Chapter 99
Chapter 99
bakinsa. Duk da ƙyawun da yayi cikin ɗanyar shadda fara tas da ƙiba daya ƙara da haske hakan bai hana iyalan nasa shaida shi ba. A take fara'ar fuskar Inna ta ɓace ɓat sai gabantane ke wani irin bugawa da sauri-sauri kamar zai buɗe. Cikin rawar murya tace, “Malam?!”. “Na'am Asabe”. Ya amsa kansa tsaye yana kallon cikin ƙwayar idanunta. Baya tai a tsorace zata zube dan ruɗani, a dai-dai sansa du Yaya Gajeje ke haɗa baki ita da Sa'a da Tinene data tashi zaune da ƙyar wajen kiran “Baba!”. Nanma kai tsaye ya amsa musu da “Na'am ƴaƴana”. Ai tuni Sa'a ta kwasa da wani irin gudu tayo kansa batare data saniba. Ta faɗa jikinsa tana fashewa da wani irin kuka maiban tausayi. Hannu biyu yasa wajen riƙe abarsa yana murmushi, ya miƙama Tinene hannu itama. Da sauri tayo kansa duk da halin ciwo da take a ciki itama ta shige jikinsa. Hayaniyarsu tasa Karima fitowa itama. Ganin Babansu yasata kware baki cike da firgici ta kwala ihun daya jawo hankalin maƙwafta suka fara leƙe ta kantaga. Sai gashi cikin ƙanƙanin lokaci gida ya ɗauki harama. dan tuni ashe jama'ar gari sunga baba sanda yake shigowa garin tare da matarsa. A take gida ya ɗauki murna, dan tuni dangin baba su Gwaggo Laritu harsun iso jin labarin dawowar ɗan uwansu. Sai koke-koke akeyi na farin ciki. Da ƙyar aka samu gidan yaɗan natsa aka kawoma Baba da baƙuwarsa ruwa. Babu musu suka amsa suka sha dan sunada buƙatarsa. Baba Rabilu cikin kasa haƙuri yace, “Yaya gaka da baƙuwa kuma bamusan wacece ba?”. Murmushi baba yayi yana mai kallon ƙyaƙyƙyawar matar, zuciyarsa fes da farincikin daya bayyana a saman fuskarsa yace, “Itama yayarku ce. Dan tazama ɗaya daga cikin zuri'armu tunda ta kasance Matata harma da tsohon ciki gashi nan”. Cikin mamaki da nuna bayyanannen farin cikinsu suka shiga sake mata gaisuwar girmamawa. itako cike da fara'a da mutuntawa a garesu take amsawa. Babu wanda ya lura a cikinsu sai jin faɗuwar Inna sukai timmm a ƙasa. Dan hatta da Tinene sai da ta gaida matar da baba ya kira da matarsa. Karima ce kawai ta wani gwalalo idanu tana kallonta. Kusan su duka kan Inna sukayi, banda Baba da ko motsi baiyiba sai dai ya kalli wajen. Ruwa Sa'a ta ɗebo da sauri ta kawo, Gwaggo Laritu dake riƙe da Inna ta amsa ta shafa mata a fuska. A take ta kawo numfashi tana binsu da kallo. idonta ta sauke akan baba da Amaryarsa. Babu zato sukaji ta fashe da kuka kawai ta fara sambatu “Dan girman ALLAH na roƙeku ku taimakeni ku hwaɗa mani gaskiya, kuce dani mahwalki nake ba gaske baneba, na shiga uku ni Asabe. Yanzu malam irin sakayyar da zakaimin kenan akan wahalar ganin ka dawo gida da nakeyi tsahon shekaru? Yanzu malam duk hwaɗi tashin da nake akanka karasa da abinda zaka dawo gareni sai kishiya? Na shiga uku na lalace ni Asabe. Shikenan watan lalacewata ya tsaya kuma sai abinda ALLAH yayi. Ku dubetahwa jama'a kamar aljana. Wlhy tahi Hauwa kyau da ƙuruciya.....” Ta ƙare maganar da ƙara jan wani nannauyan numfashi alamar ta sake suma......... ____________________________★ *_KANO_* Bayan dogon zaman jira dasu AK sukasha sakamakon gwajin DNA ya fito daga likitocin guda uku, Batare da ko su Dr Mahmud sun dubaba aka mikama Baffah. Shima ɗin bai buɗeba ya sake miƙama Dr Mahmud dan yasan amintaccen AK ne. Kuma shina ya yarda dashi ɗari bisa ɗari. Dr Mahmud da duk al'amarin yake neman rikita masa kai ya amsa ya buɗe takardun ɗaya bayan ɗaya zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri-sauri. Sai da