Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 107

Chapter 107

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,261 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sai da ta koma kukan zuci,shigowar shugaban a tsirara da wani tukunyar kasa dake ci da wuta yasa ta mik'ewa a zabure tana ya mata rai,Kar ya kasheta,bai ko saurareta ba ya ajiye tukunyar kasar,ya Ciro wani abu.kamar fifiken kaza daga tukunyar kasar ya nufo wajen da ta manne da bango ya hau shafa goshinta Yana gwarancin da bata gane ba, ihu kawai take tana sallati,idan tayi sallati sai ya buge bakinta,a haka ya Kara ficewa daga d'akin,Yaya Abu kuwa ta zub'e a kasa ta hau Kiran sunayen Allah dan da iliminta sarai,kawai shagala yasa bata wani maida hankali,zata so ta nemi yafiyar Iyayenta kafin ta mutu,zata so taga Sajeeda ta nemi yafiyar ta zata so taga Yarta kafin ta mutu, tun tana iya Addu'a da k'arfi har sai da taji numfashinta na neman d'aukewa. Haka ta kwanta tana Jin azabar radadi a jikinta,ga zazzabi mai zafi,da ace bata biyo Kabiru ba da kila ta samu ta tsira Koda babu kudin. Tana nan a kwance taga shugaban ya dawo da wasu maza uku da ido ta ringa binsu dan bata da karfin motsawa sai hawaye dake zubo Mata,umarni ya bawa daya daga cikinsu akan ya dagata ayi mata aski a fita da ita dan karfe biyar zai yanka ta. Mik'ewa tayi cikin tashin hankali da taji yankata zaiyi tuni ta nemi rashin lafiya da take ciki ta rasa ta hau ihu tana Kiran sunayen Allah akan yazo ya taimaka mata,tana ji tana gani suka ririketa Suka Mata kwal kwabo,suka daga ta sama suka fita da ita waje bayan sun bade kanta da wani abu da take tunanin Hoda ne. Kashi da fitsari haka ta ringa saki saboda akwai tashin hankali Wai kaga mutuwa da idonka,wayanda zasu kashekan ma basu San Allah ba balle suyi imani, a wani karamin daki suka ajiyeta dake d'auke da kwarangwal din kawunan mutane,suna ajiyeta suka fice daga d'akin. Yaya Abu da take Jin Kamar ta mutu ma tun kafin a kasheta ta fara sallati tana neman hanyar da zata gudu,kamar ance ta kalli bakin k'ofar ta hango abu kamar mukulli jiki na rawa ta karasa bakin kofa tana zuwa ta dauki mukullin Kamar Wasa ta zura a k'ofar taga ya bud'u. Ta bud'e k'ofar a hankali ta fito, batasan ma wajen da suka ajiyeta ba dan kamar bayan gidan ne, ga karnuka nan sunfi hamsin da aka daure,tuni ta fara neman hanyar da zata bi ta gudu,sai dai duk Inda taso ta samu hanya bata samu ba,waige waige ta hau yi ta hango wani drum a kife a wajen katangar,da balain sauri ta danne drum din har tana kurjewa a kafa ta daka tsalle ta hau katangar ta dira,tana dira ta sa gudu,duk da batasan Ina ta nufa ba haka ta ringa tikar gudu,kayoyi na soke Mata kafa ko damuwa batayi da ta tsaya ba,sai da ta fara Jin jiri,da rashin k'arfi tun tana daurewa har sai da duhu ya gifta mata ta yanke Jiki ta Fadi ..... Kuyi hakuri,wallahi wayata ta samu matsala sai da ya goge gabadaya wajen tara na sake typin gobe dai zan gama in Sha Allah naso a yau na gama *WANAN NOVEL DIN NA KUDI NE NA HADA KU DA FIYAYYEN HALLITA ANNABI MUHAMMAD SALLAHU ALAIHI WA SALAM KARKU MIN SHARING NOVEL IDAN BANA KALLON KI ALLAH YANA KALLON KI KUDIN KARATU KIKA BIYA BANA MALLAKA BA IDAN KIKA FITAR NA BAR KI DA ALLAH GA MAI BUKATA SAI TA BIYA 500 ZUWA WANAN ACCT DIN 2029764071 FIRST BANK NAFISA NUHU KO KATIN MTN TA WANAN LAYIN 08033719070 KO WANAN LAYIN 08068484400 