Chapter 22
Chapter 22
binne abu sai da ya zo matakin karshe Yesmeen ta kashe shi. Hawaye suka Kara zubo masa daya tuna kalar wahalar da ya Sha har ciwo yaji a garin gudu dayaje makabarta binne abu, Sajeeda kuwa cak ta tsaya tana kallon shi a lokacin da taga Wai duk wanan abin saboda Karen da ya kawo ne,tsabar mamaki kasa ma matsowa tayi Saboda yadda taga ya fice a hayyacin sa har da kuka,ko da dan cikinsa ne ya rasu iya tashin hankalin da zai nuna kenan, saboda Karen dama yake kirarin kashe Yesmeen har da kukansa.? Kabiru hanyar waje yayi Yana ji Ina ma mafarki yake yi ya Kara yin bayan gida yana kallon Karen,ko kashe Yesmeen yayi yanzu baya Jin zai hucce,zai so ya azabtar da Yesmeen,zai so yaga Yesmeen ta Sha wahala kafin ma ya kasheta. Da Jan kafa ya juya yayi hanyar waje dan wajen Rabiu zaije ya fada Masa duk Abubuwan da suka faru. Sajeeda kuwa har ya fice mamaki bai saketa ba kanta yayi mugun daurewa da wanan al amari dama duk wanan tashin hankalin akan Karen da Kabiru ya kawo ne tana Jin motsin fitarsa. Ta buga k'ofar toilet din tana "ki bud'e Yesmeen ya fita" Yesmeen bud'e k'ofar tayi har lokacin jikinta rawa yake idonta yayi jajjur saboda kukan da ta Sha. Koda ta fito Sajeeda ido ta zuba mata dan bama tasan tunanin da za tayi ba a yanzu A hankali ta Kira sunan Yesmeen tana "Yesmeen da gaske ne ke Kika kashe Karen da Abban ku ya kawo"? Yesmeen bata iya magana ba dan batasan yadda zata yiwa Sajeeda bayani ba tunda idan har ta fada Mata ita ta kashe Karen sai ta tambayeta dalili. "Yesmeen Mai yasa Kika kashe Karen Wai Mai ke faruwane na kasa gane abinda ke faruwa Mai yasa Kika kashe karen"? "Umma yadda kike mafarki da karen nan haka nake mafarki da Karen ko bacci bana iya yi, haka Zan ta mafarki ya shigo Yana k'ok'awa dani idan kinzo cetona sai ya koma kanki hankalina ya kasa kwanciya da Karen a gidan nan shi yasa na saka masa maganin b'era" Yesmeen ta karashe tana mamakin yadda ta samu tayiwa Sajeeda karya dan bazata iya fitowa ta fadawa Sajeeda gaskiyar abinda ya faru ba dan da ace duk a hirar su ta tab'a zargin kabirun ne sai ta fada Mata,bata taba zargin sa ba tafi zargin abokinsa idan ta fito ta fada mata abinda ke faruwa ba lailai ta fahimceta ko ta yarda da ita ba" "Da kinsani baki kashe shi ba Yesmeen tunda na fada miki gobe yace zai maida Karen wajen Mai shi,ransa yayi mugun b'aci da abinda kika yi,ni tunda nake dashi ma ban tab'a ganin bacin ransa haka ba abin ya bani mamaki akan Kare hankalin sa ya tashi haka har da kukan sa wlh har yanzu mamaki nake na d'auka wani mugun abu Kika masa Allah dai ya kyauta Yesmeen abinda za'ayi ki hada kayan ki kala biyu kije wajen hajiya kareema kice nace kiyi kwana biyu zuwa lokacin nasan Abban ku ya hucce sai na Miki waya ki dawo" Yesmeen jiki na rawa ta hau hada kayanta dan ko Sajeeda bata ce ta tafi wani wajen ba bata isa ta kwana a gidan ba,tasan Kabiru bazai tab'a barin ta ba dole zai mata wani Abu,idan har zai iya cutar da Sajeeda matar sa uwar yayansa wacce ita da bazai cutar da ita ba. Tana gama hada kayan ta Sajeeda ta d'auko kudi ta bata akan tayi kudin mota dan hajiya kareema kawar tace a Kuma tsohon