Chapter 83
Chapter 83
gidan take zaune tun bayan rasuwar mijinta acan Morocco. Takaicin halin Farah yasa taƙi tambayarta miya kawota gidan har sai safiyar yau. Bayan ta idar da sallar asuba ta sami Farah a ɗakin nasu itama ta idar da sallan tana karatun Al-Qur'ani. Zama tai a bakin gado tana kallon ɗiyar ƙanwar tasu da gata ya maidata kamar wata shashasha. Tabbas ta yarda da maganar hausawa da sukance gata mugun ciwo. Dan kuwa shine yayma Farah katutu har bata banbance fari da baƙi a cikin al'amuranta. Sai da Farah takai aya sannan ta rufe Al-Qur'anin tana duban Mahma. Cike da girmamawa da shagwaɓanta ta gaidata kamar yanda ta saba. Mahma dake dubanta da kulawa itama tace, “Miya faru kikazo nan kika kwana auta?”. Baki Farah ta tura gaba idanunta na cika da ƙwalla. Kanta tsaye cike da gadaranta tace, “Mahma na baro masa gidanne su zauna shi da dangin nasa”. “Kimin magana a warware zanfi fahimta fiye da bani ita a dunƙule. Ko kina nufin har yanzu matsalar zuwan Kakar tasane bai kareba kuma?”. “Ni bashi bane Mahma, ai nace dai na haƙura wannan, amma yanzu dan tsabar wulaƙanci shine ya ƙara kwaso min ƙannensa da wata yarinya da bansanma miye alaƙarsuba aka kawo batare da ya sanar min zuwansuba”. “Humm” Mahma ta faɗa tana murmushi da girgiza kanta. Sai da ta gama yima Farah kallon nazari na kusan sakkani arba'in kafin ta gyara zamanta da ƙyau. “Farah anya kuwa kinsan mikikeyi? Gaki dai mace mai tarin ilimin addini dana boko, wayayya wadda ALLAH yayma baiwa kala-kala da ni'imomi, sai dai kuma shashasha ce. Wai sai yaushe zaki daina biyema Hindatu da Zakiyya ne? Farah kinsan ko muhimmancin nuna darajar dangin miji da mutuntasu ga miji kuwa? Kodan kina ganin kullum Hindatu na aibanta dangin Abdul-Mutallab shiyyasa kike ganinsu kamar marasa daraja a idanunki? Bara na faɗa miki gaskiya idan zaki ɗauka. Hindatu mahaifiyarsa ce, zai iya jurewa ya shanye yakumayi haƙuri akan duk wani tarkace da zata jingina danginsa da shi koda yanajin zafin hakan. Keko matarsace duk da kina ganinku jini ɗaya da kuma fawar da kike samu ga mahaifiyarsa zai iya ajiyeku akansu wlhy. Shin bazaki godema ALLAH da ni'inar da yay miki na samun miji irin Abdul-Mutallab mai kawaici da haƙuri ba. Dan wlhy na tabbatar badan soyayyar da yake miki ko tirsasawar hindatu a garesaba yake ƙyaleki. Haƙurinsa da sanin ya kamatansane kawai ke rinjayarsa wajen baki uziri kafin ki kaisa bangon da bazai iya jurewaba. Idan kuma kikai wasa zakiyi nadama a lokacin da guri ya ƙure miki ki kuma rasa samu damar gyara komai. Saboda zuwan wannan yaran kawai ya isa nuna miki gudin halinki yasa ya guji ya faɗa miki ki sanarma mahaifiyarsa ta hanashi, kinga kuwa sai ki dawo hankalinki da irin masu halinki dan mata da yawa sunada wannan bazan halin shiyyasa da yawa duk son da mazansu ke musu sai kiga yana raguwa harsu fara tunanin ƙaro musu abokiyar zama koda kuwa babu haka a tsarinsu. Ni nasan babu wani ilimin zama da miji da baki dashi Farah. Dan kuwa idan da dama ma sai dai ki koyar da wasu. Amma tun zuwan ƙaninsa gidanku kin watsar da komai na ingatacciyar rayuwar aurenku. Kin maida hankalinki wajen kawo ƙararsa kullum da kushe danginsa da nuna ƙyamatar su kusancesa. Anya baƙya tunanin cewa akwai matsala? Baƙya tunanin