SAI A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANAN LAYIN 08033719070 KO WANAN LAYIN 08033719070 MUTANEN NIGER KUMA SU NEMI WANAN LAMBAR +227 96 82 89 84* *PAGE* *97-100* Yaya Abu Bata Kara sanin inda take ba,bata San tsawon lokacin da ta dauka a sume ba,sai muryar mutane taji a kanta,Inda ta bud'e idonta a hankali tana kallon sama sai da ta dau tsawon lokaci ta tuna abinda ya faru da ita,ta fara k'ok'arin mik'ewa zaune dan taga Inda take,sai dai sam jikinta yak'i bata had'in kai,dan ji take jikin nata ya mata wani irin salaf kamar an kwashe komai na jikinta ga Abu da taji Yana zubo mata da ko daga kwancen da take tana shako warin,sai ta hau hararo yadda take kyankyamin Sajeeda take fesa turare idan zata Shiga dakinta,ta hararo yadda take yiwa Sajeeda idan ta b'ata waje,idan ma taimaka mata za tayi haka zata ta mata da mugunta,Ashe itama watarana zata wayi gari ta zama tamkar Sajeedan zata iya cewa ma tafi Sajeedan dan ita kadai tasan mai take ji,bata San Mai ya hau kanta ta bawa Kabiru kanta ba,batasan Ina kunya da tunanin ta ya tafi ta bar Kabiru ya nemeta ba,duk ba wani abu ya jawo mata haka ba sai San kudinta,yau da ace ta ji maganar Nusrah da kila bata tsinci kanta a wanan halin ba, gashi dai tana ganin yadda Kabirun ke wadaka da kudi,amma rufewar da idonta yayi yasa ta kasa yarda kudinsa bana halal bane, rufewar da idonta yayi yasa ta so kashe Sajeeda duk saboda ta samu abin duniyar da yau a garin kwadayinta gata a kwance bama tasan Inda take ba,da yanzu tuni an yanke mata kai,yau da ta samu taci galaba a kashe Sajeeda da ya zata yi Ina zata Kai wanan nauyin,ta tuna yadda Babansu yace Kar ta sake tazo Masa gida,ta tuna yadda tayiwa babba yalwa rashin kunya akan tace tazo su tafi gida bai dace ta zauna a gidan Sajeeda ba,Ina ma lokacin tabi su babba yalwan ta tafi da kila duk bata tsinci kanta a wanan halin ba kuka ta fashe dashi,tana tuno yadda Sajeeda bata iya magana,da yadda take buga kanta a bango idan tana san tayi magana,yanzu ma batasan Inda take ba,kuka kawai take a daidai lokacin da taga wata mata ta tsaya a kanta tana "Mama kizo kiga ta farka" Sai a lokacin ta kalli Yar budurwa yarinya da ke sanye da daurin kirji, ta toshe hancinta da hannu biyu ga wani tsagu a fuskarta hausar ma da tayi Kamar ba bahaushiya ba,yadda ta toshe hancinta yasa taji wani irin kuka ya taho mata Ashe haka Sajeeda ke Jin ciwo idan ta toshe hancinta, isowar wata dattijuwar Mata da itama ta toshe hancinta tana gurgurarren hausa da "Ai kuwa ta farka bari babanku ya dawo a gaskiya gwara ya maidata Inda ya d'auko ta dan bazai yu mu zauna da ita tana wanan warin ba,na gaji da kwashe kashin dake zubo mata,ni kamar har tsutsa take fitarwa tunda nake ban taba ganin mai irin larurarta ba" "Wallahi mama warin fa har daki tunda ta farka a tambayeta Ina ne gidansu sai a kaita dan gaskiya da cutarwa zamanta a gidanan. Yaya abu da ido kawia take binsu hawaye na zubo mata daga maganarsu ta gane tsinto ta mai gidan yayi,so take ta bud'e baki tayi magana amma ta kasa so take tace su taimaka mata su kaita garinsu amma ta kasa magana numfashin da take ma dakyar takeyi,yanzu shikenan bazata iya magana ba,da ido ta ringa bin su tana Jin datijuwar na rokon Yar budurwa akan ta kaita bandaki a dan wanke mata jiki,yarinyar ta hade rai,a haife

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});