Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 96

Chapter 96

Makauniyar Kaddara Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

zatai ta barmuba, idan yarinyarnan ta samu lafiya saimu dawo a yita a tsanake dan a yanzuma babu nutsuwar da zaki fahimta tattare dake”. Baki ta buɗe a hasale zatai magana Mahma taja hannunta suka fice. Farah zata bisu Mahma ta dakatar da ita. “Wlhy idan kika biyomu ko Abdul-Mutallab naso ko baya so sai na sakashi ya sakeki tunda ke hankalinki a gwiwa yake, idan zaki zauna gidan mijinki ki zauna. Idan kuma zaki biyomune ki tabbatar kin fito kenan wawuya kawai”. Saurin ja baya Farah tayi dan Mahma ta fito musu ne a ainahinta shiyyasa itama Mammah ɗin ta gagara cewa uffan, sai masifa take a zuciyarta kamar zata haɗiye harshenta cikin ciki. Daɗi sosai AK yaji akan hukuncin Mahma, danshi kanshi a yanzu filin yin nazari yake buƙatar samu akan wannan al'amarin, ALLAH shine shaidarsa bai taɓa aikata zina da ƴar kowa ba, shi baima taɓa ganin Zinneerah ba sai a gidansu wannan zuwan. Amma gashi Baffah kansa zargin yaron nasane yake. Kai shi kansa da kansa zargin kansa yake dan kamaninsa da yaron abun a dubane akumayi nazari. A yanzu kawai yana ganin shawarar da zuciyarsa ke bashi ya kamata yabi kozai fita daga ruɗanin da yake ciki daga shi har ƴan uwansa. Miƙewa yay batare da yacema kowa komaiba ya fice a ɗakin. Hakan yasa itama Farah dafa masa baya sai dai ɗakinta ta nufa tana kuka ba nashiba. Hajiya iya da gaba ɗaya take jin komai yana mata nauyi a zuciya ta duba Khalipha a sanyaye tace, “Ka bisa Khalipha, kasan Moddibo bai iya ɗaukar damuwa da sauƙi ba”.. A raunane Khalipha ya jinjina mata kansa, dan shima a ruɗan yake da komai, saboda Hajiya Iya ta bashi takardar wajen mmn sadiq ya karanta ɗazun saboda fitowar sunansa a ciki. Ya kuma sanar mata gaskiyar abinda ya sani game da haɗuwarsa da Zinneerah.............✍ *_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇 0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* _________________________ *Page 38* ............Sai da Khalipha yay sallama a ƙofar ɗakin aka bashi izinin shiga sanna ya shigo, zaune ya sameshi cikin kujerar dake a ɗakin kansa jingine ya lumshe ido da makarinta. Bai motsaba daga yanda yake har Khalipha ya zauna a ɗayar kujerar dake kallonsa cike da tausayin ɗan uwan nasa. ɗan jimm yayi na wasu sakanni kafin yay ƙasa da kansa cikin lallashi yace, “Yayanmu dan ALLAH ka kwantar da hankalinka, insha ALLAH bin komai a sannu zai warware dukan aninda zuciya ke hasashe duk rintsi”. Wani ɗan murmushi AK ya saki yana buɗe idanunsa da gaba ɗaya launinsu ya canja, sai da ya yima Khalipha kallon wasu sakanni kafin ya tashi zaune sosai yana furzar da abinda ya tokare maƙoshinsa mai ɗaci. Cikin son danne duk damuwarsa yace, “Bestie dama kasanta?”. Ɗan kallonsa Khalipha yay alamar wa?. Idanunsa ya lumhe ya buɗe akansa, kamar bazai sake tankawaba sai kuma ya furta, “Zinneerah!”