Chapter 62
Chapter 62
su. Sai da suka gaisa da yaya Abu ya shige d'akinsa sai da yayi wanka ya fito yana jin sa a cikin nishadi,batun sallah kuwa babu,dan yanzu idan akwai abinda ke Masa wahala bai wuce sallah ba,dan ba kowane lokaci yake yi ba,yau ba karamin dadi yaji da Yan matan da Rabiu ya hada shi dasu ba,har ga Allah daya daga cikin su ta kwanta masa Husna ya samu yadda yake so,dan har lambarta ya karba dan ji yayi ma zai iya aurenta bata fi sa'ar Yesmeen ba. Koda ya fito d'akin Sajeeda ya shige dan ya dubata. Sajeeda Mafarkin da nayi ya tsaya min a zuciya dan kasa ma samun nutsuwa nayi,sai da na saka Saifullahi ya ruko mun hannun Yesmeen ya kawota d'akina, daga mafarkin nan da nayi nasan cewar dagani har Yesmeen muna cikin mugun hatsari nama Shiga hatsarin tunda Kabiru ya gama dani, Yesmeen na ganin Saifullah ya bar d'akin tayi saurin Mai do da fuskarta kasa tana "Umma ya jikinki"? Sai na cije lebbena dan ni kadai nasan mai nake ji a jikina dan yanzu kasana ma ji nayi Yana numfashi shi kadai, "Umma dan Allah dan Annabi karki nunawa Abba kinsan komai wallahi dazu ma sai da ya zo har dakina ya shakeni ya Sha alwashin kasheni idan har sirrinsa ya fita Umma wallahi Abba zai iya kasheni ki taimaka min ki rufe sirrin nan, mu dage da Addu'a da saukar Qur'ani, in Sha Allah zaki warke idan guduwa ma zamu yi sai mu gudu" Girgiza kaina nayi ina "Yesmeen ranki da nawa a hannun Allah yake yau ko mutuwa nayi,lokacina ne yayi,ji nake idan ban tona sirrinsa ba bazan samu kwanciyar hankali ba,dan ya fara tunani tura su Saifullahi kasar waje,idan har zai iya mun wanan cutar ya kurmantar da Annur dan ya siyar da su Saifullahi ba wahala zai Masa ba gwara na nuna masa nasan sirrin sa" Yesmeen zubewa tayi a gabana ta hau magiya sai kuka take tana na rufa mata asiri Abban nusrah kasheta zaiyi idan na nuna masa nasani Na ruko hannun ta Ina "Ki kwantar da hankalin ki bazan nuna Masa ke Kika fadamin ba,ba Kuma magana Zan Masa ba da kaina nake so na gano sirrin sa ya Kuma san cewar nagani din ba fada min aka yi ba da naso na fadawa su Saifullahi sirrin sa dan su san cewar zai iya yin kudin dasu suma amma na fasa fada musu zan dai hana tafiyar tasu" Yesmeen magiya kawai take akan na rufa Mata asiri sai da na rantse mata akan bazan fada masa komai ba ta samu nutsuwa dan na yanke abinda zan yi bazai tab'a zargin Yesmeen ce ta fada min wani abu ba. Bayan fitar Yesmeen daga d'akin Yaya Asmau ta shigo na fada mata ta bar Yesmeen ba sai ta tafi da ita ba Yaya Asmau tafi nuna kulawar ta a kaina akan wacce na Kira da yayata ni gani nake ma Kamar murna take da rashin lafiyata tunda duk zata yi abinda ranta ke so. Ba Mai hanata. Kafin Yaya Asmau ta koma dakinta na Kara rokonta akan ta saka mallamai suyi min Addu'a da sauka tamun alkawari da zata saka ayi min Addu'a. Ba ta kuwa bar dakina ba sai da ta tabbatar da naci abinci Yaya Abu bata lekoni ba sai wajen goma ta shigo tana har yanzu bata ga Abban Nusrah ya dawo ba dama yana dadewa hakane"? Kai kawai na gyada mata. Ta sa Kai ta fita. Tana fita na fara susa dan wani irin kaikaiyi naji kamar na cire gabana na Yar ga ruwan dake bulbulo min duk wanan masifar