka Yi

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});