Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 55

Chapter 55

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,237 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ba,mai tayi?laifine dan an tausayawa halin da take ciki,tashi daya Muka wayi gari ta daina gani, iya wanan bai Isa yasa a tausaya mata ba sai ace zaa koreta,yau kina tunanin da Nuratu na rayye zata ji dadin irin yadda kike yiwa yarta ?karki manta fa baa san ranta ta mutu ta barta ba yau da bana rayye ke mai rik'e Yesmeen ce ban taba zaton haka daga wajenki ba" "Ikon Allah Wani Abu akace zaa yiwa Yesmeen din kike zuba wanan dogon bayani,kina magana kamar ni na kashe Nuratu,kina tunanin idan Nusrah ce zata ringa daga miki hankali haka,yarinya tun jiya ta Hana mu sukuni,kike ta zuba dogon bayani kinsan da mota ta kadeta da ta fita dinan dangin babanta ba yarda zasu yi ba karshenta sai sun kulle ki" "Ai na ma gama magana Yaya Abu Ni ke auren Sajeeda ba ita ke Aurena ba bata isa ta juya ni ba a karkashin ikona take da yardata ta rik'e Yesmeen a yanzu Kuma nace ta maida Yesmeen wajen mahaifin ta tunda Yana rayye ba mutuwa yayi ba a goben Nan Zan maidata" Tunda ya fara magana wani irin Abu naji ya tsaya min a zuciya,wutar kiyayarsa ruruwa kawai yake a raina ji nake kamar na samo wuka nayi ta yanyanka shi yanzu alwashin da nake Sha ma bazai ci kudin nan ba yadda yake san yaga ya kasheni sai dai mu tafi tare bana Masa fatan Rahamar Allah daga Rana irin ta yau har zuwa karshen numfashina addu'oi masifa da balai Zan ta Masa,tunda har dani zai yi kudi,ba abinda zai hana naso ganin bayan sa. Ganin Yana k'ok'arin barin palon Yana ta sheka rantsuwa yasa na fara magana cikin bacin rai Ina Jin ruwanan na zubo min Mai doyi "Wallahi ba inda zata je Abban Nusrah idan har ka dage ka gaji da rukonta sai ka sallameni nima na tafi,haka kawai ba abinda ta maka zaka koreta,baka tashi korarta ba sai da ta daina gani,mai zaka cewa mahaifinta ya makantar Mata da ido,a haka na d'auko ta,har yanzu baka ji a jikinka mutane zasu fara zargin akwai wani abu dake faruwa a gidan ka ba kasa da wata biyar ka Zama hamshakin mai kudi,Dan cikin ka ya kurmance yanzu itama Yesmeen ta makance kila nan gaba ma mutuwa za'ayi,duk wani abu na faruwa da dalili banda na gidanan,Koda kaddara Allah ya Aiko akan ce ga dalili kafin aukuwar kaddarar amma na gidanmu daban ne Annur daga kwanciya bacci ya tashi ya daina magana Yesmeen daga kunna fitila ta daina gani,sai nayi magana ace ba haka ba idan har ka shirya korar Yesmeen ka dawo mata da ganin ta sai ta bar gidanan" "Yaya Abu Kinga yadda ta juya zancen nan ko,banda Sajeeda bata da ilimi bata san yadda Allah ke juye lamarin sa dare daya ba,a cikin awa daya idan Allah ya so azurta bawan sa a yanzu Allah zaiyi silar da zai yi arziki,yanzu Mai ya hada kurmancewar Annur da makancewar Yesmeen da arzikin da Allah yamin yanzu ace matata ke min wanan zargin idan wani taji yana so ya zargeni ita ba mai hanawa bane,wanan wane irin abu ne,yanzu ba abin zargi a wajen ki sai ni kenan Shekara ashirin da uku muna tare ace baki san halina ba?baki San abinda zan yi da Wanda bazan iya ba mai kike nufi duk da kalmomin nan da kikayi da mutane zasu fara zargina"? Kallona kawai yake Yana hucci cikin bacin rai Yaya Abu kuwa