Chapter 95
Chapter 95
kasa guduwa ta bar gidan,akan Sajeeda tayi karyar makanta,Wanda da batayi ba da yanzu tayi candy kila ma ta cigaba da makaranta,duk wahalar nan da ta Sha da rashin bacci da kwanan fargaba na kusan shekara fassarar da Nusrahh zata mata kenan har da mata Allah ya Isa,sosai taji ciwon abinda Nusrah tayi mata,Aisha ma bar Mata d'akin tayi kanta kamar ya rabe biyu saboda ciwon da yake,gashi batasan halin da Sajeeda ke ciki ba. Damuwa da kuka a daidai lokacin nan bazai kareta da komai ba dukufa agaban mai kowa mai komai shi yafiye mata a ayanzu dan tasan Kabiru bazai tab'a barinta ba zai iya komai dan yaga bayanta. Bandakin da ta gani ta shige bata damu da sanyin ruwan ba tayi wanka jikinta sai rawa yake saboda yunwar da take ji. Amma bazata iya cin abincin ba. Tana fitowa daga bandakin tayi wajen wadrobe din da ta gani,dan da alama Aishar bar Mata d'akin tayi dan ta kwana ita kadai, duk da baa Mata izinin tab'a Kaya ba doguwar rigar da ta gani a goge ta d'auko ta zura ya mata yawa sosai dan Aisha ta fita tsayi sosai har kafarta sai da ya rufe,a dube dubenta ta samo hijabi har kasa ta saka,ta rufe wadrobe din,a can gefen da taga a shimfida sallaya ta nufa dan har da Qur'ani a wajen. Sai da tayi addua ta samu nutsuwa ta tadda sallah tare da ayyanawa tana gaban A Rahman a Raheem yasan me a zuciyarta,yasan mai tazo nema a wajensa tana da yaqinin zai amsa mata dan shi Mai amsa adduar bayinsa ne,mai taimaka wa bayinsa ne a lokacin da suke cikin tsanani,sallah raka'a shidda tayi,ta sallame ta dauki carbin da ta gani ta hau Jan istigifari sai da tayi dubu,ta hau yiwa Annabi sallati tana Jan majina dan har lokacin hawaye bai yanke a fuskarta ba,sai da taji yatsunta na ciwo ta ajiye carbin ta d'auko Qur'ani ta fara karatu,sai da ta karanta iya yadda zata iya ta ajiye Qur'anin,ta koma tayi Sujadda tayiwa Annabi sallati goshinta a kasa ta karanto sunayen Allah 99 kafin ta dago da hawaye Shabe shabe ta daga hannunta ta fara Addu'a "Ya samiu dua ya rabbi Maliki ya quddusu ka bawa ummana lafiya ka tashi kafadunta, Alhamdulillah ya rabbi mungode maka da tarin niimomin ka a garemu wanan halin da muke ciki Kai ka jarrabcemu ya Allah ka yanke Mana ka sausauta ma na ba dan halinmu ba,ka tausayawa umma ka tashi kafadunta kai kake da iko akan kowa da komai,ya Rahimu ka gwada ikonka akan Abba ka bawa Umma lafiya ka bata ikon tashi akan kafafunta ka bude mata bakinta ta iya magana dan ta wanke zargin da Nusrah ke min,ya Allah ka kadai ne shaidata ba yadda za'ayi na cutar da umma ko na bari a cuceta Allah a yanzu banida yadda zan taimaka Mata ya Allah ka taimaka mata ka ara Mata tsawon rayuwa Allah ka nuna min ranar da zata warke kafin na koma gareka" Kuka kawai take rusawa jikinta na rawa sai da ta dade kafin ta cigaba da Addu'a mai tsayi,rawar da taga jikinta nayi har tana Jin jiri yasa ta rufe Addu'ar da amanar rasulu ta shafa ta kwanta akan sallayar ba jimawa bacci yayi awon gaba da ita cike da mafarkin Sajeeda. 