Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 110

Chapter 110

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,240 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Yesmeen Taki bashi fuskar a fadarta bata san Mai kudi ita dai talaka zata aura,dariya take bani dan nasan tsorata tayi ta dauka kowane Mai kudi ta hanyar da Kabiru yayi kudinsa suke kudinsu. Ba na so na matsa mata shi yasa na rabu da ita amma babban burina naga na aurar da su biyun dan tuni tsohon mijin Nusrah yazo ya karbi yarsa. Allah Kuma ya dubeta tana fara zuwa makaranta Allah ya mata farin jinin samari dan duk ba mai mata itace dai tak'i kulasu. Saifullahi kwanan sa biyu a Abuja yamin waya akan ya gama abinda ya Kai shi gobe da sassafe zai taho. Addua dawowa lafiya nayi Masa. Yana kashe wayar na cewa Yesmeen su Shiga Kitchen suyi wa Saifullahi abinci. Suna girki a kitchen Ina jiyo hirarsu Ina murmushi,a yanzu banida wani matsala sai dai nace Alhamdulillah burina kawai yanzu naga auren yayana. Su Annur kuwa yanzu basa jiran sai Saifullahi ya Kai su asibiti wajen Kabiru da kansu suke tafiya asibitin duba shi,haka zasu zage su tafi da abubuwa,Yesmeen ce dai bata yarda ta bisu ban Kuma tab'a tilasta mata ba dan gani nake tsoronsa take ji. Wajen karfe biyu muka ji dirin motar Saifullahi a k'ofar gida,sai da ya dade kafin ya shigo har Ina tunanin tura Yesmeen ta dubo Mai ya tsayar dashi sai gashi ya shigo d'auke da wata tsohuwa, mik'ewa nayi daga zaunen da nake Ina kallonsa har ya shigo da tsohuwar da ana shigowa da ita naji wani irin wari,yana isowa tsakiyar palon ya ajiyeta,na zubawa tsohuwar ido cikin tausayawa yadda take zuba wari,Ina k'ok'arin tambayar Saifullahi inda ya samo tsohuwa yace "Umma baki ganeta ba ko mama ce fa" Kirjina wani irin bugawa yayi naja da baya tare da sakin sallati jikina ya dauki rawa,Taya wanan tsohuwar zata zama Yaya Abu, sallati kawai nake Saifullahi ya hau bani labarin yadda ya ganta da ya d'auko hanyar tahowa motarsa ta lalace,a garin Nemo mai gyara motar ya dan shiga bayan gari shine ya ganta a kwance kudaje nata binta ya dauka ma mutuwa tayi Saboda warin da take sai da ya tambayi mai gyaran motar ya hau bashi labarin ta akan almajira ce da suka kasa gane wane irin cuta ne da ita mutane ma kyankyamin ta suke dan har yanzu ma mamaki suke da bata mutu ba,cikin tausayawa Saifullahi ya matsa kusa da ita dan ya bata kyautar kudi,a daidai lokacin da ta bud'e idonta tana numfarfashi duk da tsufan da yaga tayi da yadda koma kamar kwarangwal sai da ya ganeta,jiki na rawa ya roki Mai gyaran mota akan ya taimaka masa zai biya ko nawa ne,a samu wasu su wanke ta a canza mata Kaya,yayar mahaifiyar sa ce da ake ta nema,abinka da kudi,tuni ya samo wasu mata suka kaita gidansu Suka wanketa suka Nemo Kaya suka saka Mata Saifullahi ya Basu kyautar kudi,ana gama gyara Masa mota suka dau hanya yasan Sajeeda zata ji dadi, dan daidaikun rana ne bata maganar Yaya Abun Sajeeda Kuka na fashe dashi,dan ba Wanda zai yarda Yaya Abu ce ta dawo haka,itama kallona kawai take tana hawaye ba mai imanin da zai kalli Yaya Abu bai tausaya mata ba,jiki na rawa na kaita bandaki dan wari kawai take,banji kyankyaminta ba na wanketa na bata abinci na Kira Gwaggo a waya na sanar mata da anga Yaya Abu yanzu haka tana gidana,yarana ma sosai suka tayani murna dan ban basu fuskar da zasu tsani yayata ba,tuni na hau hidima