Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 31

Chapter 31

Makauniyar Kaddara Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

ƴar takarda dake a linke da alamu suka nuna cheque ne na kuɗi. Takardar Mama ta amsa batare data fahimci ta minene ba, yayinda su kuma mutanen wajen suka sami damar yin dariyar yanda ta ruɗe musu ɗazun. Mama ma dasu Alhaji duk dariyar sukeyi, daga haka suka ɗunguma ɗakin da aka kwantar da Zinneerah. Mamaki ya kama Mama ganin ashema ta farka har likitan daya shigo ɗakin dubata yana ɗan musu faɗa akan fita su barta ita kaɗai haka. Haƙuri mama ta bashi, tare da masa bayanin dalilin fitar tata. Ya ɗan murmusa yana faɗin, “A mama ai asibitin nan akwai tsaro sosai, motsin kowa dake ciki ana ganinsa ta cctv, dan haka ku kwantar da hankalinku babu abinda zai faru harku tafi insha ALLAH”. “ALLAH yasa hakan” suka faɗa kusan a tare. “Amin ya rabbi. Yanzu ga wannan, shine list ɗin komai na kuɗaɗen da zaku biya, sai kuma jini da zaku samo yanzu dan za'a ƙara mata. Dama jiran farkowarta muke mugani koda yuwuwar hakan, to yanzu kam naga alamar tana buƙatar jini leda ɗaya”. Amsar takardar Alhaji yayi yana masa godiya, daga haka Doctor ya fice. Gaban gadon suma duk suka ƙarasa sunama Zinneerah sannu, da kai kawai take iya amsa musu batare data iya kallonsu ba. Sai faman haɗiyar zuciya take dan ita kaɗai tasan mitakeji a ranta. Ganin kamar batason hayaniyar ne ya saka Nurse Salima dake ɗauke da ɗan jinjirin daya gama shige mata rai har yanzu faɗin, “Inaga batason yawan hayaniya yanzu, idan kun gama dubata sai muɗan fita waje a bata waje”. Gamsuwa da bayaninta ya sakasu amsa mata. Mama ta kalli Salimar tana faɗin, “Yauwa ƴarnan kinma sa na tuna. Ina dabinon da kika bada shawarar a tauna a bashi? Kinga yanzu tunda ga Alhaji sai ya bashi ɗin ko”. Cikin ɗan nuna shakku Salima tace, “Aiko mama na muku laifi ko nace shishshigi, nazo da dabinon danna kawo mikine na biya office ɗin Dr Mahmud ɗin inda na sami Oga acan. To daya sanar min ɗakin da zan kawo yaron sai nake cewa dama can zani nakai dabino a bashi ko zai rage kukan yunwar da yakeyi. Jin hakan da kuma kukan da yaron keyi har lokacinne ya saka Oga ya amshi dabinon da kansa ya tauna ya bashi, har yana faɗin ALLAH yasa ya gaji sunansa”. Alhaji dake saurarensu yace, “To masha ALLAH, ALLAH ya saka masa da alkairi duk da mu bamusan shi wanene ba”. Salima tace, “Baba ai shine mai asibitin nan”. Dukansu sai da suka ɗan ƙwalalo idanu waje. Mama tace, “Babbar magana, shima likitanne kenan?”. “A'a mama, shi ba likita baneba, ɗan kasuwane. Nasan dai bazaku gaza sani kojin sunan *_AK SHIRA_* ba a garin nan ai”. “Lallai kam sani bana wasaba, duk da dai ba sani na zahiri bane, amma wannan sunan ba ɓoyayyen suna bane, dan a Shira Family kowa yasan *AK SHIRA* ba ɓoyayye bane, kodan gidajen mansa kawai ai sun isa ka sanshi, balle kuma hidimar da yake ga bayin ALLAH mara iyaka”. “To aiko Baba shine da kansa ya bama jaririn nan dabino yau, tare da wannan takarda da nake kautata zaton kuɗine rubuce a ciki”. Sosai maganar ta sake girgizasu, mama ta mikama Alhaji takardar cheque ɗin. Amsa yay ya duba yana jinjina kansa. “Uhm lallai wani aiki kam sai manya. ALLAH ya saka masa da alkairi. ya azurtashi da duk alkairan duniya da lahira, ya kuma cigaba da karesa a duk inda ya saka ƙafa. Kuɗine zunzurutu harna dubu ɗari biyu ya rubuta anan”. Sosai suka ƙara jin mamakinsa, ace lokaci guda mutum yay ƙyautar dubu ɗari biyu wa jariri