Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 20

Chapter 20

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,211 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

take kallo zanin da ke jikinta ma a yau tayi mafarkin ta dashi Ganin Sajeeda ta kallota yasa ta nufi wajenta tana "Sannu umma na shigo na duba ki ne da naga har sha daya baki fito ba" Sajeeda bata iya ce Mata komai ba dan gabanta zugi kawai yake mata. Mik'ewa tayi tana "Bari na shiga bandaki Ina zuwa" Tana shigewa Yesmeen ta fito jikinta na rawa dan boye tashin hankali da take ciki tayi dama tunda aka kawo Karen nan tasan da akwai manufar da ya saka Kabiru ya kawo karen, Yanzu Kabiru ya rasa wa zai cutar sai Sajeeda mai ta masa haka da ta cancanci irin wanan zaluncin daga wajensa a iya sanin ta da zaman da tayi a gidan,Sajeeda kullum k'ok'ari take ta kyautata masa amma sakayar sa zai yiwa Sajeeda kenan,kuka kawai take na tsananin tausayin Sajeeda bata san Mai ma'anar abinda ta gani ba bata san wane cutarwa Karen zai yiwa Sajeeda ba,ta riga da tasan sirrin Kabiru a yau Allah ya haska mata abinda Kabiru ke nufi da kawo Kare cikin gidan zata yi iya k'ok'arin ta dan ta taimakawa Sajeeda Koda kuwa nata rayuwar zai zama a cikin hatsari. Sake sake kawai take a zuciyarta Motsin Sajeeda da taji a palon yasa ta goge hawayen ta ta fita waje. Ta tarar da Sajeeda a zaune tayi fayau da ita kamar mara lafiya. Kitchen ta shige ta d'auko flask din da ta zuba Mata kunnun gyada da Kofi ta Kai Mata palon ta fara k'ok'arin zubawa Sajeedan sai Sajeeda ta daga Mata hannu tana "Bazan iya sha ba yesmeen bana Jin dadi bani da lafiya bansan Mai yake damuna ba ba daidai nake ba" Sajeeda ta karashe kwalla na zubo Mata Yesmeen kuwa ta zuba mata ido itama idonta ya ciciko da kwallan tausayin Sajeeda kila ma jininta ake zukewa. Cikin rawar murya Yesmeen ta fara magana tana "Umma Allah ya baki lafiya Wai me yake damun ki haka"? Sajeeda share hawayen daya zubo mata tayi tana "Bansani ba Yesmeen idan har Zan kwanta sai nayi mugun mafarki da Karen da Abban ku ya kawo na rasa dalili jikina ba kwari Ina Jin ciwo a jikina bansan Wanda Zan fadawa ya gane Mai nake ji ba,na fadawa Abban ku yace ran Alhamis zai fitar da Karen Kinga jibi kenan rabona da bacci mai Dadi har na manta har tsoron rufe idona nake yi" "Umma daga mafarkin nan da kike yi da Karen nan da Abba ya kawo Zaki san ba kalau ba kinsan wasu karnukan fa mayune Dan Allah umma ki dage da Addu'a ki daina ma bacci,idan za ki yi Addu'ar ki fito Palo kiyi saboda kiyi a nutse" "Ina yi Yesmeen sai dai Ina fara yi bacci zai daukeni ni gidanan gabadaya nake so ma mu bari nidai haduwar Abbanku da wanan abokin nasa bai zame min alheri ba dan sai da suka hadu nayi bankwana da kwanciyar hankali Ina ta so na nusar da Abban ku ya kasa gane kiga fa daga zuwa gidanan Annur dina ya kurmance wallahi banga alheri a tarayyar Abban ku da abokin nan nasa ba na dai cewa Abban ku ya maida Karen nan Inda ya d'auko yace jibi zai maida Karen" "Umma ki dai cigaba da Addu'a kafin kiyi bacci kiringa karatun Qur'ani" Kiringa kwanciya da alwala ni tunda na fara mugayen mafarkai na dage da Addu'a na rage mafarkin dan biyun dare nayi nake tashi nayi ta Addu'a" "Zan saita alarm a wayata in sha Allahu zan ringa tashi biyun daren So nake ma na Kira