Chapter 28
Chapter 28
saukeku lafiya. Mikikeso na sayo miki idan zan dawo?”. Ƙasa Zinneerah ta karayi da kanta cike da girmamawa da ƙaunar wannan bawan ALLAH. Shima sai ya miƙe yana murmushi, “Shikenan tunda kin kasa faɗa, kafin dai na taso ki faɗama mamanki saita kirani a saya miki komi kikeso ɗin”. “Nagode Abba, ALLAH ya tsare ya bada sa'a”. Murmushi ya sakeyi cike dajin son yarinyar a ransa. Ya amsa idonsa akan matarsa. ___________________★ Tun daga wannan ranar babu wanda ya sakema Zinneerah magana akan sanin uban cikin jikinta da dalilin barowarta gida. saima kulawa ta musamman da Maman Sadiq, Abba, Maman Halima suka sake ninka mata. Koyaya aka ganta a damuwa sai anbi ba'asinta domin son kauda mata. Duk da Maman Sadiq na kawaici a kanta cikin hikima take jan abarta a jiki idan sun shige ɗaki, hakan yasa shaƙuwa mai ƙarfu ke sake shiga tsakaninsu, tana sake sakin jikinta sosai kuma. hakama ƙannenta idan ka gansu saika ɗauka dama can tare suka tashi. A wajen ƴaƴan Maman Sakina (Saude) ne kawai Zinneerah batajin daɗi da ita kanta Sauden. Dan ko ranar girkinta bacin Maman Sadiq nakai zuciya nesa da sun dinga tafka rigima akan abincin da ake zubama Zinneerah ɗin. Amma sai bata cewa komai ta barta da halinta. Tadai gargaɗi Zinneerah ɗin akan koda wasa karta shiga hurimin Maman Sakina da ƴaƴanta inhar ya wuce gaisuwa da girmamawa. Sannan duk wanda zai sakata aiki a gidan tai masa indai ya girmeta. Dayake Zinneerah ɗinma bamai kwaramniya bace sai tabi huɗubar mahaifiyarta aka zauna lafiya. Dan duk da cikin dake tare da ita da gadara Maman Sakina ke sakata aiki a gidan, itako babu musu takeyi koda batajin daɗin jikinta. Saima idan Maman Halima taga abin yayi yawane takanyi magana kota hana Zinneerah ɗin. Haka yakan saka Maman Sakina taita masifa a gidan da gori tana kiran Zinneerah da suna agola kinfi masu gida. Maman Sadiq bata taɓa tankawaba, bakuma ta taɓa gayama mai gidanba. Ta kuma roƙi Maman Halima akan karta faɗa itama, dan tasan duk dai iya zaman Zinneerah a gidan naɗan lokacine kafin ta koma gidan mijinta. Haka kwanaki suka cigaba da shuɗawa Zinneerah na rainon cikinta dake bata wahala. dan bata taɓa ƙulla kwana biyu babu ciwo. Sai dai yanda cikin ya fito ɗas a jikinta ba ƙaramin ƙyau yasa tayi ba. Gashi tana samun kulawa sosai yanzun. Dan hatta da zuwanta asibiti Naziru ke zuwa ya kaita kamar yanda Khalipha ya bar masa sallaho. A ranar farko da suka fara komawa asibitin domin ganin likita Zinneerah ta samu damar ƙare masa kallon tsaf bayan ta karanta sunan asibitin tun daga waje. *_SHIRA HOSPITAL_*. Sosai take jinjina ƙoƙarin maginin wannan asibiti, dan yayi ƙyau sosai kuma an zuba masa kayan aiki bana ƙaramin kuɗiba. Ga likitoci ƙwararru da basa wasa da aikinsu kuma babu wulaƙanci. Sai dai abinda ke matuƙar bata mamaki yanda asibitin yay matuƙar haɗuwa zaka ɗauka sai wane da wane ne masu iya shigarsa neman lafiya, amma saika shigo ciki kai gamo da masu karamin ƙarfi bila-adadin suna amsar magani hankalinsu kwance. Samun damar ganin likita akan lokacine ya katse mata dukkanin tunaninta. Sai dai yanda aka karɓesunne ya sake bata mamaki, amma jin zancen Khalipha a bakin likitan kuma sai ta fahimci a dalilin shine ake mata wannan tattalin da kulawar. An bata magungunan da suka dace da ita, tare da sake gargaɗinta akan daina duk wani aiki dan cikin jikin nata yana buƙatar hakan saboda ƴar matsalar da suka hanga tattare da shi. Ƙuruciya tasa batako damuba suka dawo gida. Sai dai bayanin da Naziru yayi na maganar kula da hutun nata a gaban Yayansa da bai kai ga fitaba yasa Abba gargaɗin kowa na gidan akan yasa ido kar Zinneerah ta sake wani aiki. Baki maman Sakina ta taɓe cikin ƙunƙuni take fadin, ‘Wayaga agola kinfi ƴaƴan gida’. Babu wanda ya tanka sai shi Alhajin ne ya dubeta rai ɓace, “Saude mikike faɗa?”