Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 6

Chapter 6

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,210 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

akan gado Ko a wani wajen kaga da kunya ko" ""Umm ni dai na tafi massallaci sai ki dage da nema" Yayi waje. Sajeeda Kuma ta shige bandaki dan tayi wanka ta yanke idan ta iddar da Sallah sai ta gyara d'akin ko zata gani. Kabiru kuwa yana fita ya labe daga waje Yana kallon lokacin da su Saifullahi suka fito daga gidan suka nufi massallacin. Sai Kuma yaji kirjin sa ya masa nauyi Mai bambanci Arne da musulmi sallah ce fa, yanzu haka zai yi sati kenan ba saka goshin sa a kasa ba? tuna irin kudin da zai yi yasa ya ture tunanin a ransa dan a wanan yanayin da yake ciki kudi kawai shi ne burin sa dan Rabiu yace masa Rabin masu kudin garin nan duk ta haka suka yi kudin su. Sai da ya ga yaran sun dawo sun shige ciki shima ya fito daga lungun da ya b'uya ya Shiga gidan. Koda ya Shiga daki Sajeeda ya Tarar ta daddage da neman pant da hijabin da tayi sallah a jikinta har zanin gadon ta canza sabida Neman da take shi kuwa ya hade rai dan ko da wasa baya so ya bata fuskaar da zata ishe shi da maganar pant din ta. "Abban Nusrah kaga har daga katitar nan nayi wlh Babu pant ba dalilin sa" "Mtsss kina da matsala wlh Tom mai Kika daddage kina nema daya ne dake"? "Aa ba dayane dani ba Ina ta mamakin yanda zan kwana da abu a gefena yanzu na duba ko sama ko kasa bangani ba" "Baki da abin yi ne Sajeeda ki cigaba da nema idan Kuma ba barawone ya shigo ya rasa mai zai dauka sai wandon ki" Kabiru yace tare da Jan siririn tsaki,ya kwanta Yana zai koma bacci karfe goma ta tashe shi daga bacci zai je wajen abokinsa da ya bashi kyautar kudi yace masa yaje Yana san ganin sa. Da toh ta bishi ta fito daga dakin tana tunanin kila wani wajen ma pant din yayi ta tsaya wahalar da kanta. Tare suka yi abincin karyawa da Yesmeen dake bata labari taji motsi jiya a bayan windonta,ko baccin arziki bata yi ba Dariya Sajeeda ta saka mata ta ringa ce mata matsoraciya yanzu haka b'eraye ne. Sajeeda Tare muka ci abinci da Abban Nusrah da yazo fita ya bani Dubu biyar Wai nayi cefane har ga Allah daga jiya zuwa yau bansan kalar Farin ciki da Addu'ar da nayi wa Abban Nusrah ba, hakika ya kyautata wa nida yarana,dan ko da Abban su ya fita suka shigo hirar kyautar da aka musu kawai suke Annur kuwa ya hau cewa "Nayi mafarki Abba ya Zama mugun Mai kudi Wai ya gina wani gidan bene duk muna ta murna amma ban ga umma a gidan ba" Murmushi na saki Ina "idan baka gani a gidan ba wata Abban ku ya auro kenan,a lailai auta kyautar da aka ma ya maka dadi irin wanan mafarki haka. Tare muka yi aikin abincin da aka kawo min da Yesmeen dan Kamar na mayar nima na dan huta tunda na samu Yan canji,dan daidaikun Rana ne baa kawo min aikatau Kuma har ya zame min jiki. Da yamma Ina d'aki sai ga Abban Nusrah ya shigo gidan da sallama fuskar sa Kamar gonar auduga ba kowa a gidan sai ni kadai dan duka yaran sun tafi islamiya. Nima ganin fuskarsa a washe yasa nima na washe bakina Ina "Abban Nusrah Mai muka samu ne naga fuskar ka d'auke da Annuri haka" Zama yayi a gefena