da ita,dan har ga Allah na yafe mata,ita kuwa kuka kawai take tana gurnani,Wanda halin da take ciki ya tuna min da Nima halin da na Shiga a baya, washegari da sassafe gwaggo ta duro ita da Yaya Asmau da Yar Yaya abu shemau suma sun girgiza da yadda ta dawo,shemau sai kuka take dan ta dade bata ganta ba,ita kanta batasan Mai yasa bata nemi Yaya Abu ba duk tsawon lokacin nan Kuka muka ci muka koshi muka hau Taya Yaya Abu da Addu'a dan nasan ba maganin da zai warkar da ita sai karfin Addu'a. A.ranar da ta cika kwana shidda a gidana muna d'akin a zaune ciki kuwa har da Gwaggo dan baba bai dade da tafiya ba shi ma yazo ya dubata ba Wanda ma zai rike yaya Abu a ransa da idan ya ganta Bai ji tausayin ta ba, Ganin kamar tana so a tayarta zaune yasa na mikar da ita na jingina bayanta da jikin gadon hawaye na zubo mata naga ta fara motsa baki kamar mai koyon maganar ta fara "Sssaaj jj ee da ki yafe min Gwaggo dan Allah ki yafemin,kice baba ya yafemin, Yesmeen ki yafemin dan Allah ku yafemin na yafewa Kabiru dan inaso nima Allah ya yafemin. A rude muka hada baki wajen cewa mun yafe mata Gwaggo kuwa sai saka Mata albarka take,a hankali muka ga ta fara shakuwa muka yi kanta gabad'aya cikin kiftawar ido ta daina motsi Yaya Abu ta amsa Kiran Allah Munyi kuka Kamar ranmu zai fita,Muna ji muna gani aka yi Mata sutura aka kaita gidanta na gaskiya duniya zancen banza,duk San mu da duniya dole mu tafi watarana tunda mutuwa dole ce,a kwana a tashi sai gashi mun tafi wata biyar da rasuwar Yaya Abu da muke ta binta da Addu'a dacewa da Rahamar Allah Kabiru kuwa da ya dawo hayyacinsa kad'an tilastawa yayansa yayi suka kirani Yana kuka ya hau Neman yafiyata nace Masa na yafe Masa yayansa suma suka ringa tayashi kukan,da Addu'a ya bimu gabad'aya sai da muka zo tafiya ya bawa Annur wani farin takarda akan ya bani, muna fita daga asibitin ya bani Ina dubawa naga takarda saki ne ya sakeni saki daya Wanda har ga Allah Dadi naji dan ko ya warke ba koma Masa zanyi ba. Cikin sauki ya bani takarda ta a haka rayuwa ta cigaba da tafiya cikin rufin asiri, Saifullahi kuwa budi yake samu ko ta Ina Fahad shi ma ya samu aiki,Nusrah kuwa mallaminta daya dage mata sai da ya turo magabatansa aka sa musu rana, ni kuwa ganin Yesmeen na tsalle tsalle da Saifullahi na Kira Saifullahi har daki na fada masa Ina so ya auri Yesmeen dan babban burina kenan a rayuwata na dade da burin nan a zuciyata amma idan Yana ganin bazai iya aurenta ba shikenan. Ga mamakina Saifullahi take ya amince da auren Yesmeen Toh mai ya ragemin a rayuwa babu,Kamar a mafarki sai gashi na aurar da yayana uku Rana daya, Saifullahi a gidan da ya gina ya ware bangarensa da na Yesmeen Nusrahh kuwa itama bata da nisa dani,ba abinda yayi farko da bashi da karshe wuyanta kayi hakuri, Kabiru har gobe Yana asibiti dan idan ciwon nasa ya tashi Yana dan tab'a hauka. Shekara biyu a tsakani Saifullahi ya biya Mana muka je muka sauke faralli ni dashi da Yesmeen da ke hidima dani kamar a baya. Yanzu zan iya cewa Alhamdulillah rabbil alameen dan yarana gabad'aya ba Wanda bashida abin yi ta hanyar halal har rububin kyautata min suke,duk da ba tsufa nayi ba bana kawowa kaina aure Wai kusa bansani ba ko nan gaba....... Alhamdulillah rabbil ala meen anan na kawo karshen littafin RUFAFFEN SIRRI kuskuren da nayi a ciki rabbi ya

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});