Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 90

Chapter 90

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,220 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

da kirjinta da taji kamar ya fado saboda tsoro ta mike da sauri,ta sa gudu,haka kawai dabarar sunkuya ya fado mata bawai dan tasan Kabirun bane dan tabbas da bata sunkuya ba ba abinda zai hana ya ganta. Gudu take da iya karfinta har ta fara hango titi,a madadin tayi titi sai ta yanki wani layi dan tasan zasu iya biyota. Ko kad'an bata san Kan garin ballantana tasan Inda take jefa kafarta ba, duk kwanar da ta gani fadawa kawai take,tana share hawayen tausayin Sajeeda da bata samu ta d'auko ta ba. Sai da ta tabbatar da tayi nisa ta samu wani k'ofar gida ta zauna tana maida numfashi,bata jima da zama ba taga an bud'e gate din gidan ta dago da sauri taga wani ne ya fito daga gidan zai Kai Kabiru a shekaru,hannun sa rik'e da carbi dan an fara kiraye kirayen sallah magriba, Ganin Yana kallonta yasa tayi saurin gaishe shi ya amsa cikin faraaa Yana "Yarinya daga Ina"? "B'ata nayi babba dan Allah ka taimaka min da kudin mota da tasha Zan tafi katsina da Yar uwata nazo munzo wani gida sai muka fito akan zamu tafi sai wasu Suka biyo mu,shine nabi ta wata hanyar tunda zu nake bulayin nemanta ban ganta ba" "Allah sarki,wajen wa kuka zo anan din"? "Aikatau aka kawo mu daga katsina shine wayanda muke yiwa aikin suka ce zasu yi tafiya Suka sallame mu" "Allah sarki Ina ga b'ata garine suka biyoku abinda za'ayi kizo mu Shiga ciki yanzu dare yayi bazai yu kina mace ki dau hanyar katsina ba gobe da safe idan Allah ya kaimu sai ki shirya a Kai ki Tasha kila itama Yar uwar taki ta gaji da nemanki ta tafi ita kadai" Yesmeen zubewa tayi a kasa ta hau yi Masa godiya yace ta biyo shi abaya. Ta mik'e tabi bayansa koda Suka Shiga wata ta gani a palon za ta kai Yaya Abu a shekaru,tana sanye da hijabi da carbi a hannunta. Sallamar da mutumin yayi ta amsa tana kallon yesmeen din dake biye dashi a baya. Yesmeen kuwa ta zub'e a kasa ta hau gaisheta itama cikin faraa ta hau amsawa mijin ya hau yi mata bayanin da Yesmeen ta Masa,itama ta ringa zuba Allah sarki tana ba komai ta kwana din gobe sai a Kai Yesmeen Tasha. Daga haka ta hau kwallawa wata Aisha Kira,Yesmeen kanta a kasa har Aisha ta karaso matar ta mata bayanin ta Kai Yesmeen daki,ta samu tayi sallah a zuba mata abinci idan ma wanka take so tayi a nuna Mata bandaki. Yesmeen ta hau yi Mata godiya Ta mik'e tabi bayan Yarinyar da zasuyi kusan saa daya. Suna Shiga d'akin yarinya ta nuna mata bandaki ta shige dan burinta kawai ta samu ta rama sallolin dake kanta dan ko azahar batayi ba tana sallah Rabin hankalin ta na wajen Sajeeda tasan yanzu Kabiru ya haukace da nemanta. Sai da ta rama sallolinta ta hau yiwa Sajeeda Addu'a akan Allah ya kareta daga sharrin Kabiru,dole tasan yadda zatayi a kaiwa Sajeeda a gaji kafin ya Kara cutar da ita dan har yanzu ta kasa gane Mai yaje nema a d'akin jiya daddare. Abincin ma da aka kawo mata kasa ci tayi dan ji tayi Sam bazata iya cin abincin ba. Tunanin da ya fado mata yasa tayi saurin kallon wacce aka kira da Aisha dake ta latsa wayarta ta ma shareta kamar batasan da zamanta a d'akin ba. Tayi gyaran murya tana "Aunty dan Allah ki taimaka min da Aron waya inaso na Kira Yar uwata" Aisha karamar wayar dake gefenta ta dauka ta mika mata