Chapter 160
Chapter 160
sukazo har gida batun kamani. Wallahi tallahi ALLAH shine shaidata wannan shine abinda nima na sani, dan ALLAH ku gafarceni na tuba”. Ta kare maganar tana share hawaye. Gaba ɗaya falon ya ɗauka salati ana duban Zakiyya da tai ƙasa da kanta, daka ganta kasan a firgice take matuƙa. Hakama Mammah a ruɗan take amma duk tasan itama akwai sunanta a ciki so take taji ta bakin Zakiyya game da cikin Zinneerah da ita dai harga UBANGIJI batasan da zamansaba. Zinneerah kam mutuwar zaune tayi tanabin kowa da kallo kawai tamkar butun-butumi, dan harga ALLAH suna neman rikitar mata da tunani. Ita kanta burinta kawai aunty Zakiyya tayi magana. Mai martaba da zuciyarsa har wani tafasa take ya kafe Zakiyya da kallo yana kuma duban Farah dake kuka itama wiwi. A zafafe yace, “To dan uban daya haiheki sai kimana bayani muji lalatacciyar yarinya kawai. Wannan wane irin kafurcine kuma daga ina kika samosa ko kuka samosa tunda dai babu yanda za'ai dashe masu ƙwai basu saniba. Shi ƙwan na wanene? Kuma yaya akai?”. Ƙasa ta zamo ta dirƙushe jikinta na rawa, dan tafi kowa sanin wanene mahaifinsu. Inhar kuma tai gigin faɗar abinda ba haka bane lallai zai mata abinda gwamma ta faɗi gaskiyar. Kafin tace komai Farah da tsoro ke neman gigitata na tsawar mahaifin nasu ta fara rawar jiki da faɗin, “Wlhy Abbah babu ruwana nidai, duk aunty Zakiyya ce ta tsara komai, itace tasa muyi wlhy badan inaso ba......” Hankali tashe itama Zakiyyan ta fara magana, “Dan girman ALLAH Abbah ka gafarceni. dan ALLAH kar kayi fushi dani, Baba wambai ka bashi haƙuri dan ALLAH”. Aminin mai martaba da suke kira da baba Wambai ya gyara zamansa cikin kasaitar mulki da dattako yace, “Zakiyya kafin azo ga neman gafara ai nakega ya dace musan yaya akai ko? Kinsan mai martaba bayason jayayya, dan haka ki buɗe baki kiyi bayani tamkar yanda suma waɗanan mata sukayi, inaga shine zaifi sauƙi kamar kafin muzo ga gaɓar da kike so”. Kanta ta jinjina masa tana sharce hawaye. “Kowa yasan Farah dai autarmu ce da tausayinta yasa duk muka ɗauka son duniya muka aza mata, musamman ma ni daya kasance itace kawai ƴar uwata mace, sauran ukun duk maza ne. Farah a Morocco ta rayu hannun kakarmu data baro london, bayan rasuwarta Mammah yayar mahaifiyarmu ta amsheta ta koma da ita london. Tausayin da kowa yakema Farah a cikin dangi shi Abdul-Mutallab ke mata shima. Hakan yasa yafi kowa nuna jin daɗinsa da komawar Farah garesu. Kamar yanda take samun gata daga Mammah haka shima take samu a garesa, ta sanadin hakan shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakaninsu, daga karshema ta juye soyayya. Kowa yaji daɗin hakan a dangi, dan babu wani ja'inja aka yanke zancen aurensu. Bayan bikin su da kusan shekar biyu babu wani labari koda na ɓatan wata daga wajensu, babu kuma wanda ya damu da hakan sai ni dana farajin damuwa. A wani zuwa da tayi Nigeria na takura mata mukaje Doctor ya dubata, inda mukaci karo da mummunan labarin daya nema zautani, dan ita koma a jikinta saboda ƙuruciya na ɗawainiya da ita a lokacin. Doctor ya tabbatar mana akwai wani tsiro daya toshe bakin mahaifar Farah gaba ɗayanta. Yanda da wahala ace ciki ya shiga, kodama ya shigan bazai zaunaba. Na bukaci ai mata aiki a ciresa idan zai yuwu, sai ya tabbatar mana taɓashi babbar matsalace, dan zata iya rasa ranta, sannan basu da wani maganin da zai iya gusar da shi a yanzu haka dai. Naci kuka sosai na kuma shiga damuwa da tunanin neman mafita ma yar uwata. Da farko dai son ganin jinin autarmu yasani damuwar, amma dalilin shigowar wasu maƙudan kuɗi ga Abdul-Mutallab da zantukan danginsa na ya ƙara aure ya far canja alkiblar tunanina, zuciyata ta fara rayamin idanfa ƴar uwata ta haihu da shi komi ya tara mallakintane ita da ɗiyanta. Idan kuma nayi sakacin hakan suka aura masa wata akwai matsala tunda likita ya tabbatar mana akwai matsala game da mahaifarta ita. Wannan tunanin ya sani ɗaukarta a wani zuwa london da nayi muka fara bin likitoci ba tare da sanin Abdul-Mutallab kosu Mammah ba. Sai dai duk inda mukaje amsar dayace mahaifarta nada matsala, kuma irin bayanin wancan likitan suma suke mana dai. Hankalina ya ƙara tashi haka itama nata, dan haushin rashin damuwarta yasani zama na fahimtar da ita. Nasha takaici ganin daga baya ta nuna ita fa ba komai bane, tunda Abdul-Mutallab na sonta tana sonshi ko bata haihuba babu damuwa, ballema bata fidda ran a gaba su samuba dan bata yarda da maganar likitocinba ALLAH ne maiyi. Duk da gatan da mukema Farah na tsiya nasan tanada zurfin tunani da aiki da hankalinta matuƙa, sai dai banyi zaton zata kasa fahimtataba musamman dana san tanada kishi mai zafi irin namu musamman akan Abdul-Mutallab. Lokacin da suke cika shekaru uku da aure kakarsa ta ƙara bijiro masa da zancen aure a time ɗin sunzo Nigeria tare, hankalin Fara ya tashi matuƙa, dan tanada tsananin kishi”...........✍ *_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇 0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* _________________________ *Page 63* ............“A wannan gaɓar saboda yanda ta nuna tashin hankalinta matuƙa sai nayi amfani da damar wajen sake zaunar da ita na nuna mata muhimmanci haihuwarta. Tare da kawo mata zancen dashen ciki. Ta razana matuƙa, ta kuma ce ita dai gaskiya tanajin tsoro, dan tasan Abdul-Mutallab ma ba yarda zaiba. Dan haka kawai mubar zancen na tayata da addu'a dan bazata iya zama da kishiya ba zata iya halaka kanta. Wannan furuci nata ya kuma ɗagan hankali matuƙa, dan nasan zata iya aikata abinda ta faɗan, na kuma tabbatar auren Abdul-Mutallab bazai fasu ba inba danginsa sunga ta haihu ba. Ta kuma nunamin su Mammah ma ba yarda zasuyiba dan abune da kowa yasan malamai na nuna illarsa a addinance dama lafiya ta wani fannin. Ban gusaba wajen zaman cigaba da nusar da ita, tare da kawo mata dabarun da zamuyi maganin kowacce matsala. Na farko karmu bari AK ya sani, ayi komai a ɓoye harta wadda za'a sama cikin ta haihu ace itace ta haihu. Ta tambayeni taya za'ai hakan ta kasance bayan koyaushe tana tare da AK. Na ce mata ta bari zanyi tunani. Bayan kwana biyu dayin maganar na samo
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182