Chapter 98
Chapter 98
Adnan akan kamanninsa da Little”. Murmushi Baffa yayi mai faɗi, ya gyara zamansa yana faɗin, “Nasani Hauwa'u, muma kuma ba hakan bane a ranmu wlhy, sai dai ki sani tun randa kukazo da yaron nan gidannan babu wanda zuciyarsa ta huta akan kamaninsa da Adnan a gidan nan. Jin gaskiyar samuwarsa tasa muke kwaɗayin yin gwajin ko hakan zai sama mana kwanciyar hankali, dan nayi alƙawarin saina ƙwatoma Zinneerah haƙƙinta awajen koma wanene. Yanzuma bayan anyi gwajin insha ALLAH gobe idan ALLAH ya kaimu zamuje can asalin ƙauyen nasune. Dan haka banason zuciyarki ta ƙara miki wani hasashe daban bayan ƙyaƙyƙyawa”. Sosai raunin mmn sadiq ya bayyana, tace, “Shikenan yaya, ALLAH ya saka da alkairi yabar zuminci. Bara nama Yaya magana to dan yana gida sai mu kawosa kawai”. “Hakan shine dai-dai, mu haɗu a shira hospital daku”. Daga haka Baffah ya yanke wayar. Wanka kawai AK ya samu yayi bayan Safiyya sunje sun gyara masa ɗakinsa da falon ɓangaren hajiya iya, abincima bai iya ciba sai tea yasa Ni'ima ta haɗa masa. daga haka ya fito ya sami Baffah dake zaman jiransa yana waya rai ɓace. Shiru yay yana nazarin wayar ta Baffah, inda kai tsaye ya gane da Mammah suke waya, runtse idanunsa yayi da ƙarfi jin yanda Baffah ke dasama Mammah baƙaƙen maganganu, wanda ya tabbatar itace ta fara masa, shiko yake maida mata murtani. Juyawa yay a hankali zai fita ya jiyo kalaman Baffah da suka sakashi dakatawa a kausashe. “Komi zakice kice Hindatu, wlhy da banma kawo hakan a rainaba game da Adnan. Amma wlhy kinji na rantse a wannan gaɓar zan tabbatar miki da cewa ni Kabeer Abdul-Mutallab Shira nine mahaifin Adnan, ba kuma tsoronkine yasa na barmiki shiba daga shi har ƴar uwarsa. Dan haka muzuba mu gani ni dake ɗan hakal ka fasa”. Daga haka Baffah ya yanke wayar yama kasheta gaba ɗaya dan baya buƙatar ta sake kiransa..............✍ *_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇 0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* _________________________ *Page 39* ..........Da sauri AK ya ƙarasa ficewa ransa na masa ƙuna da wannan halayya na Mammah, bashi da burin daya wuce ganin iyayensa sun sasanta kansu sun koma rayuwar aurensu, sai dai ya gwada ƙoƙarin yin haka yafi sau a ƙirga abin ya gagara. Kuma Mammah ce ke bada matsala a koda yaushe. Tunma Baffah na nuna masa zai amince shi, har takai yanzu idan yay masa maganar Mammah saiya ja masa warning. A mota ɗaya suka tafi ran kowa babu daɗi, dan haka motar ta ɗauki shiru sai driver daketa aikin tuƙi har suka isa Shira Hospital. Tuni AK ya tanadi likitocin da zasu aikin harsu uku domin samun gamsuwa akan abinda zai fito, dan haka suna isowa suma su Mmn Sadiq suka iso ɗauke da Little. Yanako ganin AK ya maƙale masa, duk da ɓacin ran da AK ke ciki sai da yay murmushi yana mai rungume little a jikinsa. Ganin yaronma da yayi sai yakeji a ransa ALLAH ma yasa ya kasance nashi ɗin, dan har cikin ransa wata irin ƙauna yake masa mai ƙarfi da saka zuciya nutsuwa. Cikin mutunta juna suka gaisa, inda mamaki ya cika Dr Mahmud saboda ganin Abba. Shima Abba daya ganesa sai wani tunani yazo masa. Cikin kasa jure abinda ke ransa yake tambayarsa ko ina bawan ALLAHn nan daya sakama little sunansa?. Kai tsaye Dr Mahmud dake dariya ya nuna AK, “Baba ai gashima zaune, ina takwaran nasa kuwa? Nasan ya girma yanzun ko?”