ta fara bashi hakuri tana "Hakuri zaka yi Kabiru Sajeeda halin ta sai ita na rasa wacce iri ce ita idan har dan ance zaa Mai da Yesmeen take wanan maganganun sai kayi hakuri ka barta kana kallo ma ni da nake yayarta yadda ta hayyaya ko min kamar zata kawo min duka,yanzu da mutane na nan kaga sai su dauka ni muguwa ce Allah dai ya kyauta "Kuna dai kallon irin abinda take min toh wallahi na fara gajiya Sajeeda bata San darajar miji ba duk maganar daya fito a bakin ta fadamin kawai take ni kuwa na gaji bazan dauka ba" "Ya bazaka gaji dani ba tunda ka Gama Dani ya bazaka gaji ba tunda kayi kudi dani,ai a yanzu bani da wani amfani a wajen ka tunda har ka sadu da kare kazo ka sadu dani,bani da abin mora yanzu dole ka gaji dani" Abinda naso Fadi kenan sai na juye da "Tunda bansan darajar miji ba ya zaayi kenan"? Na jefa masa tambayar Ina ciza lebbena dan takaicin maganar daya fito a bakina "Aure zan Kara Sajeeda idan na Kara Aure watakila ki shiga hankalin ki" Daga haka ya juya a fusace yayi d'akin sa na bi shi da kallo hawaye na zuraro min inama Yesmeen ta fadamin da wuri kafin Kabiru ya cutar dani,dama sai da na ayyana haka a raina kila ya zabi yayi kudi dani ne Saboda ya kau dani yayi aurensa yaji dadin rayuwarsa,ni Dana Sha wahala dashi a madadin ma idan gajiya yayi dani ya sauwake min cikin ruwan sanyi na tafi da lafiya ta shine ya zabi ya cutar dani,yadda nake Jin kasana nasan Abu ne mawuyaci na dawo yadda nake,duk a tunaninsa bansan sirrinsa ba,yau ban da Ina tsoron jefa Yesmeen a cikin masifa da a yau Kabiru ya gane kuransa dan sai na Tara Masa jama'a,Amma a yanzu nasan mai Zan yi Dan idan har na bar maganar a cikina zuciyata na iya fashewa dan bakin ciki. A haka naja kafata na shige daki Ina jiyo muryar Yaya Abu na idan bana so ayimin kishiyar sai na Shiga hankalina da itace a d'aular da nake ciki da an sha mamaki dama idan Dadi yayi wa mutum yawa sai yace Dadi kasheni. Ban juya ma na kalleta ba har shige d'akina Nusrah ta biyoni bana Jin zan iya Mata wani magana yanzu dan Ni kadai nasan mai nake ji ga ciwon zuciya ga na jiki. Haka ta karaci zamanta ta gama koke kokenta akan makancewar Yesmeen tayi kasa da murya akan na taimaka na fada mata abinda nace Zan fada mata dan idan ta koma gida ba lailai ta samu nutsuwa ba haka za tayi ta tunani Ce mata nayi Kar ta damu zamu yi waya ba wani abu bane,bana jin a yadda na ganta a cikin damuwa akwai abinda zan iya gaya Mata haka ta zauna a d'akin tayi ta zuba min Sannu kafin ta tafi gidan ta ma sai da ta Mana abincin dare sai tausayina take tana yanzu wa zai na tayani aikace aikacen gidan tunda Yesmeen bata gani, Murmushi kawai na Mata nace kar ta damu su Saifullahi zasu ringa tayani tunda duk sun iya ji nake kamar na fada mata Yesmeen na gani yadda naga ta damu sai Kuma na fasa Ina tunanin mata magana ko ta waya ne ya zama dole na tashi tsaye na nemi mai taimaka min da Addu'a na kubuta daga hannun wanan azzalumin mutumin. Yesmeen Tunda Yaya Abu ta d'auko ta daga d'akin Sajeeda taji gabad'aya ta kasa samun nutsuwa,tayi nadamar tona sirrin ga Sajeeda yafi a kirga, dan tasan ba lailai ta iya dannewa ba zata iya tarar Kabiru da maganar. Kuka kawai take tana tunanin abin da ya Kamata

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});