uban yayana ne ya jefani saboda abin duniya. Haka na kwanta Ina zubar hawaye idan ya lafa na daina idan ya motsa na cigaba da susa,Ina Jin lokacin da Abban Nusrah ya dawo na dauka zai lekoni sai naji shiru Wanda hakan na nufin dakinsa ya wuce sai da ya dau tsawon lokaci naga ya turo k'ofar d'akin ya shigo sanye da jallabiya kudin haram sun zauna masa dan har wani kiba yayi Yana sheki. Ya zauna a gefen gadon Yana "Sannu Sajeeda ya jikin naki"? Mik'ewa nayi na zauna Ina "Abban Nusrah dare daya na wayi gari da wanan masifar a jikina,a ranar da na fara Jin canji a jikina a ranar da ka kusanceni ne na karshe Abban Nusrah shekara ashirin da doriya muna tare Kai ma kasan ban taba cuta makamancin wanan ba,Mai zai jawo min wanan masifar"? Wani irin kallo ya fara min cikin hade rai ya fara magana Yana "Toh mai kike nufi da tunda na kusance ki na karshe kika ji jikinki ya canza kina nufin ni na saka Miki cuta ko me?idan a jikina kika kwashi wanan cutar ni zaki gani haka ne,wanan cutar kila a bandaki Kika kwaso ko a wani wajen dan haka ki cigaba kawai da Shan magungunan da aka Rubuto miki Zaki warke a hankali kinci abinci"? Ba karamin daurewa nayi na danne abinda nake ji ba,na gyada masa Kai da naci abincin ya fara magana Yana "Ina ganin ya Kamata Yaya Abu tazo ta ringa tayaki kwana ni sai na ringa kwana a dakina har zuwa lokacin da zaki warke" "Tun baaje koina ba Abban Nusrah ka fara guduna kenan bazaka iya kwana da ni waje daya ba"? "Aaa Sajeeda akan me Zan gujeki,kawai Ina ganin a yanzu kina bukatar kulawa sosai,shi yasa nace tazo ta ringa kwana anan ai na dan lokacine" "Abban Nusrah bana so Yaya Abu tazo ta kwana Kai nake so ka kwana din idan Kuma dan larurata zaka ki kwana dani shikenan ba komai" Nace Ina Jin kamar na shako shi har sai ya daina numfashi so nake na Kama Abban Nusrah da kaina shiyasa nake so mu ringa kwana waje daya. Kabiru kuwa ganin Sajeeda ta dage yasa yace zai kwana din zuciyar sa fal da tunanin yadda zai gudanar da abunsa ba tare da su Yaya Abu sun gan shi ba. Haka ya ringa sintiri daga dakinsa zuwa na Sajeeda Yana tunanin yadda zai yi,bai san mai yasa wankan sai a bayan gidan zai yi ba ji yake Kamar ya taso su Yaya Abun yace su koma dakinsa su kwanta. Haka yayi ta juye juye har Sha biyun na dare Yana Jin saukar numfashin Sajeeda dake nuni tayi nisa a bacci,a hankali ya lekata ya ga baccin dai take cikin sand'a ya mik'e ya fito daga d'akin. Ya nufi bakin k'ofar d'akin Yesmeen ya Kara kunnensa Dan yaji ko zai jiyo motsin su ba abinda yake ji sai karar fanka. Cikin sand'a ya koma dakinsa ya jawo tukunyar kasar da ke d'auke da ruwan maganin ya tube Zigidir Yana jira daya ta karasa yayi waje yayi wankan. Sajeeda Duk abinda yake yi Ina kallon sa rufe idona kawai nayi Kamar Mai baccin Yana fita na bud'e idona kila wani abun zai aikata tunda Yesmeen tace na ringa fitowa karfe biyu na dare Zan ganewa idona. Gabana faduwa kawai yake a lokacin da na mik'e tsaye Ina Jin kamar na Fadi saboda rashin kwarin jiki cikin sand'a na isa bakin k'ofar Ina lek'e ta ramin mukulin k'ofar. A Kan idona yazo ya fito daga d'akin sa tsirara
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111