Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 31

Chapter 31

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,229 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kaikaiyin take ji ba har ruwa mai kalar ruwan ke jikata Kamar tana period ko da take tsaye tana iya Jin yadda ruwan ke wari,bata san lokacin da ta saki sallati jikinta na rawa ba taya zaace a jikinta wanan ruwan ke fita,tana Jin Yesmeen na buga k'ofa tayi saurin toshe bakinta tana k'ok'arin maida hawayen dake zubo mata, dan bazata iya kallon Yesmeen tace mata ga halin da take ciki ba bata Jin zata ma iya jiran Kabiru a yanzu zata shirya ta tafi asibiti tana daga bandaki tace wa Yesmeen taje Palo su Yaya abu sun zo. Yesmeen kuwa waje tayi da jajjayen idonta da ta murzawa rob,dan dagaske take so ta nuna ta samu matsalar ido,tunda har kau da ita kawai Kabiru ke so yayi,idan tace ma zata gudu,kabiru zai iya sawa a nemota,gwara ta makance din, hankalin ta bai Kara tashi ba sai da taji Sajeeda na ce mata bata Jin dadi ko bata fada ba kana ganin ta kasan ba daidai take ba,Kamar ta samu wajen da ba kowa tayi ta kukan tausayin Sajeeda Sam bata cancanci haka daga wajen Kabiru ba ko ya ta rufe idonta yadda Kabiru ke saduwa da Kare ke fado mata ta kasa goge abinda ta gani a kanta,duk akan neman duniya Kabiru ya cutar da Sajeeda, Sanin halin Yaya Abu yasa ta cigaba da mitsitsika idonta dan tana da saa ido ba kadan ba tana tsoron ta gano ba ciwon ido take ba" Tana zuwa ta zub'e a kasa ta hau gaishe su Suka amsa gaisuwar Yaya abu na kare Mata kallo ta jefa Mata tambayar mai ya samu idonta tana k'ok'arin magana Kabiru ya shigo da sallama hannun sa d'auke da ledoji idonsa akan Yesmeen yasan gobe uwar haka Yesmeen sai dai ta Kare rayuwar ta a duhu. Ledojin da Yaya Abu ta gani a hannun Kabirun ya d'auke Mata hankali daga Kan Yesmeen,Yesmeen ta mik'e tsaye tana k'ok'arin komawa daki,dan dole sai ta nuna tana balain Jin jiki, Kabiru kuwa yace "Wai har yanzu idon naki ne"? "Eee Abba wlh zugi idona ke min dusu dusu nake gani" "Yanzu nake tambayarta mai ya samu idonta yayi ja haka"? Yaya Abu tace tana satar kallon ledojin da Kabiru ya shigo dasu Wai Abu ya fado mata a ido Ina ga gobe idan bata ji sauki ba dole taje Asibiti" Kabiru yace Yana ajiye ledojin hannun sa Yesmeen Kuma ta nufi d'akin ta a daidai lokacin da Sajeeda ta fito daga bandaki tana Jin wani irin zugi a kasanta dan a garin susa har ciwo taji wa kanta. Ganin Kabiru ya dawo yasa ta daure ta d'auko ledojin ta nufi kitchen ta juye fried rice da Kabiru ya siyo da yawa ta zuba a flask ta zuba musu a plate ta Kai musu d'akin Yesmeen dan gani take sai sun fi sakewa acan duk da tasan Yaya Abu ba abinda ya shafeta zata iya ci a gaban kabirun har da loma,ko a yanzu kafin ta Kai musu abincin Hira kawai take da Kabiru tana sainting haduwar gidan. Ita Kuma abinda ta tsana kenan,dan yanda take yiwa Kabirun yasa ya raina ta ba wani girmama ta yake a matsayin yayarta ba. D'akin Yesmeen din ma da ta Kai su haka tayi ta kalle kalle tana fadar haduwar d'akin. Sajeeda kuwa ta barsu a d'akin tana zata je asibiti ta dawo. Ko da ta fito daga d'akin gani tayi Kabiru ya shirya a cikin dakakken shadda da kana kallon shaddar kasan Mai balain tsada ce,sai taga gabad'aya