Chapter 26
Chapter 26
KI MALLAKI NAKI KI BIYA TA WANNAN ACCOUNT DIN KITURA MAN SHAIDAR BIYA 3968303018 ZAINAB SHU AIBU FCMB 08162859027 *WANAN NOVEL DIN NA KUDI NE NA HADA KU DA FIYAYYEN HALLITA ANNABI MUHAMMAD SALLAHU ALAIHI WA SALAM KARKU MIN SHARING NOVEL IDAN BANA KALLON KI ALLAH YANA KALLON KI KUDIN KARATU KIKA BIYA BANA MALLAKA BA IDAN KIKA FITAR NA BAR KI DA ALLAH* *Page 12* Yesmeen kirjinta ne ya doka da k'arfi da taji yace ta kunna fitilar d'akin,take mafarkin da tayi yanzu nan ya hau dawo Mata,tasan akwai muguntar da Kabiru ya hada mata ta dade da sanin Kabiru naso ya cutar da ita ba yadda zata yi da hankalin ta ta kunna fitilar d'akin ta "Baki ji mai nace miki bane kizo ki kunna fitilar nan nace karki Kara kashe wutar d'akin nan" Hannun ta rawa kawai yake ta rarumo wayarta tana "Abba na kunna fitilar dazu ai Kamar bulb din ne ya lalace shiyasa nake amfani da touch din wayata" Kabiru na k'ok'arin magana Hamza kanin su Saifullahi ya fado d'akin Yana "Abba umma tana Kiran ka" Kabiru wani irin kallo ya watsawa Yesmeen Ya kasa gane Kan Yesmeen daga yadda take rawar jiki da alama ta gane akwai abinda ya saka a fitilar d'akin ta ya Rasa wacce irin yarinya ce ita ya juyo zai fito daga dakin kenan Hamza ya Kai hannun sa wajen fitilar Yana "Aunty Yesmeen d'akin ki duhu" A lokaci guda Kabiru da Yesmeen Suka isa wajensa,Yesmeen ta tunkuda hannunsa Kabiru cikin ihun tashin hankali yace 'karka kunna fitilar nan Hamza" Saura kiris ya ya sume saboda tashin hankali a gaban idon sa Hamza ke neman makancewa bayan Annur ya kurmance,cikin borin kunya ya dakawa Hamza tsawa Yana ya fita,Hamza ya fice daga dakin da gudu ,Kabiru bai yi wata wata ba yayi Kan Yesmeen ya rufe ta da mugun duka Yana "kin zame min masifa Yesmeen dole ki bar gidan nan kafin ki jawo min wani tashin hankali" Dak'yar Yesmeen ta kwace daga bugun da yake mata tayi bandakin ta ta rufo k'ofar tana ihun kuka Daga abinda ya faru ta Kara tabbatar da zargin da take yiwa Kabiru nasan cutar da ita tunda har ya gigice daya ga Hamza na neman kunna fitilar d'akin, anya zata zauna a gidanan Kabiru ya samu nassara a kanta, zaman ta ma a gidan bai zo yayi amfani ba tunda bai fasa cutar da Sajeeda da take k'ok'arin taga ta taimakawa ba,dole tasan nayi kafin Kabiru ya kai ga shigowa d'akin ta ya caka mata wuka haka taci kukan ta a bandaki ta daura alwala ta fito. Kabiru kuwa yana fitowa daga d'akin Yesmeen yayi hanyar waje har lokacin kirjinsa bai bar bugawa ba da abinda ya so ya faru anya bazai ma cire abinda ya saka a fitilar d'akin Yesmeen ba Yana tsoro a cikin yayansa wani yaje ya kunna fitilar d'akin ya makance. Jiki na rawa ya d'auko wayarsa daga Aljihu ya Nemo lambar Rabiu Yana d'auka ya fara magana Yana "Rabiu na gaji da yarinya nan Rabiu yarinya nan ta zame min masifa ta riga da tasan sirrina kullum bibiye take dani,kasan jiya ma daddare Ina san nayi aikin da aka saka ni na karshe sai gashi tana buga k'ofa,ni nasan duk yadda akayi yarinya nan ta gani jiya, karfi da yaji tana neman hanani rawar gaban hantsi ,indai zan ganta da Sajeeda a waje daya sai nayi ta tsarguwa Ina Jin kamar zata fada Mata bansan Mai yasa shugaba yace ba yanzu ake bukatar jininta ba, wallahi ba ni da burin da ya wuce na kau da