Abban ku nace masa zanje asibiti bana Jin dadin jikina zanje likita ya dubani" "Sannu umma ki daure ki sha kunun Kinga da zafin sa" Dak'yar Sajeeda ta sha kunun kamar wacce aka yiwa duka haka take jin jikinta. Daga sallahr asuba ta koma bacci,a cikin baccin ta taji Kamar ana zungura mata abu a gabanta ta rasa wane irin masifa ne wanan" Wajen biyar na yamma su Saifullahi suka shigo gidan a guje suna ihun murna Sajeeda dake can daki ta fito da sauri Yesmeen dake kitchen itama ta fito daga kitchen din tana kallon su Faisal ne ya fara magana cikin murna Yana "Abba ya siyo sabuwar mota dalelliya yana waje yanzu zai shigo" "Umma ke Kinga kyaun motar"? Cewar Saifullahi Yana washe baki Sajeeda Da ido kawai nake bin su dan ban ji digon farin ciki a zuciyata na siyan motar da suka ce Abban su yayi ba,ni a yanzu ma tsoron yadda Abban su ke kashe kudi yake dan naji Wai Yana shirye shirye tura Saifullahi kasar waje yayi karatu,a kasa da wata hudu Abban Nusrah yayi irin wanan kudin,anya kudin nan nasa na halal ne kuwa. Bakin sa a washe ya shigo palon Yana kada mukulli ya nufo wajen da nake tsaye Yana "Sajeeda na Miki sabuwar amarya fito waje kiganta" So nake na mishi tambayoyi amma na kasa Kamar wacce aka likewa baki haka nabi bayansa,na ga dalaleliyar motar a tsakar gidan,bansan kudin motar ba amma nasan masu kudi ke hawa irin motar nan Wanda ya isa ya tadda Kai" Yake kawai nake Ina Masa Allah ya sanya alheri cikin murmushi ya Miko mun mukulin Yana "Ke na siyawa Sajeeda babban burina dama na samu kudi kiji Dadi na faranta miki ba kaina na siyawa ba ke na siyawa" Sakin baki nayi ina kallon sa ya gyada min kai "Ni Kuma Abban Nusrah baka siyawa kanka ba sai ni"? "Kin cancanci na siya Miki Sajeeda" Girgiza kaina nayi na maida Masa mukullin Ina "bazan karba ba Abban Nusrah dan duk Wanda ya tambayeni Ina na samu motar Nan bansan mai zance Masa ba" Take ya hade rai ya hau masifa kamar zai kawo min duka Wai so nake nace sata yakeyi bata hanyar halal yake samun kudinsa ba" Nidai shiru nayi bance Masa komai ba. Sai gashi a ranar yayi fushi yak'i kwana a dakina duk hakurin da na bashi yaki ya saurareni. Washegari ma ko ta kan Sajeeda bai bi ba yana tashi ya Shiga kitchen ya dafa abinci dayaji namomi ya zuba a plate din da yake kaiwa Kare abinci dan da kansa yake hadawa Karen abincin da yake ci. Zuciyarsa cike take da farinciki dan a yau zai samu cikar burinsa dan idan komai ya tafar Masa yadda yake so ya zama multi millionaire Har ya d'auki abincin zai yi waje ya ajiye saboda fitsarin daya mugun matsar sa. Sai ya nufi bandaki dan yayi fitsarin. Yesmeen dake labe tana lekansa da tun jiya take Addu'a Allah ya bata saa da nassara. Ganin ya ajiye abincin yasa ta fito da balain sauri hannunta dauke da shinkafar beran da ta Nemo tun a jiya. Tana zuwa ta juye shinkafar beran gabanta na mugun faduwa. Ta fito daga kitchen kenan taci Karo da Kabiru cikin mugun faduwar gaba ta ja da baya ya shige yana watsa Mata mumunan kallo tayi waje da gudu. Ya d'auki abincin yayi bayan gida. Yana zuwa ya tsugunna a gaban Karen ya ajiye abincin a gabansa. Da sauri Karen ya fara cin abincin Yana kada jelarsa. Kabiru kuwa sai shafa Masa baya yake Yana tunanin yadda zaiyi a Daren yau dan abinda akace yayi

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});