Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 81

Chapter 81

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,216 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

cikin aminci 🤝 Sai Allah yakawoku *WANAN NOVEL DIN NA KUDI NE NA HADA KU DA FIYAYYEN HALLITA ANNABI MUHAMMAD SALLAHU ALAIHI WA SALAM KARKU MIN SHARING NOVEL IDAN BANA KALLON KI ALLAH YANA KALLON KI KUDIN KARATU KIKA BIYA BANA MALLAKA BA IDAN KIKA FITAR NA BAR KI DA ALLAH GA MAI BUKATA SAI TA BIYA 500 ZUWA WANAN ACCT DIN 2029764071 FIRST BANK NAFISA NUHU KO KATIN MTN TA WANAN LAYIN 08033719070 KO WANAN LAYIN 08068484400 SAI A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANAN LAYIN 08033719070 KO WANAN LAYIN 08033719070 MUTANEN NIGER KUMA SU NEMI WANAN LAMBAR +227 96 82 89 84* *PAGE 60-65* Kabiru turus yayi Yana kallon Yaya Abu da jikinta ke balain rawa hannun ta na Kan pillow Yesmeen dake kasan gado kuwa ta janye hannun ta da sauri kirjinta sai bugun uku uku yake tana Addu'ar Allah yasa Kar Yaya Abu ta lekota ledar dake kasan gadon da ledar katifa ce ta shige ciki ta kudundune. Yaya Abu kuwa wani irin tsorone ya rufeta ta ma kasa cire hannunta daga Kan pillon da take so ta danna akan Sajeeda, tsoron ganin Kabiru da cafkar da taji anyi wa kafarta ta kasan gado ya matukar razanata. Kabiru kuwa kasa hada tunanin sa yayi gu daya Yana tunanin mai ya kawo Yaya Abu d'akin Sajeeda a daidai wanan lokacin da yake a matukar bukace kamar ya haukace dan maganin karfin maza ya kwankwade gabadaya saboda Kar ma jikinsa ya kwanta dan ta karfin tuwo yau yake so ya samu biyan bukatar sa jikinsa har wani rawa yake saboda ya matsu ya samu biyan bukatarsa jikinsa a tsaye kyam Hannun Yaya Abu da ya gani akan pillon dake fuskar Sajeeda da har lokacin bata iya d'auke hannunta ba yabi da kallo. Sajeeda kuwa ta fara sheshekar kuka dan ta gane wani ne ya shigo d'akin shi yasa Yaya Abu bata danne pillon ba hannunta dake rawa ta Kai ta cire pillon daga fuskarta,sai a lokacin Yaya Abu ta iya motsawa ta janye hannunta da sauri Kabiru da ya gama hada tunanin sa waje daya cikin tsananin mamaki ya dago hannunsa Yana nuna Yaya Abu da "Kasheta kike so kiyi"? Girgiza kai Yaya Abu ta fara yi cikin tashin hankali ta fara magana cikin inina ta ja da baya dan ji take kamar zaa Kara cafo kafarta tana "Naaa shigo ne dan na dubata Kabiru taya Zan kasheta" "Abu pillo fa Kika dora mata akan fuskarta kina k'ok'arin dannewa na shigo innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Abu kashe Sajeeda kike so kiyi"? "Yaya Abu da jikinta ke balain rawa grigiza kanta ta fara yi da sauri sai a lokacin ta gane ma a tsirara kabirun ya shigo ga gajeren wandon sa a kumbure. Gwallo ido tayi tana Kara Kare masa kallo a daidai lokacin da ya fara takowa cikin d'akin jikinsa na balain rawa da tsananin mamakin abinda yaga Yaya abu na Shirin yi dan sai yaji ma sha'awarsa na sacewa Saboda tashin hankali abinda ya shigo yaga Yaya abu nasan yi,"Abu kashe Sajeeda kike so kiyi "? Yaya abu cikin dakiya da borin kunya ta fara magana tana danne tsoron da take ciki "Kaine dai ka shigo kake san kasheta Kabiru taya Zan kashe kanwata,Kai mai ya kawo ka d'akin ta a haka yanzu a halin da Sajeeda take ciki har zaka iya nemanta? innalillahi wa Inna ilaihi rajiun yanzu so kake ka karasata saboda ka samu