Chapter 1
Chapter 1
*RUFAFFEN SIRRI* *NA SADNAF* *ADABI WRITERS ASSOCIATION* *BISMILLAHI RAHAMANIR RAHEEM* *PAGE 1* "Ba abinda na tsana sama da abinda zai Shiga tsakanina da baccina,kamar na kurma ihun bakin ciki haka nake ji a lokacin da naji Abban Nusrah na ta shafani wanda nasan mai hakan ke nufi,tun kafin nayi bacci bai neme ni ba sai yanzu,ban motsa ba dan har ga Allah bazai samu abinda ya keso har ya gamsu ba,sai dai shi kadai yayi kidan sa yayi rawar sa duk da ba abinda ya shafe shi ko baccin nake idan yayi ra'ayi ko ban bashi hadin kai ba zai juyo dani ne ya samu biyan bukatarsa. Ina Jin lokacin da ya rabani da zanin dana dora a saman t shirt din dake jikina,a madadin ya juyo dani sai naji ya rungumeni ta baya,ya fara k'ok'arin neman hanya da jikinsa dan tsawon zamana dashi ban wani san dan aike ba balle har wai a motsa min sha'awa,shi dai burin sa kawai ya shafani sama sama ya samawa kansa nutsuwa,inda naji Yana k'ok'arin yi yasa nayi saurin janye jikina,sai a lokacin na motsa na juyo Ina kallon sa cikin mamaki,shi kuwa idonsa a kankance ya kara jawoni,sai na juyo a rigingine dan ya samu abinda yake so dan Ina tunanin dan ta gefe yasa yayi hanyar da ba haka ba,sai dai a madadin ya hau kaina sai naga ya Kara juyar dani ya kankameni da hannu daya ya sa hannu daya ya Kara danna jikinsa wajen da yasa na Kara janye jikina da bala'in sauri na Mik'e zaune cikin mamaki Ina kallonsa. K'ok'arin jawoni yake na janye jikina Ina "Lafiya kuwa Abban Nusrah mai haka"? "Wane irin tambaya ne wanan Sajeeda bangane mai haka ba ki matso na samu nutsuwa ki koma baccin ki" "To ai kai din ne bangane ba Kai ma kasan ba wajen nutsuwar ka nufa ba bayana naji kana k'ok'arin shiga" Tsaki yayi ya Kara jawoni da k'arfi Yana "Ta bayan yafi dadi bari kigani" Da karfi naga Yana Neman tura jikinsa bayana Da k'ok'awa na fusge jikina cikin tashin hankali da mamaki na sauka daga gadon na nufi wajen haske na kunna na zuba masa ido kamar yanda shi ma ya zubo min ido, tamkar an like min baki haka naji dan tsabar mamaki na ma kasa magana,shekarar mu Ashirin da biyu da Aure bana Jin da gani har shi bakine a wanan fagen balle ince sani ne bai yi ba shi yasa yake k'ok'arin nema na ta baya har Yana cevmin yafi Dadi. "Abban Nusrah anya a hayyacin ka kake kuwa"? Mik'ewa yayi ya nufo wajen da nake tsaye yayi kasa da muryarsa yana "Sajeeda a hayyacina nake nasan zaki ji wani iri amma ki taimaka ki ba ni hadin kai ina so na gwada ta bayan nan ance yafi dadi" "Allah ya kiyaye Kabiru Allah ya kiyaye ni zaka nema ta baya ta Inda ake kashi,kabiru Anya Kaine kuwa?waye yace ma ka nemi matar ka ta baya, idan Wanda ya baka shawara bashi da ilimi kai ina ka Kai naka ilimin bayan kasan haramun ne, bazan iya ba Kai ma da ka yi tunanin kayi gwajin ka fara istigifari" Kasa ya Kara yi da murya cikin rarrashi ya matsoni Yana "Sajeeda yanzu baza ki iya taimaka min ba ki bari nayi sau d'aya sai muyi istigifari an dade ana kwadai ta min ta bayan nan haba matata" Ya fara k'ok'arin rungumoni na ture shi da iya karfina dan zuwa yanzu ma sai naji tsoron uban yayana ya kamani,gani nake kamar bashi ba "Kabiru Ina ga ba'a hayyacin