Chapter 103
Chapter 103
suka fita Suka barta,ihuu kawai take tana "Baba kana Ina Gwaggo ku yafe min tun baaje koina ba na fara ganin ba daidai ba,Kabiru na tuba ka bar kudin dan girman Allah ka maidani titi,wallahi ba Wanda Zan fadawa karka min haka Kabiru? Shigowar shugaba da bakakken Kaya da wani Kare daya dallaro harshensa waje yasa ta saki ihu taje ta manne da bango, Kabiru kuwa dake bakin kofa ya fara magana Yana "Mai gida burina sirrina ya rufu a rufewa kowa baki" Shugaba murmushi ya saki Yana "zaka iya tafiya ka dau hanya goben nan karka wuce gobe karfe daya zamu yi amfani da jinin ko ka isa can ba mai iya maka magana " Ihu Yaya Abu ta saka tana "ku rufa min asiri da jinina zaku yi amfani innalillahi wa Inna ilaihi rajiun kuyi min rai karku kasheni, Kabiru nice fa Abu yayar Sajeeda Mai na maka da kazo ka bada jinina mai yasa baka bada na Sajeeda ba" Kabiru ko kallonta baiyi ba yayi waje shugaba ya fita ya rufe k'ofar Ta tafi da gudu tana bubuga k'ofar kuka kawai take kamar ranta zai fita "kaicona na cuci kaina a garin san kudi,na jawowa kaina mutuwa wane kaddarar ne ya kaini gidan Kabiru shikenan yanzu mutuwa zanyi" Kuka kawai take tana hararo yadda zasu yankata. Kabiru Ko kad'an baiji komai ba har ya baro kungiyar dan yasan ba mai tab'a zargin Wai shi ya d'auke Abu,haka kawai yaji yayi mugun tsanarta,ko shi aka bawa wukar zai iya kasheta,babban burinsa a yanzu ya samu Yesmeen ko da a gaban mutane ne wallahi sai ya rabata da ranta,a rayuwarsa bashida babbar makiya sama da Yesmeen duk wanan masifar ita ta jawo.masa. Koda ya koma gida haka ya zauna yayi zuru Yana tunanin Rabiuu har ga Allah so yake ya bar kungiyar ya gaji yayi nadama,har tsawon wane lokaci zai dauka Yana aikata abubuwa dan asirinsa ya rufu da Yama riga da ya tonu,yanzu gobe idan mahaifiyarsa ta Kama shi fa Mai zai ce Mata. Idan yaje gobe Yan uwa Sajeeda suka gan shi fa Yadda yaga rana haka.yaga dare bai runtsa ba. Karfe bakwai na safe ya dau hanyar garinsu da Kare a Bayan mota baisan ma mai zai cewa mahaifiyar sa akan Karen ba. Zuciyarsa cike take da zullumi. Tafiyar awani ya karaso dashi har k'ofar gidan mahaifiyar sa da ta koma sabon gidan da ya Gina mata. Da Karen ya shiga cikin gidan Gabansa na dukan uku uku,a tsakar gidan ya samu mahaifiyar sa a tsaye wasu almajirai a tsugunne a gabanta,tana ganinsa ta saki baki tana kallonsa da Karen da yake ja da daya hannunsa tama kasa amsa sallamar da yayi Mata. "Wanan Karen fa Kabiru daga Ina haka ka taho da kare" Mahaifiyar sa tace a daidai lokacin da ya Isa gabanta ya tsugunna Yana gaisheta Bata amsa ba ta Kara jefa Masa tambayar "Wanan karen fa Kabiru kasan ko kad'an bana San Kare Mai ya hadaka da kare Kai ba mafarauci ba" "Hajiya akan hanyar tahowa nan na siya wallahi barayi ne suka addabeni shi yasa idan na kaita gida barayi zasuji tsoron shigowa. "Tun kana Abujan baka tsaya ka siyi Karen ka Kai gida ba sai da ka d'auko hanya zaka siya" Kabiru Kai ya hau sosawa ya dauki Karen yayi bayan gidan Yana "yunwa nake ji hajiya akwai abinci. Yana zuwa ya daure Karen ta wuyansa Ya koma ciki,Yana shiga yaga mahaifiyar sa ta kwanta kamar Mara lafiya Cikin mamaki yace "Hajiya lafiya kuwa na ganki haka"? "Wallahi Yanzu nan naji kaina ya sara min zazzabi ya rufeni