Chapter 76
Chapter 76
Sajeedan dan arzikin sa hauhawa kawai zai tayi ,har garinsu yaje ya siyi katon fili dan so yake yayi wa mahaifiyar sa gini itama ta mori arzikinsa,dan tana tambayarsa ya akayi ya samu kudi,ya sharara mata karya take ta yarda ta hau zuba Masa albarka,daga gidansu ya tafi gidansu Sajeeda da alama aikin da aka yiwa iyayen Sajeeda yayi dan Koda yaje basu Masa maganar daukota ba inda ya shirga musu karya akan nan da wata uku ma zasu fita wajen yanzu an dora Sajeeda akan magani,ya nuna musu tana samun sauki, Gwaggo ce ma kamar aikin bai wani Kamata ba sai cewa take ita dai zata d'auko Sajeedan,sai Babansu Sajeedan ne yace baza'a daukota ba tunda ance tana samun sauki,da yazo tafiya ya d'auko kyautar kudi ya Basu,duk sukayi turus suka kasa karba sai ya tuna zasu iya zargin ya akayi yayi kudi haka,sai ya saki murmushi ya hau sharoro musu karya ai yanzu harkar mai yake, Gwaggo kin karbar kudin tayi,dan haka kawai taji bata yarda da shi ba amma ta kasa zargin ko Yana aikata mumunan Abu wajen samun kudin dan gani take kamar bazai iya aikata mugun abu ba,bai Kuma yi Kama da mai aikatawa ba, kafin ya tafi ya sanar musu da zai Kara auren,babban su Sajeeda ya sa albarka dan gani yake kabirun ma yayi k'ok'ari da ya zauna da Sajeeda duk tsawon lokacin nan bai Kara Aure ba, da wani ne ma sakinta zaiyi yace bazai iya zama da ita ba, Gwaggo kuwa ji tayi kamar tayi ta yiwa Sajeeda kuka zuciyarta ta sosu da auren da yace zai yi tana tsoron ya Kara auren ya juyawa Sajeeda baya tunda Sajeeda ba moruwa take ba,sai da ta kasa dannewa ta hau rokonsa akan ya rike Amana ya kwatanta adalci a tsakanin su tana nan tana yiwa Sajeeda Addu'a in Sha Allah zata warke, Kabiru kuwa ya hau rantsuwar bazai tab'a juyawa Sajeeda baya ba,Babansu Sajeedan kuwa yace masa Yana auren yasa Abu ta dawo Dan Yana ciwon kafa ne da tuni yaje ya taho da ita da dan abin kunya ne ace taje ta tare a gidan kanwarta. A haka suka yi sallama ya taho bayan Gwaggo ta bashi lodin maganguna akan ya kawowa Sajeeda tayi amfani dashi,Yana yin nisa da gidan ya wurgar da ledar. Rabiu na d'aukar wayar ya fara magana Yana "kasan na kasa nemanta abinan kwanciya tayi,tak'i mik'ewa,Rabiuu Ina Shan wahalar yin ayyukan nan ni kadai nasan kalar wahalhalun da na sha daga lokacin da na fara harkar nan zuwa yanzu kai kuwa banga alamar kana Shan wata wahala ba" "Taya Zan Sha wahala bayan Ina taka tsantsan da komai,wanan kame kamen da kake fa kana auren yarinya da zata maka biyayya fa an wuce wajen,baka da fargabar komai sai dan aikin da bazaa rasa ba" "Toh idan na aureta bata bani hadin kai ba fa ta zama mai taurin kai irin na Sajeeda"? "Sajeeda a mutanen da tazo ai,na yanzu suna da San kudi ga Ateeka nan Ina ta moreta Ina cikata da kudi,Kuma ko damuwa batayi ba Dan tana samun abinda take so,Kamar yadda nima nake samun abinda nake so,auren nan kawai zaka yi,ka samu ka ringa cika duk aikin da aka baka,itama nasan ka kasa nemanta ne Saboda halin da take ciki,Ina ta baka shawara ka kaita a cika aikin nan kak'i Ido Kabiru ya zaro Yana "Bazan iya ba Rabiu iya wanan da nayi ya Isa ba sai na karasa ta ba har ga Allah baa san raina nayi harkar nan da ita ba taurin kanta ya jawo Mata" "Toh ai gani nake idan baka karasa ta ba bazaka saki jiki ka mori