. A zabure ta mike tana yarfar da hannaye da tafasu, “A'a kaga Alhaji bance komaiba nikam, karkuma a bugamin gangar ɗan bazakuɗa babu gaira babu sabar”. Daga haka tabar wajen fuuu. Ƙwafa yay kawai batare da yace komaiba. Tun daga wannan zuwan sai yazam Naziru kanzo ya kaita asibitin ganin likita kamar yanda akan rubuta musu. A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI sai ga cikin Zinneerah ya shiga watanni na takwas. Zuwa yanzu ta saki jikinta sosai a gidan, musamman ma da mahifiyarta da kannenta dake faɗaɗa farin cikinta a koda yaushe. Idan ka ganta bazaka taɓa dauka ita bace, bakinta ya buɗe sosai alamar dama can rashin samun ƴancin kai ke sakata zama mai sanyi. Ita kanta maman Sadiq har mamaki take a ranta dama Zinneerah nada surutu haka? Ta tabbatar nan gaba idan ta sake warwarewa sai tafima haka kauɗi. Danma lalurar cikin kanɗan taƙaita mata wasu abubuwan. Duk da waɗanan sauye-sauye da Zinneerah ta samu a rayuwarta hakan baisa ta manta da Khalipha a rantaba. Koda yaushe yana nan maƙale a ranta, wani lokacin har mafarkinsa takeyi, kota zauna zugum tana tunanin yaushene zai sake dawowa gareta ne ko dan ta masa godiya akan ɗawainiyar da yayi da ita?. Idan kuma Naziru yazo gidan har ALLAH ALLAH take taji yace Khalipha na gaisheta, dan yana kiransa lokaci-lokaci idan ya samu dama. Sai dai bai taɓa cewa a haɗasuba dan shi duk zatonsa tanada aure ne. Yauma kamar kullum suna baje a falon Mamansu suna cin gyaɗa dafaffe da Zinneerah ta ƙwallafa rai sai da aka sayo aka dafa mata, kallo suke suna kwasar dariya. Maman Sadiq dake ciki tana shirin tafiya sashe Alhaji ta fito falon da kwalliyarta. Kallon yanda suke cikin nishaɗi tayi daɗi da farin ciki na ratsa ranta itama. Ta ɗauki tiren data shirya abincin Alhajin tana faɗin, “Zinneerah tashi ki tura muku ƙofar ni zanje na kaima Abbanku abinci, idan kunji barci kafin na dawo kimasu Aliyu addu'a karsu kwanta babu addu'a. Wannan sarkin fitsarin Abdull ki tabbatar ledan katifan bata zameba a inda zai kwanta. Ga kuma magungunanki nan kisha kema kafin ki kwanta”. “To mama sai kin dawo”. Ta faɗa fuskarta washe da murmushi. Suma sauran yaran duk adawo lafiyar sukai mata ta ɗauki tiren ta fice. Yayinda Zinneerah ta saka Sadiq zuwa ya tura ƙofar suka cigaba da kallonsu. A can ɓangaren maman Sadiq ko bayan Alhaji yaci abincinsa ya ƙoshi take dubansa da damuwa. “Yaya dan ALLAH karkace na takura, baka ganin kuwa ya dace mijin yarinyarnan yasan wani abu game da ita”. Murmushi Alhaji yayi na manya. Ya gyara zamansa da cewa, “Eh kina kan gaskiyarki Hauwa'u, nima bawai hakan baya raina bane. Dama inason dai ta gama sakin jikintane sosai ta manta da duk wani ɓacin ran da yabarota daga gidan sannan. A yanda kuma nake tunani bata wajenta ya kamata muji komaiba. Nine zan shirya da kaina naje Danya ɗin domin ganawa da Baban nata da Mijinta. Kinga idan mun samu bakin zaren saimu yanke hukuncin daya dace. Dan indai ba rabuwa tai da mijin nataba tofa sai dai yasan mai yuwuwa”. Murmushi kawai taɗanyi, “To duk hukuncin daka yanke ai shine dai-dai Yaya. ALLAH yay mana jagora”. “Amin” ya faɗa yana maijin daɗi a ransa na yanda duk ta sakar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182