Chapter 17
Chapter 17
ne yayi, idan har ta samu Sajeeda a boye ta sanar da ita,kila ta san yadda zata b'ullo musu su tsira da ran su ba abinda ya daga mata hankali da taji labarin masu yin kudin tsafin nan a karshe sai sun bada jinin su anyi kudi dasu,tana tsoron yayi kudi da wani a cikin yaran sa ko ita ko Sajeeda. A kallon da take yiwa Kabiru yanzu ba abinda ba zai iya yi ba dan ya riga da yayi nisa. Bakin Karen nan daya kawo musu gida jikin ta na bata akwai wani mumunan al amari a tare da Karen dan yadda yake tatala Karen na matukar bata mamaki, da kan sa yake kaiwa Karen abinci yanzu ko fita yayi ya dawo wajen Karen yake fara zuwa ya duba, idan ba karya idon ta ke mata ba akwai wani abu kamar pant da take gani an rataye wa Karen a wuya, idan tana kallon Karen ma sai taga Kamar ba normal kare ba,a yanzu d'akin da ta ga ya lodawa kwado kawai take so ta leka taga mai a cikin d'akin da yake b'oye wa. Haka tayi ta tunane tunane har aka Kira sallah Asuba ta tashi tayi sallah,tasan ba wai zurfin ilimi ko wani sani ne da ita ba amma tana rokon Allah da tawasali da kyawawan sunayen sa da sallatin da take yiwa mafi soyuwa a gare shi ba dare ba rana daya haska mata lamarin Kabiru kada Allah ya bashi ikon cutar da su. Sai da ta shafa ta koma bacci sai tayi sallah take samu tayi bacci Mai nutsuwa. Ko awa bata yi da komawa baccin ba ta fara mafarki Mafarki. Mafarki tayi a kwancen da take Karen dake bayan d'akin ta nata haushi Wanda Haushin da yake yi ne yasa ta bud'e idon ta. Can Kuma ta fara jin ihun Sajeeda Wanda ihun da take yi yasa ta mik'e da sauri ta fice daga d'akin tayi bayan gida. Inda ta tarar da Sajeeda a kwance a kasa Karen ya danne ta suna ta kokawa ita Kuma Sajeeda nata ihu,tana rik'e zanin ta da kamar zanin nata Karen ke san fusgewa da bakin sa. Ganin ta da Sajeeda tayi yasa ta fara mik'o mata hannu akan tazo ta taimaka Mata" Waige waige ta fara yi ta hango katon icce,ta tafi da gudu ta d'auko itacen tayi wajen Karen dan ta kwada wa Karen ya daga Sajeeda sai ta hango Kabiru ya taho wajen ta a guje da wuka yayo kanta kafin ya caka Mata ta farka a gigice tana sallati. Ko da ta farkan sai taga kamar d'akin juya mata yake sai da ta dawo daidai ta gane mafarki take yi,Wanda mafarkin kamar a zahiri,da sauri ta mik'e tayi waje tana fito wa palon ta tarar da Sajeeda a Palo da Kabiru dasu Saifullahi a zaune suna karyawa. Yadda ta Fado palon a firgice yasa Sajeeda mik'ewa tana "Yesmeen lafiyar ki kuwa"? Yesmeen da bata ma san rik'e take da zuciyar ta ba ta saki ajiyar zuciya tana godewa Allah da mafarki take, kallon tsanar da Kabiru ke jefo Mata yasa ta juya da sauri tana "Umma lafiya kalau mafarki nayi mara Dadi" Sajeeda kuwa ta cigaba da bin ta a baya har suka shige d'akin. Yesmeen ta rage tsayinta ta fara gaida Sajeeda da ta zauna a gefen gadon. Sajeeda ta amsa tana Kare Mata kallo dan wajen takwas da taga bata ji motsin ta ba ta yanke yi musu abincin dan tasan kila gajiya yasa Yesmeen din bata tashi ba. "Mafarkin me kika yi haka daya saka Kika fito a firgice"? Yesmeen kuwa da taje bakin windo tana leka Karen da ya dallaro harshen