Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 64

Chapter 64

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,250 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sosa ko'ina na jikina ba,kasana kuwa sai bulbulo da ruwa yake Mai doyi, Abban Nusrah kuwa ya farka daga baccin da ya fara d'aukar sa ya kalleni yana "Jikin ne Sajeeda sannu bari na dauko miki magani" Ya mik'e ni kuwa na cigaba da sosa jikina da naji kamar wuta ake huramin,yanzu ba iya kasana nake jin kaikaiyin ba duk jikina gabad'aya. Kuka kawai nake Ina Kiran Sunan Allah,ko maganin da Abban Nusrah ke miko min ban iya karba ba,kafin gari ya karasa wayewa jikiina yayi wani irin rudu rudu ya canza kala Kamar ba na mutane ba. Kabiru Hankalin sa ba karamin tashi yayi da yadda yaga jikin Sajeeda ya koma ba dan tuni duk fatar jikinta yayi wani irin duhun kala a idonsa ma sai yaga kamar fatar jikinta ya koma kalar Karen da ya sadu dashi, sallati kawai yake a ransa Yana tunanin abun yi dan shugaban su bai fada masa duk haka Sajeeda zata dawo ba,gashi yace ba abinda zai iya yi a akai haka Sajeeda zata tayi ta fama,da alama Sajeeda dak'yar ma take numfashi, hankali a tashe ya koma dakinsa ya d'auko wayarsa ya Rabiu a waya Yana d'auka ya fara zayyana mishi abinda ke faruwa,Rabiu kuwa ya hau tsara masa abinda zai yi da zai kau da zargin komai a zuciyar Sajeeda,ya kashe wayar ya turo Masa lambar Wanda zasu je wajen sa da bakin su ya zama daya. Kabiru kuwa kamar gaske ya koma d'akin Sajeedan da ta daina ma iya sallati sai hawaye da numfarfashi da take faman yi, Haka ya taso Yaya Abu akan tazo su Kai Sajeeda wani asibitin. Yaya Abu kanta sai da ta tsorata da yadda jikin Sajeedan ya koma, tafiyar mintuna Suka iso wani karamin asibiti batare da b'ata lokaci ba likitan da Kabiru ya Kira ya hau duduba Sajeeda, Kabiru da Yaya Abu na zaune suna kallon sa har ya gama ya fita. Sajeeda Kukan zuci kawai nake dan nasan tawa ta Kare ,ta k'arfi nakeso na damko Yaya Abu na fada mata Kabiru ne ya jefani a halin nan amma na kasa magana dan ji nake jikina Kamar ba nawa ba,abinda yake bani mamaki da Kabiru yadda ya nuna damuwar sa kamar bashi yayi kudi dani ba,har da dan hawayen sa yau daa ce bansan sirrinsa ba cewa zanyi nafi kowa dace da samun miji Mai kaunata dan Yaya Abu sai kwantar Masa da hankali take saboda ya kasa Zama waje daya duk wanan abin fa yasan asibti bazasu iya min magani ba, amma saboda ya nuna bai San komai ba yake ta sintirin kawo ni asibiti,Koda likita ya dawo bayanin da naji Yana yiwa Kabiru da Yaya Abu yasa hawaye ya fara gudu a fuskata,Wai a fadar likitar da nake tunanin hada baki yayi dashi Wai wani kwauro ne ya cijeni,wanda cizon kwaron guba ne,gubar ne ya haifar min da wanan kaikaiyi da canza fatar har ruwan dake zubo min a jikina,matsalar Kuma wanan kwaron ba lailai ko na Sha magani na warke ba sai dai ayi ta adduar sauki na ringa Shan magunguna akai akai, Abban Nusrah da Yaya Abu kuwa sai sallati suke, Abban Nusrah har da hawayensa Yana rik'e likita Wai ya taimaka masa idan da akwai abinda zai iya yi akai,likita kuwa yace ba abinda zai iya Yi akai ya cigaba da bawa Abban Nusrah hakuri akan ya daina daga hankalinsa kawai ya maida hankalina sa wajen kula dani kila a gaba a dace na warke. Abban Nusrah a tunanin sa bansan sirrinsa ba haka yayi ta min sannu Yana rike da hannuna