Yana "Sajeeda Ina ga mun kusa zama masu kudi" "Allah Abban Nusrah abokin naka ya nemo ma aikin ne"? "Daga wajen sa nake yanzu haka ai yanzu ma zama bai Kama ki ba tashi Zaki yi mu tafi ki tayani yi masa godiya Kinga yau ma kudin daya bani kyauta Sajeeda" Gwalo ido nayi a lokacin daya bud'e ledar dake hannun sa wrapper Dubu Dubu ne guda biyar,mik'ewa nayi na dafe kirjina Ina "Abban Nusrah duka wanan kudin ya baka aikin me yake yi haka"? "Ke kinsan kudin sa kuwa wanan ai ba komai ne ma a wajen sa ke baki ga alkawarukan da yamin ba a ciki kuwa har da kyautar gida yace bazai manta alherin da na masa muna Yara ba" Kudin daya dora a cinyata kawai nake juyawa har ga Allah sai najini a tsorace tambayoyi nake so na yiwa Abban Nusrah amma bana so na rusa Farin ciki da yake ciki,a wanan zamanin har wane irin kudine da shi haka jiya ya bashi kyautar dubu dari biyu yau Kuma ya d'auko dari biyar ya bashi. "Wai ya na ga ba kya farinciki ne Sajeeda Allah ne ya turo min shi ya taimaka min fa Allah yasan tsawon shekarun da na dauka Ina aikin wahala" Murmushi yak'e nayi Ina "ba haka bane Abban Nusrah Mai zai hana ni murna kawai Ina ta mamakin yanda daga jiya zuwa yau ya iya baka kyautar dubu dari bakwai zugudum a wanan zamani ko dan uwan ka ke da wanan kudin ba lailai ya iya baka irin wanan kyautar ba" "A wajen masu kudi kyautar dubu dari bakwai ba komai bane Sajeeda sabida dai bamu da kudin ne shi yasa kike ganin yawan kudin, ba za ki gane abinda na ke fada ba sai anjima idan mun je gidan Zaki tabbatar da ko miliyan daya ya bada kyautarsa ba zai ji komai ba" "Allah ya saka masa da alheri" "Ameen Ameen ai idan ya samo min aikin nan sai na siya miki tsalallen mota,su Saifullahi ma sai na bi su da motoci" "Allah ya yarda yasa arzikin na alheri ne a gare mu Abban Nusrah kasan wani arzikin masifa ne,ni wlh a rayuwata rufin asiri kawai nake so bani da wanan burikan tashin hankalin indai zanci sau uku a rana yarana su kawo bukatar su na musu ba tare da na gaza ba wlh Alhamdulillah" "Sajeeda kenan yanzu dai tashi kije ki boye mana kudin ki zo ki fada min Abubuwan da ake bukata a gidan" D'aki naje na boye kudin na dawo wajen sa duk jikina a sanyaye bansan mai yasa ban ji Ina mugun Farin ciki ba shi kuwa sai zuba yake yana lissafa yadda idan ya samu kudi zai canja mana rayuwa ko girki da na so dorawa hana ni yayi yace yau bazaa yi girki ba Kuma bai yarda na Kara karbar aikatau ba. Koda Yara suka dawo haka ya tara su Yana tambayar su abinda suke so. Tuni duk suka haukace da murna daga Mai cewa machine yake so sai Mai cewa keke yake so Annur kuwa sai tsalle yake Yana mafarkin sa ya tabbata Abban su ya Zama Mai kudi,Abban Nusrah kuwa sai washe baki yake Yana su Kara saka su a addua ai Yana ganin nan da sati biyu zamu bar gidanan. Ni dai da ido nake bin sa yanda ya hakikance Yana zuba lissafi Taya mutumin da ba shi da ko asi sai ya fita yayi buga buga tashi daya ya ringa wanan lissafe liisafen sai Kuma nayi tunanin Allah Kan iya azurta bawan sa a dare daya zai Kuma iya talauta bawan sa a cikin mintuna. Bayan sallah isha yace na shirya mu

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});