unguwar su take. Koda ta karba har tazo fita ta dawo baya tana kallon Sajeeda ji take Kamar ta rik'e hannun ta ta fada Mata duk abinda ke faruwa,sau uku tana gwada bud'e bakin ta dan ta fadawa Sajeeda abinda ke faruwa sai taji ta kasa,haka kawai hawaye ya hau zubo mata gani take idan ta tafi Kabiru zai cutar da ita amma ba yadda za tayi. Sajeeda dungure Mata Kai tayi tana "ke Kika jawowa kanki ai da kinyi hakuri da gobe zai fitar mana da Karen daga gidanan kije idan na samu na shawo Kan sa yau Zan kiraki ki dawo yau gidan wani iri zai yi idan bakya Nan" "Umma Dan Allah ki dage da Addu'a umma Ina yawan mafarki marasa dadi umma karki yi wasa da Addu'a Kamar yadda kike zargin abokin Abba nima na fara zargin sa dan Allah umma kiringa addua kina yi mana" Murmushi Sajeeda ta saki tana "Ina Addu'a yata in Sha Allah ba abinda ya Isa ya mana har sadaka zan fara yi dan sadaka maganin masifa ce in Sha Allah ba abinda zai iya yi mana idan tarayyar sa da Abban ku ba alheri bane Ina rokon Allah ya kawo karshen abotar su Allah ya Miki albarka" Ameen umma Yesmeen tace tana jin zuciyarta wani iri bazata yafewa kanta ba idan har wani Abu ya samu Sajeeda Anya bazata tsaya ta fada Mata gaskiya ba Mai yasa Sajeeda ta kasa d'aukar haske a duk abinda ya faru,daga tashin hankalin da Kabiru ya nuna na mutuwar Karen ya Kamata ace Sajeeda ta gane wani Abu amma ta kasa ganewa. Har bakin gate Sajeeda ta rakata sai tayi kamar zata mata magana sai ta kasa har Sajeeda ta maida k'ofar gate din ta rufe. Banda bata san ta dagawa Sajeeda hankali ba abinda zai dawo da ita gidan kabiru ba abinda ya faranta Mata sama da karen da ta kashe dan tasan ta wargaza komai a yanzu Kuma addua zata dage ba dare ba rana. Kafin ta samu abun Hawa ta tsaya a hanya ta siyi alewa duk yaron da tagani sai ta bashi. Sajeeda Har karfe goma na dare Abban Nusrah bai dawo ba zuwa yanzu sai naji hankalina ya tashi na kasa gane Mai yake damun Abban Nusrah hakika uban yayana ya canza akwai wani boyayyen al amari,tunda Yesmeen ta tafi na fara mazartar maganganun ta sai naga kamar akwai abinda take b'oyemin haka kawai bazata ce na ringa addua ba,yadda Abban Nusrah ya nuna tashin hankalin sa akan Kare har yanzu kaina a daure yake. Haka tunani ya cike min zuciya na rasa tunanin ma da ya kamata nayi. Abban Nusrah bai dawo gidan ba sai wajen Sha biyu na dare na dauka zai dawo fuskarsa a hade sai naga fuskarsa a sake ya dawo. Bai nuna wani abu ba Kamar ma wani Abu bai faru ba har na bashi abincin sa ya fara ci Yana fada min dalilin daya sa bai dawo da wuri ba Kaya ya Kai wani kauye, Ni kuwa ganin sam bai nuna wani abu ba yasa na fara magana cikin kwantar da murya Ina "Abban Nusrah dan Allah kayi hakuri da abinda Yesmeen ta maka na hadaka da girman Allah" "Haba haba ba komai fa ni har na manta ma dan dama abokin nawa nake ji Koda naje wajen sa na fada Masa abinda ya faru bai wani nuna bacin ransa ba shi ya sa na sauko dama shi nake ji ya bani aron Kare na kashe masa,Amma a yanzu na sake gano wani goben nan Zan d'auko bai Kai Wanda ya mutu girma ba muna bukatar Kare a gidanan"
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111