Chapter 35
Chapter 35
Da ƙyar ta lallashesa tana dungure kansa da goyasa wai karya tona mata asiri Mama tazo tai mata faɗa ta tada ɗan aljanu kuma. Kwana uku dayin maganarnan aka saka Zinneerah islamiyyar safe zuwa 2 sun taso. Kusan dai-dai da yaran gidan kenan amma ƴammatan kawai dake shirin gama secondary. Su Sadiq kam sai shidda suke tasowa makarantarsu haɗe take da islamiyya. Faɗa muku irin kalar farinciki da Zinneerah tayi ɓata lokacine. Sai da akaje makarantar kuma ta raina kanta dan batasan komaiba. Amma tayi alwashin nutsuwa sosai ta fahimci komai ɗin kodan ta ribantu a duniya da lahirarta _________________★ A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI. Yau ga Abdul-Mutallaf (Little) da wattani bakwai a duniya. Yaro ƙyawunsa nata ƙara fitowa fili da lafiya ingantacciya. Bazaka taɓa cewa ba abincinsa yake samu daga mahaifiyarsa ba. Dan ma zazzaɓin haƙora kan girgiza kuzarin nasa wasu lokutan. Amma da yake zuwa yanzun cin abubuwa yake sosai, dan su Aliyu komai suka yayo kimsa masa suke shiko ya cinye abunsa sai hakan ya ƙara taimaka masa aynun. Rarrafe yake ko ina ga ɓarna, inda yana waje kowa kaye-kayen kayansa yake inba hakaba yazo ya tarar an canja musu sabon tsari. Babu ruwansa da Zinneerah, hasalima ƙyuya yake mata wani lokacin. ba komai ya jawo hakanba sai itama rashin kulashin da takeyi sosai. Dan komansa Maman Sadiq ce sai kace itace uwarsa. Shi da su Sadiq kuwa ai da kuka ake rabuwa idan zasu makaranta. Dasun dawo kuwa zakaga walwalarsa ta daɗu. Zinneerah nata karatun islamiyyarta wanda a yanzu tayi matuƙar yin nisa dai-dai gwargwado, dan ko a Alkur'ani ta kusa kai izifi biyu, ta saka himma sosai. Hakama sauran littatafai bata wasa. Bokon dai ce ba'a kai ga sakataba har yanzu saboda wasu ƴan dalilai da suka riƙe Abba. Amma yanata shirin hakan batarema da sanintaba. ★★★★★★ Little nada shekara ɗaya cif a duniya da ƴan kwanaki ALLAH ya bashi ikon fara takawa. Ranar zokaga murna wajen su Aliyu. Zinneerah na zaune a falon ita da Mama suka dinga ihunsu na murna mama na tayasu da dariya. Zinneerah dai ta murmusa ta kauda kanta ga abinda takeyi, sai dai a kallo ɗaya zakai mata ka fahimci kawaicine kawai takema mahaifiyarta, amma har cikin ranta tanason ɗanta da jin daɗin duk cigaban da zaizo masa a rayuwa. Duk da kuwa har yanzu tunaninta na nan akan aljanu suka saka matashi a ciki ta haifa musu. Wataran kuma zasuzo su sace abinsu. Maman Halima dake tsakar gida tana girki ta leƙo tana tambayar lafiya su Sadiq ke ihu haka?. Cike da murna Abdull yace, “Mama little ya fara tafiya”. Dariyar itama tayi, tare da shigowa ɗakin sosai ta ɗauka Little tana juyi dashi. Dariya su Sadiq suka sake sakawa. Amma banda Little da kowa ya fahimci miskilancin yaron tunda ya fara wayo. Sam baida yawan fara'a, akan daɗe ba'aga yana dariya ba. Garama idan su Aliyu ke masa wasa zakaji har ƙyalƙyalewa yanayi abunsa. Zinneerah ma catai ita daya rainama ko dariyar yake idan ya ganta dainawa yakeyi. Duk sanda ta faɗi haka mama kan girgiza kai kawai da faɗin, “ALLAH ya kaimu randa zakiyi hankali dai, harshi Abdul-Mutallaf ɗin miya sani da sai ya zaɓa wanda zaima dariyar? Kawai dai zuciya nason mai ƙyautata mata, keko ko wasa bayimasa kikeba”. Idan mama ta faɗi hakan Zinneerah bata ƙara cewa komai kuma, dan dai kam da gaskiyar mama. Idan kaga tama yaron wasa sai inba idon Mama a wajen. To kafin hakan ta faru kuwa akan jima musamman daya kasance yanzu itama ta fara makarantar boko a sukul ɗin su Sakina. Duk da Sakina nashan zubar mata da mutunci ga abokan