Chapter 24
Chapter 24
ya ɗarsu a rayukansu, cike da son jin ƙarin bayani Naziru yace, “Zinneerah kekam miya kawoki hanyar jigawa keda ke a jihar katsina?”. Hawayen dake sakko mata ta share tana girgiza kanta. “Nima ban saniba, na samu kaina ne kawai a haka”. Sai yanzu ne Alhaji yay magana. “Lallai da alama kamar bata cikin hayyacintane ta baro gida fa kenan”. “Tabbas hakane Alhaji, kenan har yanzu Asabe bata canjaba ko kuma Zinneerah ma tayi gamo da abokiyar zama irin Asabe a gidan aure.” Maman Halima ta faɗa saboda ganin ciki a jikin Zinneerah duk da kuwa ta saka hijjab. A karon farko shima Khalipha da tun ɗazun baice komaiba sai kallonsu ya sauke numfashi. Gyara tsaiwarsa yayi a jikin bangon daya jingina yana kallon Zinneerah da keta satar kallon maman Sadiq da suke tsananin kamanni. janye idanunsa yay ya maida ga Naziru yana faɗin, “Inaga tunda har an fahimci bakin zaren ayi haƙuri haka har zuwa lokacin da za'a sallameta daga nan ɗin insha ALLAH. Sai dai ya kamata ku sanar mata wacece ita a gareta dan na kula ba fahimtarku takeba kamar”. Sosai duk suka gamsu da bayaninsa, suka zazzauna aka shiga gaisuwa da tambayar jikin Zinneerah ɗin, wanda Khalipha ya ƙara musu bayani game da matsalar dake tare da ita akan buƙatar hutu bisa ga lalurar cikin jikinta. Sun shiga mata addu'ar fatan sauka lafiya. Maman Halima dai ce da har yanzu ke zaune a kusa da ita tana riƙe da hannunta ta nuna mata wadda aka kira maman Sadiq. “Zinneerah wannan ɗin mahaifiyarki ce, duk da nasan baki santaba kamanin dake a tsakaninku da duk bayan da mukeyi a wajennan zai tabbatar miki hakan, kai namasan zakiji a jikinki koda ba'a faɗaba dan mahaifiya tafi gaban wasa ai.” Kafeta da kallo kawai Zinneerah tayi tamkar wadda ta suma a zaune. Sai da Maman Halima ɗin taɗan taɓatane ta kawo numfashi, sai kuma ga hawaye sharr. Batare datace komaiba tai ƙasa da kanta, daga haka bata sake ɗagowa ta kalli kowa a cikinsuba. Sosai hakan da Zinneerah tayi ya taba zuciyar Maman Sadiq. Dan ta fahimci kamar Zinneerah ɗin fushi take da itane kokuma kalar nata murnar kenan oho. Kowa ma dake wajen da irin fahimtar da yayma shirun na Zinneerah. Murmushi Alhaji yayi, cike da sanin yakamata da hangen nesa irin na manya yace, “Kubata lokaci kamar yanda likitan nata ya faɗa ko”. Sai kuma ya juya ga Khalipha batare da ya jira amsarsuba. “Likita yaushene zaku sallameta?”. Murmushi Khalipha yayi yanaɗan sosa gefen goshinsa. “Alhaji banine likitanba dai, amma insha ALLAH zuwa nan da kwana biyar haka akoda yaushe za'a iya bata sallama tunda jikin nata yana ƙyau, dama matsalar kamar daga cikin jikintane yasa aka riƙeta”. “To masha ALLAH, ALLAH ya kaimu, ya kuma bata lafiya”. A tare suka amsa da amin. Daga haka sukai musu sallama domin tafiya badan Maman Sadiq tasoba. Sai dai taji daɗin abinda Maman Halima ta faɗa akan cewar itace zata dawo ta cigaba da jinyar Zinneerah ɗin har a sallameta. Kowama yaji daɗin hakan har Khalipha. ★★★ Tun daga wannan ranar jiyyar Zinneerah ya dawo hannun Maman Halima, Khalipha ma bai janye daga mata hidimaba, hakama Naziru, ga Alhaji ma ya ƙaru. Sai ga Zinneerah ta sake zama ƴar gata, sai dai abinda kebama kowa mamaki har yanzu taƙi barin damar da zasu fahimceta game da komanta. Hatta haɗuwarta da mahaifiyarta sun