. Da sauri Abba ya kalli AK da Little ke a jikinsa zuciyarsa na bugawa. Cikin ɗan rawar murya yace ai ga yaron nan a hannunsa”. Ba Dr Mahmud ba, hatta AK sai da zuciyarsa ta harba. Yay saurin duban Abba da faɗin, “Uncle kana nufin kaine wanda ya bani damar zaɓama yaro suna shekara uku data shuɗe?”. “Tabbas nine kuwa. Kuma wannan shine yaron”. Sosai maganar Abba ta sakasu jin shock su duka. Baffah dake saurarensu ya nemi jin ƙarin bayani. Dr Mahmud ne yay masa bayanin komai har yanzu firgici da al'ajabin kamannin little da AK na bayyane a fuskarsa. Murmushi baffa yayi yana jinjina kansa. Sai dai komai baiceba yabarma zuciyarsa. Dan yama gama yarda AK na ɓoye masa wani abune game da yaron kenan, inba hakaba yaya akai hakan ta faru? Tunda a wannan zuwan basusan yazoba sai a shanun ƴan talla yaji. To lallai kam zaiyima tufƙar hanci, dan yama gama yanke hukunci saura zartarwa. Baffah ne ya dakatar da wannan hasashen su Dr Mahmud suka shiga aikinsu. Duk wani gwaje-gwajen daya dace akan ƙwayoyin haluttar little da AK akai musu. Abinka da masu abu, ba'a wani zauna wasaba suka shiga ganin sun tantance komai dan Baffah yace bazasubar asibitinba sai da result....... _________________________★ *DANYA* A lokacin da gwajin ƙwayoyin halitta ke gudana acan Shira Hospital tsakanin AK da Little anan danya kuma baƙuncin Baba su Inna suka samu da farar safiya babu zato babu tsammani. Duk suna zaune a tsakar gida ƴan barka na shigowa jefi-jefi da ƴan gulma. Karima na ɗaki kwance ita da ƴar jinjirarta tana kwasar kuka akan abinda ya barota da Kaduna, dan wahalar ciki tasa bata samu damar nazari akan komaiba sai yau da take jinta sakayau. Tinene na kwance a ƙofar ɗakinsu wai ƙirjinta da kanta na ciwo, tun safe data tashi da abinda ta wayi gari kenan. Sai Sa'a daketa kaikawon yin aiki ita da Yaya Gajeje. Inna kuma na zaune kusa da Tinene tana gyaran gyaɗa da Yaya Gajeje tazo da ita gidan domin yin miya. Sallamar mace da sukaji ya sakasu ɗan juyowa kusan su dukansu dan duk zatonsu ƴan barka ne ko cikin dangin Babawo dakan zo jefi-jefi, dan innarsa ma da tace zata dawo tun jiya har yau basuga ƙeyartaba. Sai dai ta aiko musu da kayan kunun da tace dana barka kuma kamar yanda uwar miji keyi a al'adar ƙauyen. Ƙyaƙyƙyawar mace mai tarin kamala da ƙwarjini ta sake maimaita sallamar datai musu ganin duk sun zubo mata idanu basu amsaba. Yaya Gajeje ce tai ƙarfin halin amsawa da cewa, “Maraba, bismillah shigo baiwar ALLAH duk da dai bamu wayekiba”. Murmushi matar tayi tana ɗan juyawa bayanta jin motsin takowar abokin tafiyar tata. Kafin ta samu damar bama Yaya Gajeje amsa Baba ya shigo shima da sallama a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182