karatunsu na cewar ai bazawarace ta taɓa aure harda ɗa. Da farko ƴan ajinsu kan ƙaryata ta sukeyi, dan a ganinsu nawa Zinneerah ɗin take da za'ace ta haihu, a yanzunefa suke shekaru sha biyar suna farkon shiga sha shida. Tsabar son ƙara wulaƙanta Zinneerah saita ƙirƙiri dinga gayyatarsu gidansu dan aga little. Wasu ko sunje sun gansa basa yarda, amma yau da gobe sai suka fara amincewa da Sakina ɗin har suna tsokanar Zinneerah. A farko takansha kuka. Amma zuwa yanzu da take neman watanni kusan biyar a makarantar sai hakan ya bar ɓata mata rai. Tama sake ɗammarar maida hankali akan karatunta kamar yanda a kullum Mama ke jaddada mata ta dage wannan karatun sai ya zame mata ado mai ƙawata tarihinta watarana. Ba fahimtar Mama takeba kai tsaye akan furucin, dan ita a shirmenta har yanzu Mama batasan yaya aka samu Little ba. Bayan sun gama darerakunsu akan fara tafiyar little ɗin Mama ta fice. Su kuma suka cigaba da hidimarsu a ɗakin kasancewar lahadice yau islamiyya kawai yaran zasuje da yamma. Ganin Little ya ɓingire ƙasa alamar barci zaiyi yasa Zinneerah ajiye buk ɗin hannunta da take Assignment ta ɗaukesa ta goyashi, dan Mama ma ta shige ciki kanta na ciwo. Fita tai tsakar gida dan ta taya Maman Halima aiki kasancewar yau ranar girkintace. Maman Sakina kawai ta samu zaune dasu Luba dake wanki a bakin rijiya. Ba wani shiga sabgarta suke a gidanba shiyyasa itama bata matsawa kanta na shiga tasu. Dan wasa-wasa Zinneerah ma akwai miskilanci da tsiwa idan taso. Sai dai yanayin rayuwar data tashi a cikine ya sakata komawa sanyi-sanyi. Yanzu ɗinma Maman kawai ta gaida taja kujera ta zauna a bakin rijiyar itama inda aka tara wanke-wanke. Cikin neman tsokana Luba ta dubeta taɗan taɓe baki, sai kuma a bazata ta bushe da dariya. Kallonta Aliya tayi, hakama Mamansu. “Luba lafiyarki kuwa da wannan dariya kamar wata mara hankali?”. Cikin dariyar tace, “Mama bazaki ganeba. Wlhy wannan agolance take bani dariya. Idan ta fita waje samarin anguwarnan suyita wani rawan kai a kanta su sun sami budurwa, shashashun basusan harda surƙumemen ɗa gareta a gidaba. Jiyafa Faisal ɗin gidan Alhaji Zubair bakiga yanda ya nacemin da tambaya akan wacece ita ba? Niko na ce masa bazawarar agolan gidanmuce”. Dariya suka bushe dashi su duka har Maman. Maman Halima dake kicin ta fito a fusace tana kallon Luba mai zancen. “Haba Luba wane shirmene haka da girmanki. Zinneerah ba ƙanwarki bace amma kike wannan sakarcin?”. Da kunƙunin rashin tarbiyya Luban tace, “A'a Umma nikam ba ƙanwata bace, dan bamu haɗa komaiba banda agolanci datazo gidanmu cin arziƙi”. “To sannu mara kunya, yanda kikejin nan gidankune itama haka gidansu ne. Dakike aibantata wajen mutane cewar bazawara kuma agola kina tunanin hakan zai hana wanda ALLAH yasa ya zama mijinta zuwa har gidan nan neman aurenta. Kubar wannan banzan halin dan baida ƙyau, ku matane gidan wani zakuje wataran kuma.......” A fusace Maman Sakina ta tare zancen. “A'a Maman Halima kinga, miye na wannan dogon alkaba'in bayan gaskiya yarinyar ta faɗa. Daga ni har ke kowa yasan ai ita agolarce a gidan. Kuma bazawara. Luban ai taimakonta takeyi wajan faɗar gaskiya dan kar bayin ALLAH suzo a rufesu a basu budurwa bayan gata harda ƙurmusheshen ɗa a baya”. Maman halima zata sake magana Maman Sadiq da hayaniyarsu ta sakata fitowa dole tai saurin faɗin, “Yaya dan ALLAH abar maganar dan bata da amfani. K kuma Luba ki kwantar da hankalinki ko baki faɗa musu ba dama idan sunzo ɗin zasu sani ai. Cin arziƙi kuma da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182