Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 108

Chapter 108

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,252 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ma ta haifi yarinya,haka ta figeta ba ko tausayi,ta ajiyeta a bandakin ta debo ruwa ta hau watsa mata daga nesa tana toshe hanci,tuni taji wani irin radadi da azabar kaikaiyi ta fara girgiza Kai tana tuno yadda itama ta tab'a figar Sajeeda tayi mata yadda yar budurwar yarinya nan ta Mata,lailai ta yarda sharri dan aikene,Sajeeda bata da hakkinta gashi tun a gidan duniya an samu mai rama Mata,ta hau gurnani tana "Sajeeda ki yafemin na samu sauki a rayuwata nayi nadamar Abubuwan da na Miki,baba ka yafemin Gwaggo kimin addua kaicona" Kuka kawai take Yar budurwa na daka mata tsawa tana cudata da tsintsiya daga nesa,dan bazata iya ma matsowa kusa da ita ba. Koda ta gama wani wajen ta maida ta,ta dauko wani.kaya ta zura mata, duk rai a hade take.masifar babanta ya jawo musu balai ya rasa wa zai kawo gida sai Mai larura,abincin ma a wulakance ta bata tana tura mata cokalin bakinta Kamar zatayi amai,tana gama bata ta bar d'akin a fusace tana bazata yarda ta kwana ba indai kuwa babanta bai maidata ba a yau wallahi guba zata saka mata taci ta mutu. Wani irin tsoron Allah ne ya shigeta,da taji abinda yarinyar tace,duk wani mugunta da tayiwa Sajeeda yau gashi Yar cikinta na Mata har tana kirarin zata kasheta,Ashe duk abinda take Allah Yana kallonta lokaci ya bata ta gama duk abinda za tayi,Allah kadai yasan irin kararta da Sajeeda ta kaiwa Allah da har ta fara ganin irin wanan sakayya. Kuka kawai take dan har ta sake Bata kayanta wari ya dume d'akin. Har ga Allah da ace tasan idan ta mutu Aljanna zata tafi da ta roki Allah akan ya dauki ranta da wanan rayuwar kwanci tayar din,ashe baka yiwa bawa gori da halin da ya Shiga ciki,idan har kayiwa bawa gori da jarrabtar da Allah ya Masa,zaka iya wayar gari kaima a jarrabce ka kamar yadda itama kwadayinta ya kaita ga Shiga halin Sajeedan,kafin ta mutu tana bukatar Neman yafiyar Sajeeda da Iyayenta,kafin ta mutu tana bukatar ta nemi yafiyar Yesmeen, Yesmeen da bata Mata komai ba ta Dora Mata Karan tsana. Tana daki ta ringa jiyo muryar dattijuwar na yiwa wani Wanda take kyautata zaton shi ne maigidan akan ayau take so a fitar da ita daga gidan tunda ta farka, yadda taji muryarsa na rawa yasa ta tuna nata mijin da take juyawa da tana tunanin har da bakin cikinta ya Kashe shi. Ido ta zubawa k'ofar a lokacin da ta ji sun nufo d'akin mutumin na zuwa ya rike hannunta matarsa ta Taya shi Suka yi waje da ita. Suna zuwa k'ofar gidan matar ta saketa tana "Yayi maza ya kaita bakin titi" Ta rufo k'ofar. Mutumin da alama.yana tausayin ta. Haka ya nade rigarss duk da warin da take haka ya kinkimeta dan tuni ta dawo sirriya Kamar Mai cutar kanjamau. Da alama gidan nasa a wajen gari yake dan sai da suka yi tafiya Mai nisa Yana yi yana ajiyeta yana sosa hanci da wari ya saka ya ringa haka,karar motocin da take ji yasa ta gane sun kusa titi. Hawaye ne ya hau zubo mata dan idan ya ajiyeta bata san waye zai taimaka mata ba,Yana kuwa zuwa bakin titi ya ajiyeta yana "da ace kina iya magana da kin fadamin wani naki na neme shi na Kai ki,a yashe na tsince ki a daji da naje saro itace,nan wajen gari kike hanyar barin garin Abuja bansan Mai ya kawo ki Nan ba,har ga Allah naso