kayi Aure,ai ba sai ka kasheta ba Kabiru zaka iya sakinta mu tattara mu bar maka gidan,har ace a halin da Sajeeda take ciki na a kwantar a tayar zaka iya nemanta toh ta Ina ma zaka nemeta a halin nan da take ciki idan ba kasheta kake so kayi ba" Kabiru da ransa ya fara b'aci ya daka Mata wani irin tsawan wargaza masa shiri da take Shirin yi gashi duk alamomin rashin gaskiya ya bayyana a fuskarta shi ba yaro bane da zata raina Masa hankali danne pillon take so tayi a fuskar Sajeeda ya shigo "Laifine dan nazo wajen matata ko da nemanta nayi haramune karki wani wayance Abu dan da zuciya daya muke zaune dake a gidanan ban taba kawowa zaki iya aikata haka ba,Kiri Kiri naga kina san danne kanta da pillo har mai kanwarki ta miki haka da kike so ki kasheta ?dama haka kike?yanzu da ban shigo ba kasheta zakiyi kenan Mai ta Miki"? "Ni zaka yiwa sharri Wai taya Zan kashe Sajeeda gurnanin ta na jiyo Ina daga daki shine na shigo dan na dubata,ganin bata dora kanta a pillow ba yasa na daga kanta dan na dora Mata pillon sai naji an ja kafata ta kasan gado hakane yasa na saki pillon a kan fuskarta dan zaka ji ma nayi ihu lokacin da ka shigo wallahi ba kasheta na shigo nayi ba karka manta fa kanwata ce uwar mu daya uban mu daya akan me Zan kasheta"? Sajeeda Wani irin kuka ne ya kwace min da naga Abban Nusrah yayi shiru alamar karyar da ta tsara Masa yayi tasiri a zuciyarsa na fara girgiza kaina Ina nuna ta da hannu Ina "Mai na miki Yaya Abu da kike San kasheni?Mai na Miki da na cancanci haka daga wajenki?iya sanina ban taba miki komai ba,yanzu akan duniya kika zabi ki kasheni?mai na Miki kike so kiga kin rabani da numfashina"? Duk cikin gurnani nake magana Ina nuna ta da hannuna da naga kabiru ya zubawa ido cikin mamaki Yana kallo da alama bai tab'a tunanin zan iya motsa hannuna ba kirjina ciwo kawai yake min Ina kallon makiyana guda biyu Abban Nusrah shi ma shigowa yayi dan ya nemeni ta baya dan a tub'e yake daga shi sai gajeran wando,mijina uban yayana shi ya jefani a halin nan haka bai ishe sa ba sai ya Kara nemana ta baya,ya karasani daya gefen Kuma yayata da muke uwa daya uba daya da ita,ita takeso ta kasheni wai dan ta aure shi,akan ta gan shi da kudin da bata San da ya ya same shi ba kuka kawai nake Ina cigaba da nuna Yaya Abu da hannu Yaya Abu da hankalin ta ya Kara tashi da yadda taga Sajeeda na gurnani tana nunata da hannu ta matsa kusa da ita da sauri dan gani take tunda ta iya motsa hannunta kila ma bakinta ya budu tayi magana ta tona mata asiri Ta ruko hannun Sajeeda tana "Ya Isa haka Sajeeda dole kiyi kuka saboda Kinga mijin ki na neman yimin sharri daga nazo na taimaka miki,amma ba komai tunda kora da hali yake min goben nan zan tattara na bar gidan kafin wani Abu ya Sameki ace nice ni nasan wani ne ya shigo dan ya cutar dake tunda na ji an rik'e min kafa ta kasan gadonki" Fusge hannuna nayi daga rukon da tayi min Ina cigaba da gurnani, Abban Nusrah ya matso kusa da gadon ya ruko hannuna yana "Sajeeda Alhamdulillah kin fara iya motsa hannunki alamar kin fara samun sauki da kina da baki da kin fada min gaskiyar abinda Abu ta shigo yi miki dan daga yadda kike gurnani ni nasan bata da gaskiya bansan mai kika Mata take so ta kasheki ba" "Wai ya zaka ce Ina so na

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});