batare da tace mata komai ba ta tashi tayi waje. Yesmeen kuwa jiki na rawa ta hau shigar da lambar Nusrah dan ba lambar Wanda ta rik'e a kanta sai lambar Nusrah da Sajeeda. Safa da marwa kawai take dan burinta Nusrah ta dauki wayar ta fada Mata halin da ake ciki. Tana Jin an dauka ta saki ajiyar zuciya tana "Nusrah Yesmeen ce kina jina"? "Yesmeen kece ko mafarki nake yi"? "Nice Nusrah ke kadai ce"? "Aaa nida Mama ne a daki tana yiwa jaririya wanka" Yesmeen kasa tayi da murya tana "kibar d'akin Nusrah magana Zan Miki Mai mahimmanci kiyi sauri" Nusrah mik'ewa tayi daga Kan gadon,tayi waje Yaya Abu dake yiwa jaririya wanka ta bita da Ido "Yesmeen ya akayi ba bar d'akin a Ina Kika samu waya taya akayi Kika kirani"? "Nusrah Umma tana cikin hatsari kiyi sauri ki kira Gwaggo taje ta d'auketa dan ni guduwa nayi Abba ne yake san kasheni"? "Kamarya Yesmeen bangane maganganun ki ba" "Nusrah bamu da lokacin da zan ringa Miki bayani kiyi saurin Kiran Gwaggo Abba shi ya jefa umma a halin da take ciki,nasan bazaki gane ba, Abba kungiya ya Shiga dan yayi kudi,toh da umma yayi kudin shiyasa take ta rashin lafiya labarin nada tsayi Abba ya San nasan sirrinsa shi yasa nayi karyar makanta,saboda Kar ya cutar dani, Nusrah Dan Allah banida lambar Gwaggo kiyi sauri ki kirata yanzu saboda gobe da safe taje ta d'auko umma Kar Abba ya sake cutar da ita"? "Yesmeen a hayyacinki kike kuwa kinsan Mai kike cewa kuwa Abban mu fa naji kina ya Shiga kungiya yayi kudi da umma innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Kamarya Wai kimin bayani bangane ba" Yesmeen da sauri da sauri ta hau bawa Nusrah labari. Nusrah kuwa jikinta ya dauki wani irin kyarma ta saki ihu tana "Abba ya cucemu Yesmeen ga mama nan ita zan gayawa yanzu nan" "Aaa Nusrah karki"!!! Kit taji Nusrah ta kashe wayar Yesmeen hankali a tashe ta hau Kiran wayar Nusrah Amma bata dauka ba. Bazata so Nusrah ta fadawa Yaya Abu ba. Nusrah kuwa dakinta ta koma tana kuka wiwi tana zuba sallati dan shakka babu ta yarda da maganar Yesmeen. Yaya Abu kuwa yadda ta shigo yasa ta ajiye jaririyar akan gado ta tarota tana "Wai waye ya kiraki a waya ne lafiya" "Mama Abba ya cucemu Abba ashe kungiya ya Shiga dan yayi kudi,Ashe Abba ba kudin Allah da Annabi ne dashi ba da umma yayi kudi,? Yaya Abu yamutsa fuska tayi tana "Kamarya bangane ba"? Tiryan tiryan Nusrah ta kwashe komai ta fada mata ta Kara da "Mama ki taimaka ki tafi daddaren nan Kar ya cutar da umma innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"? Yaya Abu Zama tayi a gefen gadon tana "yanzu Yesmeen ce duk ta fada miki haka ke kin yarda Abban ku kungiya ya Shiga ba sharrin yarinya nan bane? toh bar kuka haka kinsan me za'ayi yanzu nan zanje nabi motar dare naje na dauko Sajeeda karki sake ki fadawa kowa wanan maganar dan idan har Kika furta maganar nan Kamar kin tonawa Abban ku asirine kinji Mai nace ko" Nusrah Kai ta hau gyadawa tana "Mama ki ceto mana umma kiyi sauri Kar ya cutar da ita. Yaya Abu mayafinta kawai ta yafa ta dauki Jakarta tana "karki fadawa kowa maganar Nan Nusrah" Daga haka tayi waje da sauri tana yin nisa da gidan ta d'auko wayarta ta hau Kiran wayar Kabiru Ko kad'an tak'i yarda a zuciyarta da kungiya ya Shiga dan yayi kudi, karyar Yesmeen ne kawai,Ashe duk tsawon lokacin nan Yesmeen na gani,anya ba ita ta

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});