hankalinsa zai iya fara karkata bisaga ƙudirin dangin nasa nason ƙara aurensa. Yanzufa cikine dake, amma ki duba ko'a jikinsa. Yanda ya nuna murnarsa da farin cikinsa akan wancan cikin da kika samu ya zube bai nunaba akan wannan. Banama tunanin ya sanar da kowa a cikin dangin nasa, tunda dama wancan karon hanashi faɗa musu kukayi wai sai dai suji kin haihu. Sai gashi baki haihunba kuma sabida ALLAH ya rubuta cikin ba zaunanne baneba. Wlhy ki dawo hayyacinki, ki dawo da ingattacciyar rayuwar aurenki kamar farko domin cigaba da damƙe zuciyar mijinki. Duk wannan gantali da shirmen naki babu inda zai kaiki sai komawa baya a garesa. Dan kullum sabbin halayyarki dusashe taurarenki yakeyi a wajensa. Ki dinga daurewa wajen danne wannan zafin kishin naki da kika gada kodan tsare martabarki. Wlhy duk yanda kuke zaton kunada kishi na damaku na shanye. Amma tunda nai haƙurin zama da kishiyoyi har biyu a lokacin rayuwar aurena ya kamata kuma ku saduda. Dan rayuwarma nawa takene baki ɗaya. Daga randa UBANGIJI ya bukaci ganinka dole ka amsa kiransa koka shirya kobaka shiryaba. Duk wata dukiyarka da suna da ilimi da mulki da nasaba da koma miye da kake takama dasu bazasu amfanar dakai da komaiba sai ƙyawawan halayenka da ibadarka. Dan haka sai kisan inda ke miki ƙaiƙayi kibar wannan shirman da kika ɗakko mara hanyar ɓillewa ki koma Farah ɗinki dana sani ada mai hankali da sanin yakamata akan rayuwar aurenta. Ki kuma tashi ki shirya ki koma gidan mijinki tunkan ya fahimci kinbar gidan. Ki kuma kama kanki akan zaman dangin nasa. Ki kiyayi yawan kawo kararsa dan kina zubar masa da kimarsa a idanunmu alhalinsa dan kece sheɗaniyar. Dan wlhy idan Hindatu ta dawo naji kin kira wayarta akan wata matsalar danginsa da kaina zan saka Abdul-Mutallab ya ƙara aure......” Da sauri Farah ta ɗago ta duba Mahma idanunta na kawo hawaye. Mahma tace, “Kalleni da ƙyau da gaske nakeyi, dan ko ita Hindatun sai dai tazama ƴar kallo bareke da kike matsayin ƴa. Idan zakije ki kama kanki kije ki kamasa kafin na saitaki a layin daya dace da ke tunda ke shashash ce. shin gata haukane ma kenan?”. Cikin kuka Farah tace, “To amma Mahma shima idan yazo kimasa faɗa ya daina min ihu banaso. Sannan ya daina nunamin kamar danginsa sun fini a wajensa tunda nima dai ƴar uwarsace kuma jininsa mafi kusanci”. “Naji zan masa. Amma sai naga gyara daga gareki sannan.” “Insha ALLAH zan gyara, kuma zanyi duk yanda kikace”. A karan farko Mahma tai murmushi da kamo hanunta jikinta. Tace, “Yauwa kokefa ƴar albarka. Amma duk kin wani susuata kanki tamkar wata shashasha wadda batasan ciwon kantaba da mutuncinta. Karki sake kiyi saken da Abdul-Mutallab zai kufcemiki dan zaki dawwama a dana sani har ƙarshen rayuwarki kuwa”. Kanta ta jinjinama Mahma cike dajin daɗin nasiharta tana kwantar da kanta a bisa cinyarta. Sake kwantar da murya Mahma tayi ta lallasheta sosai da ƙara mata shawarwari sannan ta sakata tai wanka ta shirya, ko breakfast batai zamanyiba ta kamo hanyar dawowa gida zuciyarta fal tsare-tsaren dawowa da martabar aurenta daga yau kamar yanda take ada kafin zuwan Khalipha daya susutata saboda rashin son ganin dangin AK raɓe dashi bisa huɗubar Mammah............✍ *_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182