sa waje tana Kara tuna mafarkin da tayi ta juyo a hankali ta kalli Sajeeda taga irin kayan da tayi mafarki da Sajeeda ta saka shine a jikin ta sai taji hankalin ta ya Kara tashi,so take ta gane Mai fassarar mafarkin da tayi kafin ta fadawa Sajeeda wani Abu. Kabiru ya banko kofar da k'arfi Yesmeen a firgice ta ja da baya Sajeeda kanta sai da ta tsorata Kabiru cikin hade rai ya fara magana Yana "Baki ji Ina Kiran ki bane"? "Ban ji ba Abban Nusrah" Sajeeda ta mik'e tsaye dan ita yake kallo Yesmeen kuwa ta sada kansa kanta kasa dan a yanzu ba hallitar da take gani ya firgitata sama da Kabiru,bata San ya akayi Sajeeda bata tab'a lura da yadda jikinta ke rawa idan ta gan shi. Sajeeda bayan Kabirun ta bi sai da suka koma Palo suka zauna ya d'auko kudi daga Aljihunsa gudan Dubu Dubu ya fara mik'a mata Yana "Gashi nan a siyo Abubuwan da Babu a gidan" Turus Sajeeda tayi tana kallon kudin,dan a yanzu kudaden da take gani a hannun Kabirun ya fara girmama tunanin ta "Ki karba mana kika tsaya kallona" "Abban Nusrah Dubu dari naga fa kana miko min Abban Nusrah Ina kake samun kudi haka,a kasa da wata uku kayi irin wanan kudin" "Sajeeda idan har bayanin da na Miki na samun kudina bai gamsar da ke ba kisa a ranki sata nakeyi tunda ke dama baki tab'a kyautata min zato ba kullum sai dai ki munana min,Ina ga ai na fada miki duk karshen wata zan ringa d'aukar al bashi miliyan daya toh jiya albashi nayi idan kin ga dama ki yarda idan baki ga dama ba karki yarda wanan matsalar ki ne daga yau karki sake min tambayar daga Ina nake samo kudina ni ba yaron ki bane da Zaki saka ni a gaba kina min tambayoyi kamar danki. ke a rayuwar ki rayuwata ta baya ta kanikanci ne yake burgeki na dauko dari biyu ko dari da hamsin na baki, toh ni da wanan rayuwar da kike min fata har abada arziki da budi yanzu na fara gani,idan Zaki saki jiki ki mori niimar da Allah ya Mana toh,idan bazaki saki jiki ba wanan matsalar ki ce. Daga haka ya mik'e tsaye ya fara kwalawa Yesmeen Kira Da sauri Yesmeen dake daki ta fito har tana tuntube Tana isowa ta zub'e akan gwiwarta kamar dai yadda ta saba cikin girmamawa. Ya d'auko kudin ya mik'a mata Yesmeen hannunta ta hau rawa tana zuba addua a zuciyarta dan yanzu duk abinda zai fito daga hannun Kabiru tasan ba na halak bane. Daurewa tayi ta karba Kabiru cikin hade rai ya fara magana Yana "Kije kasuwa ki Karo Mana kayan amfanin gida dan Naga alamar babar ki bata san zuwa" "Kamar dame dame zaa siyo"? Kabiru shiru yayi Kamar mai nazari sai can kuma ya karbi kudin Yana "jeki Sako hijabin ki sai muje kasuwar idan na gama Miki siyayyan sai ki kawo kayan gida ni na wuce wajen aiki" Sai a lokacin Sajeeda tayi magana tana "Bance bazan je ba Abban Nusrah ka kawo na siyo kayan" "Bazan bayar ba" "Allah ya baka hakuri tunda kace da kan ka za ka siyo mai zai hana ka tafi da su Saifullahi Yesmeen Ina ga ko karyawa bata yi ba" "Da ita Zan tafi idan zaki hana Kuma sai naji" Sajeeda bata Kara cewa komai ba taja bakin ta tayi shiru. Yesmeen kuwa ta mik'e hankalin ta a tashe tayi cikin d'akin ta tana zuwa ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111