kawai. Alhaji ya katse zantukan nasu da faɗin, “To lallai kam abokina dole kaci sunan AK Shira ai”. Dariya duk sukayi banda Maman Sadiq datai ɗan murmushin kawaici. Hakama Zinneerah dake saurarensu kawai tana share hawayenta a ɓoye. Alhaji ya buƙaci Salima ta rakashi yaymasa godiya, daga nan yaje wajen neman jinin da biyan kuɗaɗen da sukace. Bata musaba ta miƙama Mama jaririn suka fita. Office ɗin Dr Mahmud sukaje. Bayan Salima tai knocking ya basu izinin shiga suka shigo. Shi kaɗaine a ciki, sai dai mayen ƙamshinsa na nan manne da office ɗin duk da babu shi a ciki. Dr Mahmud yace, “Salima lafiya dai?”. “Laya ƙalau Doctor, dama Baba ne yace na rakosa yayma Oga godiya. Sune masu jinjirin nan na ɗazun”. “Oh ALLAH sarki, Baba ina yini”. “Lafiya lau likita, ya aikin naku?”. “Alhmdllh baba. Sai dai gashi kuma shi harya tafi, kasan shi uziri ba ƙaremasa yakeba. Dama yakan zo duk irin wannan ranar a tsakkiyar shekara da ƙarshenta ne ya bada jini inhar yana kano, yanzu hakama zaije Lagos ne ya biyo tanan ya bayar, ina ƙyautata zaton yanzu haka ya isa airport”. Alhaji yace, “Ashsha. Naso kam na gansa nai masa godiya wlhy, sannan ya cika ladansa nama yaron nan huɗuba ya kuma saka masa sunan nasa dan ya cancanta”. Cikin jin daɗin wannan karamci Mahmud yace masha ALLAH, shi da ya faɗa da wasa ashe ALLAH ya amsa mai sunan nasa aka samu, duk da nasan yanzu yayi nisan kiwo, amma bara na taɓasa a waya muji ko zamu samu ya ɗaga baba ka zauna”. Zama Alhaji yayi yana murmushi. Dr Mahmud ya ɗauka wayarsa shima fuska ɗauke da murmushi ya shiga kiransa. Tana gab da tsinkewa aka ɗaga. Harma Mahmud ya fidda ran hakan. Cike da zumuɗi Mahmud yace, “Afuwan ranka ya daɗe kaga na kiraka”. Basusan amsar da aka bashi daga canba. Cikin ƴar dariya yace, “Tona gode ranka ya daɗe. Dama masu jaririn daka ɗakko ɗin nan ne sukazo maka godiya, tare da sake kawosa ka cika ladanja ta masa huɗuba da saka masa sunan naka”. Nanma basuji miya faɗaba, sai dai yanda fuskar Dr Mahmud ta ƙara washewa da fara'a zaka tabbatar da magana mai daɗi yake masa. Sai kuma ya saka wayar a amsa kuwwa (Hansfree) ya ajiye gaban Alhaji. Wata tattausar murya mai cike da tarin nutsuwa kamar ta rowa sukaji tace, “Assalamu alaikum, baba barka da rana”. Da sauri Alhaji yace, “Wa'alaikissalam, barka dai ranka ya daɗe, yaya ƙoƙari?”. “Alhmdllhi baba. Yanzun nakejin daddaɗan albishir na samun takwara, gashi kuma nayi gaggawar tafiya”. Yanda yake maganar cike da nutsuwa kamar bayasone ya saka Alhaji yin murmushi mai faɗi. “Alhaji ai kowa zaiso samun mai sunanka a gidansa kodan tarin alkairan dake tattare dakai. Munga hidima ALLAH ya saka da alkairi ya ƙara buɗi. Amma naso ace kaine da kanka kaima yaron nan huɗuba da sunan daka zaɓa masa”. Kaɗan sukajiyo sautin murmushinsa daga can, cikin sake nutsar da muryar tasa mai sauti a tausashe yace. “Nima naso hakan Baba, dan kun bani abu mai daraja da bazan mantaba a tarihin rayuwata, amma duk da haka na bama Mahmud wakilcin yima takwarana huɗuba. ALLAH ya rayasa ya albarkaci rayuwarsa, ALLAH yasa ya zama mai tausayinmu da jin ƙanmu anan gaba”. Atare suka amsa da amin kowa cikin jin daɗi. Musamman ma Alhaji dake mamakin yau shine ke magana da AK Shira baki da baki ta waya. Wata hikima sai UBANGIJI. Shikam dai har abada bazai taɓa mantawa da haihuwar wannan yaro ba a rayuwarsa. Kamar yanda ya bada wakilci ga Dr Mahmud hakance ta

Table of Contents

Chapters

182 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182