3am Sajeeda A hankali na bud'e idona sai na Kara maida idona na rufe,a rufewar da nayi bana so na yaudari kaina nayi tunanin Ina rayye,duk da ban tab'a mutuwa ba nasan duk Wanda ya mutu binne shi akeyi a Kai shi makwancinsa wato Kabari Wanda a yadda ake bamu labari ana dawo maka da ranka,sai dai banjini a Matse ba,banjini a dadaure ba,ba dai bayan na cire rai da rayuwa na jiyo kamshin mutuwa ba mutuwar nayi ba,a hankali na Kara bud'e idona sai na kurawa saman rufin d'akin ido na mintuna kafin na juya kaina na kalli gefena na Kara juyawa na kalli daya gefen,tuni tunanina ya bani inda nake wato asibti,daga b'arina na hagu nurse ce a kwance a daya gadon da ba kowa. A hankali na daga hannuna na dora akan kirjina naji Yana bugawa na mitsini kaina a daidai wajen da nake Jin bugun zuciyata sai naji tabbas ba mafarki nake ba Allah ya barni a raye bayan na fidda rai da rayuwa,Allah ya barni a raye bayan ciwon da naji a kirjina da na kwatanta shi da ciwon ajali,Ashe Ina da sauran kwana a gaba, Ashe cuta ba mutuwa bace ba,tuni hawaye ya hau zubo min Ina daga kwance wallahi ban taba tunanin Zan rayu ba,kuka na fara yi kasa kasa na fara motsa bakina dan nace Alhamdulillah. Ga mamakina sai naji sautin maganata a kunnena,sai na zaro idona na hau wuwurga idona naga ko dai wata ce a gefena take hamdala na dauka nice,sai dai banga kowa ba nurse ce dai dake bacci a daya gadon. Kirjina na dan bugawa da Kar na yaudari kaina na Kara cewa "Alhamdulillah ya rabbi" Sai na Kara Jin sautin muryata a kunnena. Sai na saki murmushi Ina tunanin yadda nake neman saka rai da magana bayan nasan da wuya. Sai na Kara gwada magana Ina "Yesmeen Kinga Zan yaudari kaina Ina Jin maganata a kunnena" Sautin maganar ya Kara tafiya kunnena daya saka jikina d'aukar rawa nasan abune da bazai yu nayi magana ba taya kunnena ke yaudarar kaina da Ina magana har maganar tawa na fitowa. Sai naja tsaki a zuciyata na fi minti goma a haka kafin na waiga wajen nurse ina bari na sake yaudarar kaina sai nace "Nurse ki bani ruwa in Sha" Sai naga ta bud'e idonta tana kallona,sai na zaro idona Ina Jin bugun kirjina da ido na bita naga ta sauko daga gadon ta nufo wajen da nake tana "Yanzu nan fa bacci ya daukeni ruwa zaki Sha" Jikina wani irin rawa yake hannuna da nake iya motsawa na Kai na damki hannunta Ina "Kina nufin kinji Mai nace"? Sai naga ta yamutsa fuska sai ta kawo hannunta ta tab'a kaina tana "Ko dai zazzabi ne a jikinki bangane naji mai ki ka ce ba ba ruwa kikace Zaki Sha ba"? A hankali na saki hannunta na maida idona na rufe bazan iya fassara halin da nake ciki ba,hakane kawai yasa na rushe da kuka na hau yiwa Allah godiya,Ina addua Allah yasa ba mafarkan da na Saba yi bane nayi akan Ina magana,Allah buwayi gaggara misali,Allah maji rokon bawansa,Allah mai amsa adduar bayinsa a lokacin da ya fidda rai,dan wallahi na fidda rai da rayuwa ko iya maganar Allah ya bani ikon yi alhamdulillah bani da bakin gode masa,Ina ma zan ga Yesmeen Ina ma tana kusa dani,Ina ma itace ta fara jin muryata,nasan bazan iya fassalta farinciki da zata yi ba ,ta Sha cewa tayi kewar murya ta,ganin nurse din ta fice waje yasa na fara magana a fili dan na tabbatar "Alhamdulillah ya Allah Alhamdulillah Allah da ka nuna min Wanan ranar da zan iya magana, Kabiru asirinka ya tonu" Wallahi naji sautin maganata ta tafi kunnena dan da k'arfi nayi, Kukan farinciki kawai nake,tunanin da ya fado min yasa na gwada daga daya hannun nawa sai naga na daga sai na zaro idona, bana iya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111