Chapter 50
Chapter 50
na damko hannun Yesmeen da ta tsorata da yadda na mik'e a zabure Ina "Yesmeen bani labarin komai bani labari dalla dalla akwai Abubuwan da nake so nasani" Yesmeen daga ranar da ta fara leka Kabiru da duk Abubuwan da taga Kabiru nayi da idonta,da yadda bata iya bacci zuwa ranar da ta Kama shi Yana saduwa da Kare duk ta kwashe ta fada min, na saki ihu dana gane a ranar da ya sadu da kare a ranar ya sadu dani na damko Yesmeen cikin ihu Ina "Kin cuceni Yesmeen kin cuceni da baki fadamin da wuri ba Yesmeen sai da Abban Nusrah ya gama da rayuwata Kika zo kina fadamin kin kasheni Yesmeen dan da kin fada min da na dade da barin gidanan,da yanzu bai ci galaba a kaina ba yesmeen dani yake so yayi kudi,ya sace min wando,ya sace min audugar dana cire yanzu Kuma yaje ya sadu da kare yazo ya sadu dani,Yesmeen duk kinsan abinda yake ciki kinsan cewar ni yake so ya cuta baki tab'a fadamin ba yesmeen Karen da Kika kashe daga labarin da kike bani kawo shi yayi dan ya ringa saduwa dani, innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Yesmeen kin cuceni kin cuceni Yesmeen" Ihun kuka kawai nake Yesmeen na durkushe tana magiyar nayi shiru Ni kuwa na cigaba da ihun kuka,taya Zan kawo mijina uban yayana Wanda muka shekara Ashirin da biyu mun tafi na uku zai iya cutar dani akan neman duniya,yardar da na Masa yasa ko da Wasa ban taba kawo Masa zargin zai iya cutar dani ba,a kullum kyautata masa zato nake Ina munanawa abokinsa,taya zan tab'a kawowa dani yake so yayi kudi,a yau na wayi gari da manya manyan kuraje a jikina ruwa Mai doyi na fita a gabana,Ashe da Kare Abban Nusrah ya sadu yazo ya kwanta dani,kuka kawai nake kamar Zan shidde. Bugun da aka fara. Yiwa k'ofar yasa Yesmeen mik'ewa a gigice tana "shikenan asirinmu ya tonu" Yaya Abu ta Kara buga k'ofar da k'arfi tana "Wai me ke faruwa ne Sajeeda ihun mai ki ke yi ne?akan me zaku shige daka ku kulle k'ofa" Ko motsawa banyi ba jikin Yesmeen kuwa sai rawa yake dan bazata iya zuwa ta bude ba dole Yaya Abu zata gane tana gani,tasan indai ta bari Kabiru ya dawo gidan ya sameta sunan ta matacciya abinda zai fi mata shine ta gudu Koda babu kaya,da Wanan tunanin ta tsugunna a gaban Sajeeda dake wani irin gunjin kuka tana "Umma kiyi hakuri ki yafemin ban fada Miki bane saboda bana so na mutu ya rantse sai ya kasheni,ko a ranar da na gan shi da Karen nazo Ina buga Miki kofa ko Allah zai saka ki fito,umma ba Kuma lailai ki yarda Abba zai iya aikata haka ba Abba ya riga da yayi nisa umma ki yafe min rashin fada Miki da ban yi da wuri ba,umma tafiya zanyi bazan iya zama Abba ya dawo ya sameni a gidanan ba indai na zauna nasan kasheni zaiyi umma zan tafi zan ringa Miki addua nima kiringa min na fada hannu na gari ki yafe mun umma" Ta mik'e da sauri tana k'ok'arin yin waje na kamo hannunta Ina k'ok'arin danne kukan da nake har lokacin Yaya abu buga kofata kawai take kamar zata b'alle Numfashina kamar ya d'auke haka nake ji na rik'e Yesmeen Ina "Ba inda zakije Yesmeen bazan fada masa ba,dan da ace ma tuntuni kika fada min Yesmeen da ban nuna masa kin fada min ba,tawa ta riga da ta Kare tunda har ya bada jinina dan ya samu kudi,daga yadda nake Jin