har ruwan da aka samun ya Kare aka sallame mu bayan ya lafto uban magunguna Yaya Abu kuwa sai cewa take wane irin kwarone haka ita dai bata tab'a ji ba. Abban Nusrah kuwa ya hau ce mata akwai yasan ma wata da ya ciza. Haka muka dawo gida, Abban Nusrah ya ringa kula dani,Yana wani tattalani,ni kuwa kullum jikina Kara rikicewa yake a yanzu ko tashi bana iya yi, adduar zuci kawai nake dan wani irin rama nayi,ba abinda kake hangowa a jikina sai kasusuwana,jikina kuwa na ta fidda ruwa mai doyi,yanzu Abban Nusrah bama ya iya kwana a dakina,amma idan garin Allah ya waye kafin ya fita haka zai ta kula dani,har da dan kukansa wai duk ya nuna ya damu da halin da nake ciki,Yaya Asmau kuwa kullum sai ta kirani,ta dubani,ta Kuma shaida min ta saka a ringa min Addu'a ana min saukar ita tafi yarda da makiya ne suka jefe ni ba wani kwauro daya cijeni,daidai da mahaifina da mahaifiyata sai da suka zo dubani,ba Wanda zai zo dubani bai girgiza da yadda na dawo ba,duk Wanda ya tambayi Mai ya sameni haka,Abban Nusrah da Yaya Abu sai su hau bayanin kwaro ne ya cijeni shi yasa na dawo haka, tunda iyayena suka zo nake Neman hanyar da zan fada musu sirrin Abban Nusrah ko Zan samu su tafi dani su nemi mallamai su mun Addu'a,bansan Kuma ta yadda zan fada musu ba dan bana iya magana bansani ba ko wani abu Abban Nusrah yamin da ya saka naji bana iya magana, fadar tashin hankalin da iyayena suka Shiga da halin da nake ciki bata bakine dan mahaifiyata Gwaggo tunda tazo bata da aikin da ya wuce kuka,a gaban idonsu kuwa Abban Nusrah sai Kara kula dani yake, duk dan ya nuna musu Yana kula dani, Na lura so take ta kebbe dani,amma ganin Abban Nusrah yasa ta kasa sakin jikinta tana dubani sai ta fita,mahaifina kuwa kwana daya kawai yayi ya koma,akan zai Nemo min maganin gargajiya kila a dace, ana sauran kwana biyu mahaifiyata ta koma Abban Nusrah ya fita da zumar wai zaije ya dawo akwai kayansu da ya iso da zai je ya gani bazai Dade ba zai dawo. Fitarsa da minti biyar sai ga mahaifiyata ta shigo fuskarta cike da damuwa ta zauna a gefen gadon tana Kare min kallo hawaye ya hau zubo mata tana "Sajeeda Kinga yadda kika dawo kuwa?Wane irin kwarone wanan da zai cijeki ki koma haka,har cizon sa yasa kiringa fitar da ruwa mai wari haka daga gabanki?Wai me ke faruwa da ku ne haka?ya akayi Yesmeen ta makance?mai ya kurmantar da Annur,?na kasa gane Mai ke faruwa da ku haka,na tambayi mijinki yace dare daya kuka wayi gari Annur ya daina iya magana Yesmeen Kuma ta daina gani,duk a cikin shekara daya wanan masifar ta same ku haka mai yake faruwa haka? Gwaggo ta sosa min inda yake min kaikaiyi na hau k'ok'arin na bud'e bakina dan nayi magana amma na kasa alama kawai nake Mata da hannu dan a Kira min Yesmeen ko zan samu ta fadawa mahaifiyata abinda ke faruwa bani da sama da ita,ita zata iya taimaka min na fita daga hannun wanan azzalumin,amma mahaifiyata ta kasa ganewa sai kuka ta saka min tana adduar Allah ya bani lafiya tana Shan alwashin daina bacci dan addua kawai zata ringa min,karshe sai Yaya Abu ce ta shigo d'akin,ta ajiye kumatu tayi jajjir da ita saboda Jin dadin da ta samu da alama rashin lafiyar da nake Dadi yake mata dan tamkar ita ta Zama matar gidan,ita ke girki,ta ajiyewa Abban Nusrah nasa,duk abinda ranta keso kawai take yi,

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});