kasa gane mike a ranta. Dan taƙi cewa komai, ta kumaƙi nuna murnarta a fili ko damuwarta. A duk yanda Maman Halima ke janta a jiki dan son jin wani abu gameda rayuwarta da Inna taƙi sakin jiki da ita, duk da kuwa ta fahimci babu wata mummunar manufa ga Maman Halima ɗin. Sanin yakamatane kawai irin na matar. Tun daga ranar Maman Sadiq bata sake zuwa asibitinba, sai dai ranta fal yake da damuwar yanayin Zinneerah a kanta. Tadai danne ne kamar yanda mijin nasu ya bata shawara akan ai haƙuri da komai har Zinneerah ɗin ta dawo gida. Itakam Zinneerah bawai farin cikine batai da ganin Mahaifiyartaba. Har ranta ita kaɗai tasan daɗi da take a ciki, sai dai wani ɓangare na zuciyarta ya sakata jin ciwo da zargin mahaifiyar tata ta watsar da itane akan sani kenan. Dan duk wanda zai kalli Maman Sadiq ɗin yasan tana a cikin kwanciyar hankali a gidan aurenta na yanzu. A ganinta idan ba tana saneba yaya za'ai ta watsar da ita tsahon shekaru batare data taɓa waiwayar inda take ba, hakama danginta. Wannan dalilinne ya saka yin kamar batai farin cikiba. Sai dai a randa abin ya faru tasha kuka a ɓoye, still rashin ganin kuma Maman Sadiq bata sake zuwa asibitinba ma ya ƙara taɓa mata zuciya. Ana gobe za'a sallamesu Khalipha yazo mata da zancen da yasata tasha kuka sosai, dan har saida ta kaita da zazzaɓi mai zafin gaske. Ba komai yaja hakanba sai jin Khalipha ɗin zaiyi tafiya. Ashe dama yana karatune a wata ƙasa can daban, hutu yazoyi gida shine yake ɗan zuwa nan asibitin yana rage zaman banza saboda asibitin nada alaƙa da shi. Yanzu kuma hutunsa ya ƙare, yaso ace sai an sallami Zinneerah yaji cikakken labarinta sannan. Amma sai Yayansu yaƙi saurarensa da ɗaga masa ƙafar ƙarin kwana ukun daya buƙata. Ya tabbatar masa da dole-dole saiya koma makaranta gobe idan ALLAH ya kaimu. Shiko a duniya baya taɓa iya ƙetare maganar Yayan nasu saboda ƙauna da girmamansan da sukeyi akaf gidansu koma yace family ɗinsu. Kuɗaɗe masu yawa da sayayya yayma Zinneerah ya kawo mata cike da damuwa. Bayan ya mata nasiha akan yanda zata kula da kanta yace ta bashi lambar mijinta koda ya tafine zai nemsa suyi magana ta waya. Shiru Zinneerah bata iya cemasa komaiba akan wannan magana. Ya sake mainaita mata, nanma shiru tai sai hawaye dake gudu a kumatunta. Ƙyaleta Khalipha yayi, dan a tashi fahimtar kawai ta bashi cewar Zinneerah kodai rabuwa tai da mijin nata kokuma bata buƙatar ana alaƙantata da shi bisa wani dalili na ɓacin rai. Dan haka ya ƙyaleta kawai saboda ya amsa lambar Naziru. koma miye zai dinga ji daga garesa kawai. Haka dai Khalipha yay mata sallama ya wuce ya batta da kukan zuci. Dan hatta Maman Halima da bata daɗe da saninsaba yaron da halayensa sun sakashi shiga ranta sosai. Dalilin tafiyar Khalipha gaba ɗaya yinin ranar a rashin daɗin rai Zinneerah tayisa a asibitin, harma tanaji ta ƙagara a sallamesu gobe idan ALLAH ya kaimun, gara taje gidan maman tata taji nata dalilin itama na guje mata datai ta barta cikin wahalar rayuwa.. Haka dai a daddafe suka kai washe gari, inda ALLAH ya taimakesu aka basu sallama tunda safe. Dan haka Nasiru yazo ya kwashesu dan yakai gidan yayan nasa inda mahaifiyar Zinneerah ke rayuwa a yanzu matsayin gidan aurenta..............✍ *_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182