yayma takardun kallon kusan sakan biyar kafin ya ɗago ya ɗan dubi sashen da AK ke zaune rungume da Little dake barci yanzun. Cikin wani irin rawar murya da firgicin abinda ya gani ya maida kallonsa ga takardun yana magana da rawar harshe. “Ba lallai ku fahinci duka bayanan cikin takardun ba saboda wani abun daga bincike likitocine kawai. sai dai ina mai sanar muku cewar zan faɗi gaskiyar abinda na gani kamar yanda baffa ya bukata tsakanina da ALLAH”. Ya ɗan sharce gumin daya taru masa a goshi da cigaba da faɗin, “B...Baffah sakamakon duka takardun ya nuna ya..ron... Na na na AK ne, dan duk ƙwayoyin halitarsa babu banbanci da yaron kamar yanda ya biyosa a kammani”. Ya ƙare zancen da tsananin raunin harshe dana zuciya. Kusan a tare suma su Baffah zukatansu suka buga. AK dakejin kansa na neman tarwatsewa ya ƙanƙame little a jikinsa yana rumtse idanunsa da matuƙar ƙarfi, har takai yaron ya farka daga barci yana ƙoƙarin fara kuka saboda jin matsar da akai masa. Yanda yayi ɗinne yay matuƙar tada hankalin Dr Mahmud da gaba ɗaya hankalinsa ke akansa. Da sauri ya miƙe zuwa garesa yana ambaton sunnsa. Hakanne ya fargar dasu Baffa ruɗani da ɗimuwar da suka shiga suma duk sukai kansa. Da ƙyar suka iya ɓanɓare little daga jikinsa, Baffah da Abba suka riƙe AK ganin jikinsa na wani irin rawa maiban mamaki da tsoro, cikin ƙanƙanin lokaci kuma duk sai gaɓoɓinsa suka saki alamar ya suma. Wannan shine tashin hankali wanda ba'a saka masa rana, dan kuwa dai Baffah ji yay tamkar ya fasa ihu dan tashin hankali goma da ashirin, yana matuƙar ƙaunar AK a ransa. Dan yana ɗaya daga cikin ɗa mafi soyuwa a garesa, sai dai yana dannewa ne gudun rarraba kan ƴaƴansa. Da ƙyar suka iya ɗagasa zuwa gadon duba mara lafiya dake a office ɗin Dr Mahmud. Mmn Sadiq kam kuka take sosai dan gaba ɗaya ta gagara fahimtar wannan al'amari maiban ruɗani da al'ajabi........ *_BAYAN WASU AWOYI_* Bayan wasu taƙaitattun awoyi aka samu nasarar farkawar AK da tun ɗazun ya farfaɗo daga sumar da yayi. A hankali ya buɗe rinannun idanunsa ya saukesu akan Baffah dake zaune riƙe da hannunsa. Sai Abba dake ta wajen ƙafafunsa shima a zaune. Mmn sadiq kam ta wuce gida tuni tare da little dan taje ta huta itama gudun kar taje ƙasa. Dan kallo ɗaya zakai mata ga gano tsananin tashin hankali da ruɗaninta. Kallonsu yayi ya maida idanun ya lumshe a hankali yana wani irin murmushi da baida maraba da kukan ƙunar zuciya. Idanunsa a lumshe yace, “Baffah nasan ba lallai ku yarda daniba akan bansan yaya akai na samar da Abdul-Mutallab ba. Domin ni kaina na kasa yarda da kaina balle ku da zan faɗamawa. Sai dai ku sani lallai ina cikin *_MAKAUNIYAR ƘADDARA_* babu wani haske da zai haska min idanun ganinta kuma sai UBANGIJINA da haƙurin fahimtata da zakuyi na ɗan wanu lokaci dazanyi ƙoƙarin ganin bakin zaren, b.........” Saurin katsesa Abba yay ta hanyar faɗin, “Ya isa Adnan. A yanzu halin da kake ciki baya buƙatar duk waɗanan maganganun. Dan Mahmud ya tabbatar mana da jininka yayi ƙololuwar hawa sama. idan kuma ka matsa da yawa za'a iya samun matsala. Mu dukanmu nan musulmai ne, muna kuma iya fahimtar yaran ƙaddara ko jarabawa, suk da dai ita wannan tazo mana a makance. Dan kai da Zinneerah ne ya kamata muji amsar tambayoyinmu a gareku, sai kuma gashi kuma neman amsoshin kukeyi a karan kanku. A ganina mafita ɗaya ce da shawara ta rage mana Alhaji”. Ya faɗa yana duban Baffah. Kai tsaye
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182