. A saman laɓɓansa. A bazata Khalipha ya saki murmushi, a ransa ko gulma yake (kai yayanmu kako iya faɗar sunan). A fili kam sai ya gyaɗa masa kai tare da ƙara nutsuwa sosai. “Nasanta Yayanmu, amma sanin na kwanaki goma zuwa sha ɗaya ne kacal idan ban mantaba. (A take ya fara bashi labarin haɗuwarsu a randa aka bigeta, wanda a dalilin aiken da yay masanema yaje jigawan, suna hanyar dawowa motar ta samu matsala. ya baro wanda sukaje taren da motar shiko yabi ta haya dan zuwa ya isar da saƙon karsu makara tunda yasan jira yakeyi). “Wannan shine dalilin dayasa na santa Yayanmu, ni duk zatona ma tanada aure wlhy, shiyyasa ban wani taɓa maida hankali akanta ba, inma baka mantaba na baka labarin accident ɗin ai a wancan lokacin. kuma ni a zuwan nan da mukaima sai ban ganetaba saboda duk ta canja, sai randa naga Gwaggo (Mmn sadiq) sannan na ƙara tabbatar da itace, inataso muyi maganama hakan bai faruba saboda ciwon Granny”. Ɗari bisa ɗari AK ya yarda da Khalipha, dan yason bai iya ƙaryaba, tunda suke dashi bai taɓa kamashi da wani abu na rashin gaskiya ba, zamansa ya gyara da ƙyau yana furzar da numfashi, cikin tsatstsare Khalipha da idanu yace, “Miye amsata ta ɗazun game da kamannina da yaro?”. Ƙasa Khalipha yay da kansa cike dajin nauyin gaskiyar abinda ke a ransa. Muryarsa a dakushe yace, “Yayanmu al'amarin akwai rikitarwa, harga ALLAH banida takamaimai amsa, dan bayan matarka nine mutum na biyu da zan iya bada shaida akanka, hakan yasa duk abinda zuciyata zata iya hasasomin ƙwaƙwalwata bazata iya ɗaukaba, shawara ɗayace shine ai gwaji kawai, maybe hakan ya kawo hasken da kowa zai iya fahimtar bakin zaren. Ka gafarceni idan nayi kuskure”. Murmushi AK ya sake saki mai sanyi yana gyaɗa kansa. Cikin nuna gamsuwar zantukan Khalipha yace, “Shiyyasa nake kiranka Bestie, dan mafi yawan tunaninka irin nawane, inason mutum mai gaskiya da ƙyaƙyƙyawan nazari akan komai Khalipha. ALLAH yay maka albarka, nima a raina shawarar zuwa Nigeria nake domin gwada ƙwayoyin halitarmu ni da yaron, maybe hakan zaisa na iya tuna wani abu dana manta ko samun ƙwarin gwiwar bakin zaren”. Khalipha dake murmushi yana jinjina masa kai yace, “Nagode Yayanmu”. “Nizan gode maka ai, dan ka zama ɗan uwa ɗaya tamkar da dubu. Yanzu kaje ka huta kaima, sai dai banason ka sanarma Granny tafiyata, sai na gama shiri zan sanar mata, insha ALLAH nanda awanni biyar zan wuce”. Cikin waro idanu Khalipha yace, “Yayanmu ince sai nan da kamar kwana biyu?”. Kai kawai ya girgizama Khalipha yana miƙewa da murmushi akan fuskarsa. Ganin ya nufi toilet shima sai Khalipha ya miƙe ya fita cike da tausayin Yayan nasu, ya tabbatar jarumtarsa da ƙoƙarin iya shanye damuwane kawai ya danne dukkan halin da yake ciki, amma duk wanda ya sanshi ya kalli ƙwayar idonsa yasan baya cikin kwanciyar hankali. (Ya ALLAH ka kawo mana mafita, ka haska mana duhun da muke ciki domin rahamarka ya UBANGIJI). Khalipha ya faɗa yana nufar ɗakinsa zuciyarsa cike da rauni da ɗaci. Har ransa kuma yanajin zai iya auren Zinneerah koda ace ƴaƴa goma ta haifa, amma yanason jin ta bakinta itama harga ALLAH. ★★ Tun bayan fitar Khalipha a ɗakin babu wanda ya sake jin ɗuriyar AK a gidan sai bayan awannin daya ambata ma Khalipha na wucewa 9ja. Duk da halin da yake ciki

Table of Contents

Chapters

182 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182