Chapter 171
Chapter 171
zuwa duba Inna kafin a shiga hidimar bikin amma AK ya hana, acewarsa ta bari a gama biki sai suje dan akwai maganar Dr Mahmud ma da Sa'a a ƙasa. Kamar yanda ya umarceta da haƙurin haka ta haƙura aka shiga shagalin bikin su Abidah da aka shiryama bidi'oi kala-kala, danma AK ya zaftare wasu a ciki yanata faɗa. Ranar ɗaurin aure a bazata sai ga sunan Khalipha a cikin anguna. An zarga masa igiya uku da ɗiyar Uncle Ahmad Raheenat (Noor). Kowa kam yayi farin ciki da wannan haɗi musamman ma Uncle Ahmad. Shima dai ango da gaske yanaso dan ƙiri-ƙiri ya nuna farin cikinsa. Abin sauƙin ma shima yanada gidansa dama da yake gini, ƴan abubuwane kawai suka rage a ƙarasa dan haka aka hau sauran aiki babuji babu gani. Matar Uncle Ahmad tayi baƙin cikin wannan haɗi itakam, sai dai babu yanda zatai dole ta haƙura. Dan dama taƙi sakin jiki da matan gidan sam. Suko da yake ba kanwar lasa bane duk sai suka watsar da ita suma suka cigaba da sabgogin gabansu. A bikin nan dauriya kawai Zinneerah keyi dan batajin daɗin jikinta, hayaniyarma sam bataso, shiyyasa lokuta da dama zaka sameta can gefe a killace. Hakan sai yayma AK daɗi dan bata halarci bidi'a ko daya ba da akai garama kamu da akayi anan cikin gidan. Ana saka kiɗa kuwa sai da tabar gidan saboda ciwon kai mai tsanani. Can gidansu ta koma tai kwanciyarta ta hutama ranta. Ansha shagalin biki harna kwanaki uku aka miƙa amare ɗakinsu. Adilah lagos, Safiyya Abuja. Sauran kuma Ni'ima da Abidah duk anan kano ne, sai Noor da aka bari sai nan da kwanaki uku an kammala aikin gidan Khalipha. (To amare da angwaye ALLAH ya sanya albarka ya kawo ƴan dugwi-dugwi iyalan baba). Washe garin da aka shashshare daga bikin nan kuma aka kai kuɗin auren Sa'a danya. Inda baƙi suka sami tarba ta mutunci da girmamawa. Inna ga dama ta samu amma babu halin damawa, sai hawayen zuci takeyi. Dan tuni aka maidota gida. Sai dai a duk sanda ta kalli Tinene da tsohon ciki ranar sai ciwonta ya rikice. Hakan yasa suka yanke shawarar maida Tinene gidan Gwaggo laritu harta haihu, dan an ajiye magana randa ta haihu za'a ɗaura mata aure damai cikin tunda ya amsa nasane. Daga kai kuɗi baba yace shikam dai baimaga wani abun jeka ka dawo ba a ɗaura aure kawai a huta. Zuwa wani satin ta tare ɗakinta taje tai haƙuri tamkar kowa. Hakan yama Dr Mahmud daɗi, hakama su Baffah da suka kai kuɗin. Nanko take aka zarge igiya uku tsakanin Sa'adatu Sulaiman Danya da Dr Mahmud Dawood. Zokaga baki wajen ango. Aiko AK ya dinga masa sherin kurame yana ramawa shima kamar yanda yay masa. Dan bazai fito kai tsaye yay maganaba sai dai yayi a fisge ya tsuke baki cikin basarwa tamkar bashine yayi ba. Cike da farin ciki suka dawo kano da wannan labari, Zinneerah kam tafi kowa murnar wannan al'amari dan har kukan daɗi tayi. Cikin amincin ALLAH sati na zagayowa akai tariyar Sa'a. sai dai Zinneerah bataje Danya ba dan batajin daɗin jikinta kam, Khalipha ma tasa amaryar ta tare a nasa gida da aka kammala. Yanzu kam sai dai mu cigaba dabin kowa da fatan alkairi. Tun bayan tariyar Sa'a komai ya sake lafawa, Khalipha ya koma London shi kaɗai domin karasa karatunsa. Zinneerah ma cikin ƙarfin hali AK ya sata zana exam na November/December. Tasha wahala saboda laulayin dake damunta, amma babu laifi tayi ƙoƙari Alhmdllh, sai fata da addu'ar fitowar ƙyaƙyƙyawan result. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya Zinneerah na rainon cikinta dake ƙara fitowa yana wahal da ita, duk ta rame sai haske data ƙara kam masha ALLAH. Yanda wahalar tai mata yawa ne ga aikin gida ga little ya fara makaranta, dan yanzu yafi zama anan fiye da ko ina, yawonsa sai weekend, ga gida shiru ita kaɗai yasa Hajiya iya cemasa ya maidota nan gidan sai ta haihu. Babu wani ɓoye-ɓoye ya ɓata ransa. Dan shi dai yafison su cigaba da lallaɓawa a hakan har ALLAH ya sauketa lafiya. Tunda dai bawai kwance take rijif ba. Aikin gida da lalurarsa girki da sauransu duk tanayi. Fitace kawai bata cika sonyi ba dan wahala take sha sosai koda kuwa zuwa gidan su Granny ne kawai tayi ko gidan mmn sadiq. Shiyyasama ta tattara kowanne yawo ta ajiye. “Ikon ALLAH, wai ka cika baki da iska! Bazaka maidotan bane komi kake nufi moddibo?”. Shiru yay mata kamar bazai tanka ba, sai da yaja wasu sakanni ya dubeta yana ajiye wayar hannunsa. “Granny ki fahimta mana dan ALLAH, taya yarinya na gidan mijinta ace ta taso ta baro. Wazai kula damu ni da Abdul-Mutallab to?”. “Owoo, sai ta zauna zaman kula da ku ita kuma ta kashe kanta. Kana ganin yanda duk jikinta ya koma ko abincin kirki bataci sai yame-yame”. “Granny duk nasan da waɗanan matsalolin kuma suna damuna wlhy nima, ina kuma yin iya bakin ƙoƙarina na ganin na bata kulawa nima, kuma Alhmdllh jikin natama ya fara sauƙi. Kawai dai idan kin yarda a samo wata ta zauna da ita ni ko nawane zan biya. Kokuma ke ki koma can dan ALLAH ”. “Wa? Kama kanka. Kawai sai naje ƙososo na zauna muku a gida raba kanka malam”. Murmushi yayi a ransa yana faɗin, ‘Ai wlhy ke zan lallaɓa kije madam, nasan maganinki ai’. A fili kam sai yay mata shiru, daga ƙarshe ma ya miƙe yana faɗin, “Bara naje na ɗauka Abdul-Mutallab a makaranta”. “ALLAH ya kiyaye ka gaishesu”. Zinneerah na falon farko na sashenta a kwance cikin kujera barci ya ɗan fara figarta daga charting dasu Meenal suka shigo. Kamar yanda Little ya saba duk da kuwa yanzu ya ƙara girma da wayo ga shegen miskilanci kamar sunyi kaki sun ajiye ya nufeta da gudu. Yana ƙoƙarin faɗa mata a jiki AK ya ɗagashi sama dan yanayinta ya nuna masa batajin daɗin jikin. Kuma lafiya lau ya fita ya barta. Itama ajiyar zuciya ta sauke ganin ya hana little ɗin faɗa mata a jiki. Ta yunƙura ta tashi zaune tana musu sannu da zuwa. Amsawa yay idonsa a kanta yana kaiwa zaune kusa da ita little a jikinsa. “Jikin ne kuma?”. Fuska Zinneerah taɗan yamutse tana kamo hannun little ɗin. “Kawai dai banajin ƙarfi ne amma babu inda kemin ciwo, garama tashin zuciya daketa damuna tun cin kifin nan na jiya da naci”. Tausayintane ya sake kamashi, musamman daya tuna yanda taita damunsa da maganar kifin. harma ya dawo gida jiya da nufin bazai sake fitaba ta takura sai da ya fita kusan goma na dare ya nemo mata kifin, gashi kuma taci ta kasa zaman lafiya. “Sannu ALLAH yay miki albarka ya saukeki lafiya. Bara na taɓa Mahmud naji kozaki iya shan wani abu dazai baki nutsuwa”. “Yayanmu kama barshi zai bari dan kansa. Dan nayi waya da Yaya gajeje tace na samu ɗan kanwa kaɗan nasa a ruwa na sha zai faɗa min”. Kafin yace wani abu little da yay kamar ba saurarensu yakeba yace, “Aunty sorry, idan kika haifa mana babynmu zan kaiki makka”. Dariya zancen nasa ya basu, dan haka suka murmusa AK na shafa kansa. “ALLAH ya tabbatar ɗan albarka.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182