Chapter 79
Chapter 79
shafa kowane shafi,sai naji kamar Ina gani" Gyada Kai Yaya Abu tayi tana ba shakka toh ga abincin ki nan sai kici" "Nagode mama" Yaya Abu wani irin kallo ta zuba mata kafin tayi hanyar waje,ta bar k'ofar d'akin Yesmeen din a bud'e tana ayyana irin dukan da za tayiwa Yesmeen idan ta gano tana gani kitchen ta koma ta d'auko ragowar maganin da ta zubawa Sajeeda ta fito ta koma d'akin Yesmeen cikin sand'a ta zubawa Yesmeen ido da idonta ke kallon sama har lokacin tana zaune a yadda ta barta abincin ta na nan a gabanta,sai shafa littafin addu'oi take tana miis mis da baki. A hankali ta tsugunna a gaban Yesmeen ta barbada maganin a cikin abincin,tana cigaba da kallon Yesmeen idan har Yesmeen tak'i cin abincin nan tasan tana gani idan kuwa taci tasan dagaske bata gani,dan ko kad'an bata yi motsin da Yesmeen zata san ta shigo ba ta koma gefe daya tana kallon yesmeen da har lokacin take ta shafa littafin,Yaya Abu kuwa tuni ta fara tunanin karya Yesmeen take tana gani,tayi gyaran murya tana "Kici abincin ki Mana sai ya hucce" Yesmeen duk abinda Yaya Abu take yi tana kallonta da ace Yaya Abu zata Mata kallon tsaf zata ga yadda jikinta ke balain rawa har tana hada gumi,da dukan alamu Yaya Abu so take ta kasheta itama dan tana kallon sama ne kawai amma tana kallon sadda ta zuba mata abu a cikin abinci,da kulle k'ofar d'akinta take Yi,Yaya Abu ya kafa Mata dokan ta daina kullewa dan ta tsani tazo ta ringa kwankwasawa, ta riga tasan Yaya Abu so take ta gano ko tana gani ko bata gani,a yanzu indai tak'i cin abincin nan zata gano tana gani,karshen ta idan Kabiru ya dawo aka fada Masa tana gani,a yau ya aikata lahira ba Mai iya kwaceta dan itama Yaya Abu ba karamin tsanarta tayi ba,da hankalin ta ba yadda zata ci abinda zai cutar da ita,a yau dai asirinta zai tonu dan bazata ci abincin ba, zata nunawa Yaya Abu tana gani,maganar Yaya Abu ya katse mata tunanin da take da tace taci abincin Mana Kar ya sallamce,duk Shirin da take yi na su gudu da Sajeeda idan har Yaya Abu ta tafi wajen Yesmeen gobe ya tashi a banza tsawan da ta daka Mata da "Kici abincn nan nace kuut a lailai yarinya nan ta dauka dunkulallen kai ne dani, har na shigo d'akin nan naganki da littafi kice min bakya gani,ci abincin nan nace" Yesmeen so take ta saukar da kanta ta kalli Yaya Abu tace tana gani,ta fada Mata dalilin da yasa tayi karyar makanta,indai da zuciya a kirjinta ai dole ta tausayawa Sajeeda da ita kanta,sai dai a madadin ta saukar da kanta sai ta hau lalubar abincin ta d'auko cokalin ta debo abincin duk bisa umarnin zuciyarta dan Yaya Abu na gabanta a tsaye ta kame kugu da alama kiris take jira ta rufeta da duka,tana bude bakinta Yaya Abu ta tunkude hannunta ta d'auke abincin dan tasan indai tana gani tasan bazata tab'a yarda taci ba,tana ficewa Yesmeen ta kifa tayi sujada tana godewa Allah Dan Allah ne ya rufa Mata asiri ya kareta,yanzu ba iya Kabiru ne abin tsoro ba har Yaya Abun bata tab'a tunanin zata tunkuda hannun ta ba ta dauka zata barta taci abincin ba abinda zai zaunar da ita a gidanan da Sajeeda Yaya Abu na tafiya gobe taga Kabiru ma ya fita zata Nemo Mai taimaka Mata su gudu,ta koma ta zauna tana