kabirun ya canza kamar bashi ba,ganinta ya saka ya tsaya sai da ta karasa wajen sa ya fara magana Yana "Zan dan fita yanzu nan na dawo wani Kaya muke so a tura can cotonou" "Yanzu Abban Nusrah ba asibiti kace zaka kaini ba,kasan mai nake ji a jikina kuwa Abban Nusrah so kake sai na fara susa a gaban mutane zaka kaini asibiti har yanzu ruwa mai doyi zubo min yake" "Yanzu dan Allah ya ki ke so nayi ga mahimmin abu da nace miki zanje nayi,yanzu kije ki Kara Shan maganin ki gobe da sassafe Zan Kai ki asibiti ni bansan Ina Kika kwasowa kanki wanan abin ba bari naje na dawo Kinga ma bai Kamata ki fita da baki a gidan ba" Daga Haka ya yi hanyar fita Sajeeda ta bi shi da ido,tana Jin wani irin takaici na rufeta,har ace tana cikin irin wanan tashin hankalin Kabiru bai wani damu ba,ta shige daki ta kwanta ta fara matsawa kanta da tunanin yadda akayi ta wayi gari da wanan masifar a jikinta. Duk yadda taso ta gano ta kasa ganewa sai ta d'auko zargin kabiru ne ya goga mata sai ta fasa dan iya sanin ta baya neman matan banza bata sani ba ko haduwa da abokinsa da yake kirarin ya canza Masa rayuwa ya jefa shi a cikin halin banza, Sai da ta sake wanke jikinta ta canza komai na jikinta ta koma d'akin Yesmeen hira Asmau da Yaya Abu kawai suke Yesmeen na rabe a gefe da jajjayen ido,duk minti minti sai ta sosa idon, Sajeeda sai sannu take jera mata,yaya abu kuwa sai tabe baki tayi tana ciwon idon Yesmeen take yiwa wanan rakin Sajeeda ma ke biyeta taja saki tana Kara karewa d'akin Yesmeen kallo tana "Allah ya baki Sajeeda kiga Wai hadadden d'akin nan ne d'akin Yesmeen har yanzu baki fada min yadda aka yi mijinki ya kudance haka ba"? Murmushin yake Sajeeda tayi tana "Yaya Abu naga kina hira dashi idan ya dawo ki tambaye shi kiji" "Karki gaya min magana mana kawai dan na tambaye ki ya aka yi mijinki ya samu kudi haka shine zaki gaya min magana" "Allah ya baki hakuri Yaya Abu wlh ba haka bane idan na fada Miki yadda yayi kudin ba lailai ki yarda ba Kamar yadda har yanzu nake cikin fargabar yadda yayi kudinsa dare daya,Wai wani abokinsa ne Rabiu Yana da balain kudi,abokin sa ne tun primary shine Suka hadu watanin da suka wuce shine ya sama mishi aiki a company sa wanan gidan ma da kike gani shi ya bamu kyauta,baki ga yadda yake facaka da kudi ba,shi yasa nake a tsorace dan hidimar tayi yawa gani nake kamar abokin nasa ba ta hanyar arizki ya samu kudinsa ba dan abin yayi yawa kudi da aka nema ta halal bazai yu a ringa kashe su kamar baa San zafin su ba,amma duk yadda naso nunawa Abban Nusrah yayi baya da abokin nasa yak'i yarda idonsa ya riga da ya rufe" Sallati Yaya Abu ta saka tana tafa hannuwa sai da ta gama ta fara magana tana "Sajeeda kamar anyi Miki baki Allah ya muku wanan arzikin ki wani tsaya kwokwanto ke Ina ruwanki da yadda abokin nasa ke samun kudinsa,ko fashi yake yi Ina ruwan ki lokacin arzikin ku ne yazo gwara ki saki jiki ki more arziki nidai idan mijinki ya dawo zan roke shi arziki na zauna da ku yadda na ga wanan daula ba abinda zai maidani gida tunda ni ba aure ba,ba komai ba idan Allah yasoni da arziki sai kiga nima na hadu da Mai kudin Murmushin yake kawai Sajeeda tayi dan bata san mai zata cewa Yaya Abu ba

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});