jikina nasan tafiyar tawa gajeriya ce a wanan lokacin ba abinda nake bukata sama da na ganku a gabana har zuwa lokacin da Allah yayi tafiya ta wanan shine kaddarata auren wanda na dauka mijina Mai kaunata ashe shi zai zama ajalina,karki damu bazan nuna masa komai ba dan ko na nuna Masa nasani ba abinda zai canza a abinda ya riga da ya faru iya lokacin da ya rage min zan ta rokar Allah ya tona masa asiri yarana Kuma Allah ya Kare su daga sharrin sa,ki cigaba da nuna wa bakya ganin saboda Kar ya cutar dake" Yesmeen na k'ok'arin magana na hanata dan naga a mugun tsorace take na Mik'e na nufi bakin kofata Ina Jin jiri da dibana kamar kaina ya fashe saboda ciwo,na bud'e k'ofar a daidai lokacin da Yaya Abu ta karbi wayarta daga hannun Yaya Asmau tana "gwara na Kira shi na fada masa abinda ke faruwa dan bangane wanan ihun kukan da take ta kulle k'ofa ba" Bud'e k'ofar da nayi yasa tayo kaina kamar zata kawo min duka" wanan wane irin rashin hankaline Sajeeda saboda me zaki kulle kanki a daki da Yesmeen ki ringa rusa wanan uban kukan,Mai yasa kika kasa yarda da kaddarar da Allah ya jefo miki,mutuwa Yesmeen din tayi naga gani ne kawai bata yi kin bi kin dagawa kan ki hankali irin wanan ai sai ki Kara saka yarinya a cikin damuwa" Ban iya ce mata komai ba na koma cikin d'akin ta biyoni tana cigaba da fada ni kuwa na kwanta hawaye na cigaba da zubo min,a Wanan lokacin ji nake kamar na zaunar da Yaya Abu na fada Mata cutar da Kabiru yamin,na bud'e mata jikina ta gani,a wanan lokacin ba Mai tsaya min sai jinina,amma nasan halin ta a yanzu Ina yi mata magana ba lailai ta yarda ba,ko ni da Kabiru yayi wa cutar nan na kasa yarda zai iya min haka, akan neman duniya ya zabi ya yanke ticket din tafiya lahira kudin da ko ya nema dole ya mutu ya bar shi,har mai na Masa da a rayuwa ya rasa da wacce zai yi kudi sai ni. Kuka kawai nake da na tuna da Kare ya sadu ya zo ya sadu dani, kila wani lakanin aka bashi akan sai ya sadu da kare kafin ya sadu dani,tunda daga ranar lafiya ta yanke min,ko a yanzu da nake kwance ruwan nan mai doyi ke zubo min. Yaya Abu kuwa hannun Yesmeen taja da ta maida idonta sama tana laluben iska Suka fice daga d'akin na maida idona na rufe Ina tunanin yadda Zan bullowa Kabiru batare da ya gane fadamin Yesmeen tayi ba. Kabiru A zaune yake a guess house din Rabiu Yana duba gidajen da aka turo Masa hotuna akan ya zaba dan so yake ya koma birnin tarayya wajen da Babu Yan sa ido, ballantana a samu wayanda zasu ga yadda yayi kudi tashi daya, a yanzu ya Kamata yaji Dadi ya more rayuwar sa,tunda yaje gidan Rabiuu yace Masa Yana hanya sai dai har yanzu bai iso ba,wayarsa ya ajiye tare da sauke ajiyar zuciya daya tuna yau zai fara sanin wata macen bayan Sajeeda,wani irin banbarakwai yake ji. Wajen karfe daya yaji dirin motar Rabiu ba jimawa sai gashi ya shigo da wasu Yan Mata uku duk basu wuce shekara Sha takwas zuwa ashirin ba,ba abinda Kabiru ke gani,sama da yayan cikin su,kallon Rabiu yake dan su hada ido ya mishi Karin bayani. Sai Rabiu ya zauna ya kalli Kabiru Yana "Abokina ga su nan fa da zafin su wacce ta maka a ciki duk Yan hannu ne kudi kawai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111