Chapter 150
Chapter 150
yay yana maida kansa gefe da faɗin, “Ku kwantar da hankalinku ba wani abu bane, na saku zuwa nanne domin ku zama na farko dazan fara tabbatarmawa kafin kowama ya sani”. Hajiya iya dake cikin jimamai tace, “To muna saurarenka, ALLAH ya jishemu alkairi”. Da amin Mahma da Gwaggo Maryama suka amsa. AK ya gyara zamansa kansa a ƙasa dan nauyin maganar da zaiyi. “Kuyi haƙuri duk da ba magana bace wadda ya kamata kusani, amma saboda wasu dalilai naga ya dace ku sani ku kuma zama hujja akan binciken da zan ƙarasa. Mu dukanmu nan munsan cewar Zinneerah ta haihu a shekarun baya, kuma koda yaushe maganarta shine batasan a inda ta samo ciki ba. Wasu kan ɗauketa mara hankali, wasu na ganin tana wasa da hankalin mutanene kawai ko rainin wayo da makamantan haka. Wasu kuma kan mata uziri da cewar ƙaddara ce ta afka mata. Tabbas ƙaddara ce, da a zahirance zamu iya kiranta *_MAKAUNIYAR ƘADDARA_*. ALLAH shine shaidata ban taɓa taɓa ƴar kowa ba da nufin fasiƙanci. hakkane ya tada hankalina matuƙa akan Zinneerah har takai bana iya barci, a ƴan kwanakin nan gaba ɗaya cikin shan maganin hawan jini nake saboda tashin hankali da tunanin ta hanyar da aka samar da Abdul-Mutallab, sai da Granny ta kawo wani zance da Khalipha yayi akan dashen ciki sannan ALLAH ya haskamin hanya. A dalilin haka na cigaba da bibiyar abubuwa da dama a ɓoye batare da sanin kowaba, har ALLAH ya tabbatar a yau nakai gaɓar da nine na farko da zan fara tabbatarma duniya lallai dashen cikin Abdul-Mutallab akaima Zinneerah bata hanyar banza ta samoshi ba. Dan bata taɓa tarayya da namiji ba sai daren jiya. Inaji a raina ALLAH ya keɓance tane daga haihuwa da kanta sai cs akai mata domin irin wannan ranar dazai wanketa ga kowa”. Kallon kallo aka shigayi tsakani Mahma da Granny da Gwaggo Maryama, shi dai AK tunda ya fara bayaninsa harya ƙare bai yarda ya kallesu ba idanunsa a ƙasa. Cikin karfin hali Mahma ta katse tararrabin su ta hanyar kallon AK da faɗin, “Abdul-Mutallab ka sakamu a duhu nikam, kenan tayaya aka dasama baiwar ALLAH nan gudan jininka?”. “Wannan ne nakeson sani yanzun, amma Mahma kiyi haƙuri, inaga wannan abin ba kowa bane ya ƙullasa sai Zakiyya, Farah da Mammah, dan naji wasu zantuka nasu da suka rikitani jiya da rana sanda nazo gidan nan, to kafin na shigo na fara samunsu a garden ne amma su basu san na jiba. Sannan idan kin lura duk sanda akai maganar dashen cikin nan sai sun razana. Dalilina na biyu Dr Mahmud ya tabbatar min shi baiga wani alamun mai ciki tattare da Farah ba. Sannan ni kaina idan zanyi aiki da hankalina ai ciki girma yakeyi a jikin mace, amma ace kusan 5months babu wani alamarsa a jikin Farah. Idan baki mantaba cikin farko data samu tun yana wata uku suka matsa sai da ta tafi Morocco, bata dawo London ba sai da tai ɓari kamar yanda suka faɗa. To wannan ma a ƙiyasina tun yana wattani ukun ta shiga damuna zataje, amma zuwan danai da Granny ya sani taka mata birki. Hujja ta biyu a labarin da Zinneerah ta bamu na zuwanta katsina aikatau yayi kama da wadda aka yaudara saboda ƙuruciyarta, bayan an cutar da itane ta gudo batare da saninsu ba. Abinda kawai ban fahimtaba anan shine Mammah tasan hakan kokuwa ita Zakiyya da Farah ne kawai suka sani ko itama Farah bata sani ba? Hujjata ta ƙarshe samun Zinneerah da martabarta ta ƴa mace”. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Mahma dasu Granny keta ambata, hawaye suka shiga sakkoma Mahma, tasa hannu ta sharesu da faɗin, “Lallai biri zai iyayin kama da mutum Abdul-Mutallab, dan nima kaina ina mamakin rashin tasawar cikin Farah. Sannan akwai wasu abubuwa na rashin gaskiya da zakaga suna shan aikatawa a wani lokaci kuma, lokacin cikin farko na taɓajin wata wayarta da Adilah lokacin tana hostel a makaranta, sai dai ina shiga ta yanke wayar. Indai kuwa hakane sun cutar da yarinyar nan matuƙa, sun ɓata mata suna, sun sakata wahala da ƙarancin shekaru. Wane irin son zuciya ne wannan? Kai kanka damu sun cutar ai”. Ta kare maganar tana kuka sosai. Gwaggo Maryama ma hawaye takeyi, Granny dai idanunta sunyi matuƙar yin jajur alamar shiga ƙololuwar ɓacin rai. taja numfashi mai zafi da faɗin, “Lallai kayi haƙuri Moddibo, idan har ta kasance wannan zancen ya zama gaskiya sai nayi shari'a da uwarka da matarka. Dan wlhy sai na bima inno kadin haƙƙinta. Yanzu abinda nakeso da kai kar kai musu maganar komai, kuma tabbas inaga Zakiyya itace hajiyar da aka kai Inno gidanta. To karka yarda su haɗu anan gidan yanzun, dan idan suka gane itace zasu iya bin wata hanyar suga sun rufe asirinsu. Abinda nakeso dakai yanzu daganan zuwa safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu ka aika hukuma a kama matar data kai Zinneerah aikatau katsina, itace zata kaimu ga hajiyar farko, ita kuma ta kaimu wajen wadda Zinneerah ta faɗa mana tata jerangiya da ita asibiti, na tabbatar zamu kamo bakin zaren insha ALLAHU.” Duk da kalaman cewar sai tayi shari'a dasu Mammah ya bashi tsoro dan yasan Granny akan tsayawa wanda aka zalinta hakan bai hanashi ɗaga mata kai ba cikin girmamawa yace, “An gama insha ALLAH, dan yanzu hakama zancen da nake miki tana police station tare da Khalipha. Tun da safe yaje Dayan akanta, ya tatar tana katsina, shine ya zarce can har inda take bisa taimakon wani bawan ALLAH ɗan nan Danya ɗin. Dan da nace a fara kamamin matar baba sai Khalipha ya bani haƙuri akan a barta kodan darajarsa dan yama tarar itama bata da lafiya. Mu kama matar dai kawai tunda ta hanyartane kawai za'a iya bin diddigin abun”. Mahma tace, “Alhmdllh hakan da kukai shine dai-dai, yanzu yaya akai mi matar tace?”. “Mahma ba'akai ga tambayarta komai ba, dan inaga ko mintuna goma basuyi da isowaba ma, ina gama waya daku ya kirani yake sanarmin ya dawo harda matarma tana station yanzu haka”. Gwaggo Maryama dai ta kasa tofa komai, sai hawaye taketa faman zirararwa. Hajiya iya tace, “Kabeer ya san duk wannan?”. “A'a ban faɗa masa ba”. “To ya kamata ya sani dagashi har Ahmad da Abubakar (Abba mijin maman sadiq) da baban ita Zinneerah, dan babbar maganace wannan data wuce yinta iya mu kaɗai”. “Babu damuwa Granny, dama ai dole zasu sani, dama munason mu kammala gano inda mutanen suke tukkuna sai na sanar dasu. Amma tunda kinga ya dace su sani tun yanzu shikenan”. Mammah ta buɗe baki zatai magana kenan sai ga Zinneerah ta fito tana tafiya a hankali batare da tasan da zamansu a falonba. Ita cama take AK ɗin baya gidan, dan tun ɗazu ta tashi, cikin ƙarfin hali ta gyara masa ɗakin da wanke toilet, yanzuma ta fito ɗaukar kayan sharane. Tun fitowarta ƙamshin turarenta ya isar masa hanci, dan haka ya waiwayo domin tabbatarwa. sai dai yayi dai-dai da suma duk suka ganta ɗin. Sai dai babu wanda ya iya cewa komai a cikinsu harta iso kusan tsakkiyar falon, turus taja ta tsaya gabanta na faɗuwa ganin yanda suke mata kallon ƙurulla su duka. Sai duk ta daburce dan gani take kamar duk
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182