na taimaka miki,amma naga hakan na Neman haddasa min matsala da mai d'akina Allah ya baki lafiya ya kawo Mai taimaka miki" Girgiza Kai Yaya Abu ta hau tana gurnanin Kar ya tafi ya barta ta taimaka Mata. Sai dai tana ji tana gani ya juya ya fara tafiya haka ta kwanta a titi tana sharbar kuka,ta dauka zata ma iya daga hannunta sai dai ta kasa,haka ta kwanta a kasan tana Kiran sunayen Allah dan yanzu bata da mataimaki sai Allah. Sajeeda Tunda muka dawo garin kano muka dan samu nutsuwa, Saifullahi shi ya ringa Kai kawo,bansan yadda yayi ya d'auko mahaifinsa a Kai shi asibitin mahaukata ba,sai da ya dawo yake fadamin,hawaye cike a idonsa ya hau rokona akan na yafewa Babansu iya halin nan da yake ciki kawai ya isa yasa a yafe masa dan tun a gidan duniya Allah ya ke hisabi,wani zai iya dadewa Yana sabawa Allah bai samu ya tuba ba har Allah ya dau ransa kamar yadda Allah ya dauki ran Rabiu a lokacin da bai tab'a tunanin ba,Wanda sai da ya mutu wasu da yawa Suka san halin da ya jefa kansa da arzikin sa ya fara konewa, Wanda ya na da tabbacin shi ne ya jawo mahaifunsu ya Shiga wanan kungiya,kila Allah Yana san mahaifin su da rahama shi yasa ya tona Masa asiri a gidan duniya kowa yasan halin da jefa kansa a ciki,na tuna baya da ba haka yake ba, mahaifunsu nagartacen mutum ne,haduwa da mugun aboki da San zuciya ya Kai shi ya baro" Hawaye kawai ke zubo min dan duk maganar da yayi ba karya tun kafin ma ya rokeni akan na yafewa Kabiru na yafe Masa dan Allah Yana San masu yafiya,nima zanso ya yafemin kura kuraina,ko iya warkar dani da yayi a lokacin da na fid da rai da rayuwa na fara kawowa kaina mutuwa Allah ya mikar dani, cikin ikonsa ya nuna min tsafi karya ne,raina a hannunsa yake ba a hannun kowa ba shi yake azurta Wanda yaso ya Kuma talauta Wanda ya so Allah shi buwayi ne gaggara misali,yayi min niimar da zan dawwama ina gode masa dan bana Jin ko duk kudin duniya zaa hada dan a nema min magani zan iya samun sauki,cikin ikonsa ba tare da an sha wahalar komai ba ya warkar dani,iya wanan kawai ya Isa yasa na yafewa Kabiru da Yaya Abu da naji kwana biyu ta tsaya min arai,bansan inda take ba dan bata je gida ba Nasan duk Inda take tana nan tana Shan wahala har ga Allah balain tausayinta nake ji,dan ko makiyina bana Masa fata ya Shiga halin da na Shiga balle jinina da muke uwa daya uba daya,cikin sheshekar kuka nacewa Saifullahi na yafewa Kabiru duniya da lahira yamin godiya ya kalli kanensa ya musu nasiha yace su ringa yiwa abbansu Addu'a,yayi wa Yesmeen godiya irin daiwaniyar da tayi dani. Ya maida kallonsa Kan Nusrah da ke rik'e da jaririyarta tabi ta rame Kamar ba ita ba,ya Kira sunanta ya fara magana Yana "Bawa bai Isa ya tsallaka kaddarar sa ba Nusrah hakuri zakiyi haka Allah ya kaddara Mana,banso na cigaba da miki b'oye b'oye mijinki ya aiko Miki da takardar ki saki biyu ya Miki yace bazai iya cigaba da zama dake ba idan kinyi yaye zai zo ya dauki yarsa" Jarumtaka na aro na yafa na hau sallati a zuciyata,abinda nake ta gudu kenan amma ba yadda zamuyi Na daure na fara magana Ina "Nusrah kice alhamdulillah" Nusrah take tabi umarnina tayi hamdala Banga alamar tashin hankali a tare da ita ba cikin kwantar da murya na fara magana Ina "Aure rai ne dashi Nusrah Allah yayi aurenki dashi ya Kare Koda ba ta silar mahaifin

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});