Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 22

Chapter 22

Makauniyar Kaddara Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

da zuciyarta yayi yasata dakatawa dayin game ɗin, haka yau ta tashi da wannan tsinkewar zuciya da batasan dalili ba, jin abin na ƙara ƙarfi ne ya sakata ajiye tab ɗin ta Khalipha gefe ta zame ta kwanta tana ambaton ‘hazbunallahu wani'imal wakil’ a ranta ko zataji ɗan daɗi............✍ *_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇 0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 9* ________________________ *_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_* *_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_* *_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_* *_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_* _Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_. *MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.* *AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON* *AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*. *_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_* *ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*. *KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻 _______________________ *Page 9* ..........Jin kamar ana nufo ɗakin ya sata miƙewa zumbur taja hijjab ɗinta da Khaliphan ya kawo mata saboda salla ta saka da sauri. Ƙirjinta ne ya sake ƙarfin bugawa fiye da ko yaushe lokacin da Khalipha yay sallama a ƙofar ɗakin. Haka yakeyi mata a duk sanda zai shigo sai yayi sallama ta amsa sannan yake shigowa. Yanzu ma bai shigo ɗinba sai da ta amsa ya turo ƙofar ya shigo. Kallo guda tai masa tai saurin maida idanunta ƙasa saboda kwarjinin da yake mata da cika ido. Sai dai kuma luguden dakan da ƙirjinta ke mata ne ya tilastata sake ɗago kanta badan ta shirya ba. Naziru ne biye da bayansa. Sai matarsa. Sai wasu mata biyu da batasan daga inaba. Sai dai shigowar ta ƙarshen ya sakata wani irin zabura tana binta da kallon ƙurilla maiban mamaki. Yanda take kallon matar da yanda itama matar take kallonta tana tafiya da ƴar sassarfa ne yaja hankalin su Khalipha garesu baki ɗaya. Kusan mini ɗaya matarnan da Zinneerah na kallon juna batare da sun saniba, sai can Zinneerah ta fara janye nata tana sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya a ɓoye. Kanta ta maida ƙasa tana ƙoƙarin haɗiye hawayen da suka cika mata ido da batasan na minene ba. Jin yanda ɗakin yay shiru ɗayar matar da suke tare da itama al'ajabi ke neman halakawa ta katse shirun da faɗin, “Baiwar ALLAH sannu kinji, ALLAH ya kiyaye gaba, ya ƙara lafiya”. Kusan a tare duk sukace amin, banda matarnan mai kama da Zinneerah da gaba ɗaya hankalinta bayama tare da ita. har yanzu kuma idonta nakan Zinneerahn. Sun ƙara jajanta mata da mata addu'ar samun lafiya mai ɗorewa sukai musu sallama suka fita bayan matan nan biyu sun ajema Zinneerah kuɗi. Koda zasu fitanma matarnan tana tafiya tana waigen Zinneerah har suka fice. Shi dai Khalipha yana tsayene yana kallonsu da nazari tun shigowarsu har suka fice. Wayarsa da ke ring a aljihu ta sashi sauke numfashi da warware hannayensa daya harɗe a ƙirji ya cirota a aljihu. Wani lallausan murmushi ya saki wanda yay dai-dai da ɗagowar Zinneerah. Sai ko ga idanunsu cikin na juna. Tai azamar maida kanta ƙasa ƙirjinta na wani irin harbawa, dan ba ƙaramin dukan zuciyarta wannan murmushi nashi yayiba. Shikam wayar ya kai a kunne yana ɗan lumshe idonu, cikin wata murya mai ɗunbin ladabi da girmamawa yace, “Assalamu alaika Yayanmu”. Batajin mi ake faɗa acan ɗin, sai Khalipha ne taji ya wani sake narke murya da shagwaɓa yana faɗin, “Oh Yayanmu Please ka jirani gani nan zuwa, nifa nace zan kaika da kaina yau, nanda mintuna goma insha ALLAH ina gida”. Bataji mi nacan ya sake cewaba. Sai Khalipha ne ya matso gaban gadon yaɗan bubbuga yana cigaba da sauraren abinda ake faɗa ɗin daga can. Ɗago kanta tayi ta kallesa dai-dai ya sake narke fuskar tamkar wani yaro ƙarami, kokuma yana a gaban wanda yake wayar. “ALLAH Yayanmu bazanyi gudu ba, kasan mashin bakamar motaba ai, kuma zanbi ta hanyan dazan samu sauƙine fa Please ”. Ita dai Zinneerah ganin yana neman zauta mata kwanya taso sake maida kanta ƙasa sai yay saurin mata alama da hannu wai yana zuwa. Bai jira cewartaba ya fice da hanzari. Bin bayansa tai da kallo harya fice, tsigar jikinta na wani tashi batare da tasan daliliba. Sai kawai ta fashe da kuka. Kuka sosai Zinneerah taci wanda yana alaƙa da wasu baƙin al'amura a gareta, sai dai ƙuruciya ta hanata fahimtar komai. Ta zame a hankali ta kwanta tana lumshe idanunta badan barciba, sai don son samun damar tunani da wassafo matar ɗazun da takesonyi harma da tuno halin data shiga a dalilin ganin nata da wanda ta lura itama matar ta shiga saboda ganinta. A ɓangaren Maman Sadiq kam itama tunda suka fito daga asibitin tafiya kawai take tamkar bata cikin hayyacinta, jitake kamar ta dawo ta sake ganin Zinneerah ɗin saboda abinda takeji a ranta da dukkan magudanar jinin jikinta a dalilin tozali da yarinyar. Duk da wani ɓangare na zuciyarta na ƙwaɓarta da cewar ba haka bane ta kasa yarda sam. Daga Naziru har matarsa hankulansu nakanta ne suna nazarin halin da take a ciki, sai dai basuce komaiba har ya maidasu gida shima ya wuce nasa gidan da matarsa. Inda sai anan suka sami damar tattaunawa akan yanayin maman Sadiq ɗin. Tunda suka shiga cikin gida ta buɗe ɗakinta ta shige saita kasa zaune ta kasa tsaye, kaikawo taketa famanyi a ciki, duk da masifar kishiyarsu Saude da take jiyowa akan taƙi fita ta ɗora girkin rana ga lokacin kaima yara abincin rana makaranta ya kusa bata fito ɗinba. Sai Uwargidansu da sukaje asibiti tare ce ta jiyo tana bama Sauden amsa da “Haba dai Maman Sakina, kodan himma irinta Maman Sadiq ai yakamata ki fara tunanin anya lafiya kuwa? Amma sai ki ɓige da neman fitina daga shigowarmu gidan dai”. A harzuƙe da masifar da dama Sauden jira take

Table of Contents

Chapters

182 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182