kudinka ba duk tsawon lokacin nan Wai ka kasa Kara Aure wai Kar aga ka mata wulakanci,da nine da tuni nayi biyu ma,nasan banda an rufe mata baki da tana magana zaka iya zuwa kace min zaka fita a kungiya dan naga kamar tsoron ta kake" "Bazaka Gane ba Rabiu Sajeeda tamun hallaci a rayuwa ta kaunaceni shi yasa nake jin ban kyauta mata ba amma zan tura gidansu Barakan sati biyu kawai zaa saka dan ko ba'a Sakani aiki ba yanzu ji nake idan banyi ta bayan nan ba Zan iya zaucewa na siye Iyayenta da kudi sosai,har sun kori saurayinta,duk da naga alamar ba Sona take ba Iyayenta ke tilasta Mata Ina sakar musu kudi nasan an wuce wajen. "Kudi ai sunyi a rayuwa abokina kayi abinda ranka ke so ko jarirya ka nuna kana indai kana da kudi,da gudu zaa baka,yanzu abinda za'ayi sai ka nemi wata a titi kayi aikin kafin kayi auren" Hira suka Kara tab'awa kad'an kafin suyi sallama Kabiru ya kwanta Yana tunanin yadda zai barje baraka idan har ya aureta,dan yarinya ce mai tarbiya dan ko gwada rike hannun ta bai tab'a ba dan babu ma fuska hakan ya Kara kwadaita masa da san ya aureta ya ringa yiwa Iyayenta ruwan kudi,da yake mabukata ne da hannu biyu Suka rike shi, mahaifin Barakan ma idan zai gaishe shi sai ya rusuna,ba Kuma komai ya jawo haka ba saboda Yana da kudine. Sajeeda Ba abinda na saka a gaba yanzu sama da Addu'a dan tunda bakina ya daina yankewa da addua nake Jin dadin jikina,babbar matsalata yanzu Yaya Abu ce da naga ta karfin tuwo take so ta kasheni,yanzu bata tilasta min naci abinci bama ta kawomin,dan sai dai naji muryarta daga Palo,sai dai idan Yesmeen ta faki idonta ta kawo min naci. Bansani ba ko canza salo tayi ni dai addua kawai nake Allah ya kareni daga sharrrinta. Ina nan a kwance wajen sha biyu na Rana sai ga Abban Nusrah ya shigo yana washe baki,hannunsa rik'e da waya,yana "Ma Sha Allah na shigo d'akin sai dai kasan ba magana take ba,bani Nusrah"? Muryar mijin Nusrah da naji yasa na baza kunnena Ina jin Mai suke cewa,barka barka da naji Abban Nusrah nayi Yasa na gane Nusrah haihuwa tayi,tuni hawaye ya hau zubo min na faranciki dan ban taba kawowa Ina rayye zata haihu ba,tana yawan Kira ta layin Abban Nusrah da sai ya shigo zai fada min ta Kira wani zubin idan ta matsa Masa sai ya kawo wayar ya saka a handsfree,haka zatayi ta magana ita kadai tana min kuka da Addu'ar samun sauki,Ina Umman take Abba dan Allah kasa tayi motsi naji ana yin suna Zan taho"? "Ai kema kinsan ba iya motsin za tayi ba amma bari naga ko zatayi" Ya matso da wayar bakina "hawaye na zubo min na fara gurnani dan ta jini,bani da bakin magana Amma Addu'a nake akan Allah ya bata lafiyar shayarwa,cikin rawar murya ta fara magana tana "Umma Allah ya baki lafiya kina raina cikin nan ne dama ya hanani zuwa washegarin suna zanzo,in Sha Allah akwai wayanda na saka suke miki addua anan umma dan Kamar larurarki bata asibiti bace Unma Sunan ki zaa saka wa jaririya zaa ringa kiranta da ummi" Rabon da nayi murmushi Ina ga tun kafin Abban Nusrah ya kashemin rayuwa,maganar Nusrah yasa na saki murmushi na fara gurnani,Abban Nusrah ya d'auke wayar daga wajen bakina yana "Yau kinsa Umman ki murmushi rabon da naga fuskarta haka har na manta" "Allah Abba naji dadi, in Sha Allah umma zata
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111