Jin yadda kirjinta ke bugun uku uku,yau dai ta tsallake rijiya da baya. Tana dagowa daga sujada ta koma ta zauna a daidai lokacin da Yaya Abu ta sake dawowa da wani plate din ta dire a gabanta tana "Ga wani abincin kici wancan da na d'auke abu ne ya fada a ciki. Daga haka ta kullo rufo dakin Yesmeen ta koma kitchen ta d'auko abincin Sajeeda,a yanzu ta tabbatar wa kanta da yesmen bata gani,ba yadda zaayi ta kashe Yesmeen,dan bata ga amfanin kau da ita ba za Kuma a gano idan suka tafi lokaci guda da Sajeeda dama gwaji take so tayi ta Kuma ga Yesmeen din ba gani take ba. Sajeeda Hawaye kawai ke zubo min da naga Hamza Wai shi ya kaini bandaki ya gyarani,ya canza zanin gadon da na b'ata ko kyankyamina banga yayi ba ballantana ya toshe hancinsa. A fadar sa ma a d'akina zai kwana dan sunyi hutun makaranta,ina Jin lokacin da Yaya Abu ta kwalla masa Kira ya fita ba jimawa ya dawo da farantin abinci a hannun sa dama tare suke ci da Annur,shinkafa da taliya ne da miya,ya hau tsakiyar gadon ya juya abincin ya kalli Annur Yana yazo suci,haka Hamza ya ringa ci Yana bani a baki, Kamar yasan wani zubin da yunwa nake kwana dan Yaya Abu yanzu ba bani abincin take ba, Yesmeen Kuma ba ta iya zuwa ta bani dan Yaya Abu sai ta Kai Sha biyu a zaune a Palo tana kallo,a haka yayi ta bani har sai da na d'auke kaina ya bani ruwa na sha,yaje gaban mudubi ya kwaso magunguna na da ni nasan ba aikin da suke min amma ba bakin da zan hana a ringa bani,haka na Sha ya maida ledar gaban mudubi ya dawo ya zauna,Annur kuwa suna Gama cin abinci ya ringa buga game a tab din da Abban Nusrah ya siya musu,shi kadai ne banga Abban Nusrah ya siyawa waya ba,wayar Yesmeen ma da ya kwace Ina ganin dan Yasan tasan sirrinsa ne Amma sai cewa yayi wayar bata da amfani a wajenta tunda ba gani take ba,Hamza Kuma ya d'auko wayarsa ya ringa daddanawa,duk da ido nake bin su iya su da nake gani wallahi Dadi nake ji a raina,haka nake kwana ni daya Kamar mayya ba Mai kula dani,dama su barmin su su ringa kwana a d'akina nasan ko Yaya nayi gurnani Hamza zai tashi kila ya gane Ina bukatar wani abun ne,Yesmeen ma Yaya Abu ce ta koreta a ranar da ta shigo d'akin da dafa bango akan zata na kwana dani, Yaya Abu ta koreta akan me zata kwana ita da ba gani take ba ba Kuma wani abu za ta iya min ba. Shigowar Yaya Abu ya katse min tunanin da nake na juya Ina kallonta,tana ganin su Annur ta hade rai tana "Uban me kuke nema a d'akin nan"? "Ba komai dama munzo mu zauna da umma ne saboda ita kadai ce yau ma anan zamu kwana dan umma na bukatar kulawa tunda ba mai kulawa da ita daddare" "Toh wanan ne baku Isa ba,bazaku kwana anan din ba,kaji min yaro da iyayi waye yace maka baa kulawa da ita maza maza tashi ku tafi dakinku zan bata abinci" "Ai taci abincin tare muka ci abincin da ita dan Allah mama ki barmu mu kwana Yaya Saifullahi ma dazu da muka yi waya dashi cewa yayi mu ringa kwana da ita" "Toh bazaka kwana ba nace so kake kace bana iya kula da ita har wani waya ake bugo ma ace ka kula da ita dalla tashi ku ficemin daga d'aki" Annur da sauri ya dauki tab dinsa yayi waje,Hamza kuwa baa San ransa ba ya mik'e Yana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111