ita,kasan yanzu saura kiris dana ya Kunna fitilar d'akinta,duk wani abu da akace na mata sai ta tsallake,yarinya nan bana Jin ita kadai ce tasan akwai abinda na saka a fitilar d'akin ta dan k'in kunnawa tayi da yarona yaje kunna fitilar har da tunkude shi alamar tasan akwai wani abu Ina tsoron yarinya nan ta tona sirrina dole mu dau mataki" "Toh yanzu ya kake so ayi"? "So nake a b'atar da ita kawai tunda shugaba yace baza'a kasheta ba,kasheta zai zame min tashin hankali a b'atar da ita kawai na samu kwanciyar hankali. Na samu kudin nan a yanzu ya Kamata na more wa rayuwata amma yarinya nan a gidanan bazan samu kwanciyar hankali da zan ci kudina cikin nutsuwa ba,tunda tasan sirrina ni ba kace akwai wayanda ke siyan mutane ba"? Dariya Rabiu ya saka Yana "Siyar da ita zaka yi" "Eee siyar da ita zanyi ko na basu ma kyauta bana kaunar ganin yarinya nan,a rayuwa ba wacce na tsana sama da ita, indai tana gidanan asirina zai yi saurin tonuwa,a halin da Sajeeda take ciki yanzu bana san na bata k'ofar da zata zargeni,shi yasa ban fito da kiyayyar yarinya nan fili ba,amma indai da yadda za'a batar min da ita dan Allah ka taimaka min na mori arzikin nan cikin kwanciyar hankali. "Toh shikenan ka bari gobe idan mun hadu a kungiya duk sai ka fadawa shugaba abinda kake so ayi maka ba lailai sai da jinin Yesmeen zaka yi amfani nan gaba ba zaka iya nemo wani gwara a b'atar da ita tunda ta zame maka barazana" "Dan Allah a taimaka min" "Karka damu Abokina zaa san abinda za'ayi" Kabiru sai a lokacin ya samu kwanciyar hankali suka dan tab'a hira suka yi sallama Murmushi Kabiru kawai yake yana hararo yadda zai more rayuwarsa idan ya kau da Yesmeen. Koda ya koma ciki d'akin yaran ya fara zuwa ya zuba musu warning akan Kar Wanda ya Kara Shiga d'akin yesmen duk Wanda ya Kara Shiga sai ya ci mutuncinsa dan yana tsoron wani a cikin su yayi gangancin da Hamza yaso yi yau dole ma gobe ya cire abin tunda Yesmeen ta san da abu a fiitlar. Sajeeda Har muka je asibitin muka dawo da lodin magungunan da aka bamu ban ji wani sauki a jikina ba,a yanzu ma kasana nake Jin Yana d'aukar dumi shi kadai tsawon rayuwata ban taba Jin haka ba bansan Mai ya jawo min haka ba,Ina ta so na tuna abinda ya jawo min wanan dumi da leman da nake fama dashi na kasa tunawa,na San dai ba daidai nake ba kafin Abban Nusrah ya samu nutsuwa dani,da Kuma ya samu nutsuwa dani naji jikina ya Kara canjawa bansani ba ko rashin lafiya ne ya jawo min haka. Duk yadda naso na daure na dauki jikina kasawa nayi,haka na kwanta a daki, har Abban Nusrah ya shigo ya zauna a gefena ya ruko hannuna Yana tambaya ta jikina Hawaye na zubo min na fada masa yadda nake Jin jikina duk da magangunan dana sha. Cikin tausayawa ya hau min sannu ya kara b'allo min maganguna na sha ya zauna a gefena ya hau shafani Kamar wata yarinya,a ranar har daki ya d'auko abincina ya kawo min naci,inaso na fita na duba yarana amma bana san tashi dan sallah ma dak'yar nakeyi saboda Ina tsayawa Zan ji jiri na dibana. Koda na tambaye shi Yesmeen tunda na dawo banga ta leko ba sai cemin yayi maganin mura ta sha ta Dade da bacci. Shi ya ringa ja na da hira Yana ta bani labaran yadda yake samun kudi, Wai ana masa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111