ka kake ba a tsawon lokacin da nake tare da Kai nasan baka shaye shaye ballantana nace ba'a hayyacin ka kake ba,a iya sani na ka na da ilimin ka daidai gwargwado ka san abinda ya ke daidai da wanda yake haramun, bazan tab'a maka biyayya na Sabawa Mahallicina ba Ina mai rokon ka idan a hayyacinka ka ke wani ne ya baka shawara ka zo ka neme ni ta baya,ka gaggauta rabuwa da koma waye dan so ya ke ya Kai ka halaka" Daga haka na nufi Kan gado na na dauki zanina na daura nayi hanyar fita daga d'akin ya hau kwalla min kira Yana "Sajeeda Sajeeda karki sake ki bar d'akin Nan Ko juyawa ban yi ba har na bar d'akin har lokacin ban daina mamakin sa ba. Koda na fito dan karamin palon namu fitila na kunna idona ya sauka akan agogo naga karfe uku na dare na zauna akan kujera tare da dafe kaina jikina har rawa yake bansan tunanin ma da ya Kamata nayi ba. Na kasa yarda da abinda ya faru yanzu a daki,na kasa yarda mijina uban yayana da shekarar mu Ashirin da biyu da aure da arzikin Yara biyar har mun aurar da Yar mu ta fari Nusrah shi ne yau dare daya zai nemeni ta baya wai ya dade yana san yayi gwaji an ce Masa yafi dadi har waye zai ce wa Kabiru ya gwada abinda Allah ya haramta. Sosai na zurfafa a tunani bansan tsawon lokacin da na d'auka Ina saka da warwara ba,sai Kiran sallah ne ya katse min tunanin da na tafi. Mik'ewa nayi na koma d'akin. A kwance na ganshi Yana dan girgiza kafarsa da alama ba Bacci yake ba idonsa biyu. Bandaki na shige na daura alwala na fito har lokacin Yana kwance bai motsa ba,nasan fushi yayi,da ace wani abin na Masa da har zai yi fushi dani da sai na bashi hakuri,amma ni nasan ba laifin da na masa bazan tab'a masa biyayya a sabon Allah ba ba muyi haka tun kuruciya ba sai yanzu da muka Manyan ta,tsawon zamana dashi ban tab'a hana shi hakkin sa ba Koda kuwa fada mu ke amma dai yau na bijire masa dan bazan iya Sabawa Allah ba, tsigar jikina har tashi yake idan Ina hararo yanda wai zai sadu dani ta baya. Sallah nake amma na kasa yin sa a nutse sabida tunanin da ya dankare min zuciya. Har na sallame Yana kwance zuwa yanzu sai naji kamar canzo kabiru aka yi bashi bane dan iya sani na baya Wasa da Sallah fushi dani bazai saka wai yak'i fita massallaci sallah ba. Kasa hakuri nayi da carbina a hannu na Mik'e na zagaya ta wajen da ya kwanta Ina "Abban Nusrah "Abban Nusrah yau ba zaka yi sallah bane"? "Dama can ke kike saka ni nayi Sallah"? "Bani nake saka ka kayi sallah ba amma dai bai dace idon ka biyu kana Jin ana sallah ka k'i tashi kayi akan lokaci ba" Tsaki yayi ya juya min baya. Zuwa yanzu bazan iya fadan kalar mamakin da nake na sauyawar halin mijina dare daya ba,ga nemana ta baya ga k'in sallah. Bai tashi ba sai da gari yayi haske ya shige bandaki ya dauro alwala yazo ya tada sallah Yana sallamewa ya fice daga d'akin. A ranar sukuku na wuni na rasa mai ke damuna dan tunda Abban Nusrah ya fice daga gidan bai Kara dawowa ba. Har karfe hud'u na yamma Ina zaune zuciyata fal da tunanin muryar Yasmeen ya katse min tunanin da na tafi "Umma ko dai magani zan d'auko miki ki sha"? Girgiza kaina nayi na aro murmushi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111