ji nake wuyana a shashake ma" "Sannu hajiya Allah ya sauwake ya baki lafiya kina da pcm na dauko miki ki Sha"? Eee akwai a gaban mudubi d'auko min,sai ka Shiga kitchen akwai abinci a flask. Kabiru dakinta ya Shiga ya d'auko Mata pcm din da ruwa ya kawota dak'yar ta karba ta Sha tana rik'e wuyanta. Kabiru ya shiga kitchen ya debo abinci ya dawo palon ya zauna ya fara cin abincin ganin tana ta wash wash yasa yace "Hajiya ko dai asibiti Zan Kai ki"? Girgiza Masa Kai tayi idonta a rufe,a haka ya zuba mata ido Yana jera mata sannu. Ba jimawa yaga bacci yayi awon gaba da ita. Sai yaji inama a yanzu zai iya zagayawa baya ya nemi karyar tunda bacci ya d'auke ta,amma ba wanan damar saboda sai karfe daya na dare aka ce ya kwanta da Karen,kila yanzu ma ya gama da jinin Yaya Abu ya tabe baki Yana kwadayin ta ne ya jawo Mata. Bacci bacci yaji ya fara ji shi ma hakane yasa ya tashi ya Shiga daya d'akin da ya zama d'akin Baki. Yana kwanciya bacci yayi awon gaba da dashi. Mafarki A kwancen da yake yaji an turo k'ofar hakane yasa ya bude idonsa a hankali yaga mahaifiyar sa ta shigo da igiya a daure a wuyanta cikin b'acin rai ta fara magana tana "Kabiru mai nayi maka kake so ka kasheni saboda me zaka daureni, Kabiru ka kunceni Kabiru ka kunceni Kabiru ka kunceni" A firgice ya tashi ya hau kalle kalle sai da ya dau tsawon mintuna ya gane mafarki yake,mik'ewa yayi da sauri yayi waje dan sai yake ganin kamar ba mafarki yake ba a gaske ne mahaifiyar sa ta shigo. A kwance take har lokacin akan dogon kujera,ido ya zuba mata yana tuno mafarkin da yayi da ita Mai ke Shirin faruwa ne Mai yasa zaiyi mafarki da mahaifiyar sa tana a kunceta A hankali ya fita waje,ya zagaya bayan gida Inda ya daure Karen Yana zuwa yaga Karen a kwance Kamar yadda mahaifiyar sa ke kwance,gabansa yanke wa yayi ya Fadi ya hau tuna Sajeeda da yadda yayi amfani da Kare a madadinta. Cikin faduwar gaba ya karasa wajen Karen Yana zuwa ya tsugunna a gaban Karen ya kunce daurin wuyansa. Ya mik'e ya koma ciki ga mamakinsa Yana komawa ciki yaga mahaifiyar sa ta mike tana tattaba wuyanta tana ganin shi ta fara magana tana "Kasan ji nayi Kamar an shake min wuya mai ke Shirin faruwa dani ne"? Kabiru da jikinsa ya dauki rawa kasa ce Mata komai yayi mahaifiyar sa kuwa ta mik'e tana kila iska ne bata ga ta zama ba bari ta d'auko Qur'anin ta daga haka tayi d'akinta. Kabiru yayi waje da balain sauri hankalinsa a balain tashe sai a yanzu ya gano shugaba so yayi ya cuce shi ya yaudare shi ya nemi mahaifiyar sa, taya zai cutar da mahaifiyarsa?taya zai nemi mahaifiyar sa jikinsa rawa kawai yake ya d'auko wayarsa a daidai lokacin da Kiran shugaban ya shigo wayarsa. Rai a balain bace ya daga wayar Yana k'ok'arin magana shugaban yace "Matar da ka kawo jiya ta gudu,bansan ya akayi ta tsere ba dan haka ka kawo mana wani Jinin" "Bazan kawo ba ka kasheni kawai dan Nagaji da wanan masifa ba abinda kasani,tunda har ka bari Abu ta tsere nasan asirina ya gama tonuwa,har ni zaka yaudara kace na kwanta Da mahaifiyata a siffar Kare,Allah ya tona maka asiri wallahi wallahi bazan kwanta da Karen ba na gaji ba abinda zaka iya yi na bar kungiyar na daina yi kayi duk abinda zaka yi" "Nan da awa ashrin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111