Chapter 174
Chapter 174
“Daddyna yace nakiraki zaije anguwa”. “Naji to, kace ina zuwa”. Sai da little ɗin ya fita ta duba Mama A'i. “Mama an gama haɗa abinda ya rage ɗinne?”. “Eh an gama maman Abdul, harma na miki karanbani na shirya a tray ”. “Kai aiko ngd aiba karanbani bane”. Zinneerah ta faɗa tana mikewa. Fita tayi domin kai masa kayan breakfast ɗinsa. A falo ta samesa zaune yaci gayu cikin ɗanyar shadda ash, yana zaune a dogon kujera little a kusa dashi yana duba masa ƙafarsa da yaji ciwo. Koda tai sallama bai ɗagoba har ta karaso inda suke ɗauke da tray ɗin. “Barka da hutawa”. “Barka” ya amsa mata yana ɗan dagowa ya dubeta. Duk yanda yaso maida idonsa ga ƙafar little ɗin kuma sai ya kasa. tai ɗan murmushi da ɗauke kanta ganin kallon da yake mata. “A ajiye nan ko dining?”. Lumshe idanun yayi ya ɗan buɗe a kanta, cikin kasalar data samesa yanzu yace, “Ajiye anan kawai”. Saman centre table ta ɗaura tray ɗin da duban ƙafar little dake cikin hannunsa. “Shi kuma wannan miya samu ƙafar tasa?”. Iska AK ya ɗan furzar. “Yace faɗuwa yayi ga waje harya fashe, taimakemu da man zafi ma a ɗaki”. Bedroom ɗin nasa ta nufa tana faɗin, “Maganin mai gudu kenan idan yana tafiya”. Murmushi kawai AK dake binta da kallo yayi, dan a kwankin nan data haihu duk ramar nan ta ciki da tayi nan ɓacewa take, sai wani irin buɗewama takeyi alamar lafiya ta samu. Miƙewa yay yabi bayanta yanama Little gargaɗin ya jirasa ya dawo. Zinneerah na ƙoƙarin fitowa sukaci karo, baya ta koma tana faɗin, “Ouch Yayanmu zaka fasamin kai”. “Kokuma ni zaki fasamin ba”. Ya faɗa yana matsota. Kallonsa take da mamaki, ganin dai da gaske kanta yayo tai saurin faɗin, “Yayanmu wani abu ya farune?”. “Faffaruwa ma madam” Yay maganar yana kamo hannunta da jawota jikinsa. Hancinsa ya cusa cikin wuyanta yana magana raɗa-raɗa. “Ko tausayinama baƙyaji kin barni da kwana da little ke kinacan kina morewarki ko?”. Dariya zancen nasa ya bata, amma sai batayiba tai murmushi da ƙoƙarin ƙwace kanta. “Yayanmu ai amfanin mata biyu kenan, ni ina fama da wannan fiɗan inani ina ɗaukarka. Kawai aunty Farah ta dawo kaga ni sai nayi arba'in”. Gani tai ya saketa baki ɗaya yana tsuke fusaka. Ya watsa mata harara yana jan guntun tsaki, batare da ƙara cewa komaiba ya juya ya fita a ɗakin. Bayansa tabi da kallo tana murmushi, a fili tace, ‘Uhm ka gama mazuranka ne dan nasan kana son kayarka’. Iskeshi tai yana zuba abincin da kansa. Batai maganaba ta matsar da little kusa da shi ta zauna, “Ina waje. ciwon Alhaji?”. Ta faɗa tana kamo ƙafar little. Nuna mata yayi, ta buɗe man zafin ta shafa masa yana wani shii da baki da yarfar da hannu. “Daddy kace tayi a hankali zafi”. “Oh ALLAH, ALLAH yaron nan saika kashe auren da babu soyayya, yanzu shafa maganinne da zafi?”. Zancen nata ya bama AK dariya amma sai ya gimtse bai yiba. Yadai kamo hannun little ɗin yana bata amsa a daƙile. “Dama can babu soyayyar ne ai”. Tasan da biyu ya faɗa, dan haka taja bakinta tai shiru. Sai dai ta cigaba da kallonsu yanacin abincin yana bama yaronsa har suka kammala. Bai wani jima da gamawarba ya mike yana kallon agogo. “Saifudden zai kawo muku cefane. Dan bazan dawo ba sai dare”. Mikewa itama Zinneerah tayi da faɗin, “ALLAH ya saka da alkairi ya kara buɗi, miza'a dafa maka da daren”. Kallonta yay cikin ido sonta da buƙatarta na ɗawainiya da shi, yaja numfashi da duban inda little yake. Ganin hankalinsama ba'a kansu yakeba sai ya sake kallonta. “Abinda nakeso a dafamin kam ai ba bani za'aiba. Sai dai nayi manage da tuwo”. Murmushi tayi tana maida kanta gefe dan tasan ina ya dosa, ta hau tattara kwanikan, “Uhm ni Yayanmu ALLAH fitina kake ƙarowa kullum, na kawo mafita kuma kaji haushina”. “Ke dai kika sani” ya faɗa yana nufar ƙofa. Murmushi kawai tayi ta cigaba da abinda take. Sai da ta kammala ta tisa ƙeyar little da baima lura da fitar Daddyn nasaba ta rufo sashen. A sashenta ta samesa zaune suna gaisawa dasu Yaya Gajeje ƴan biyu duka na'a jikinsa yana kallonsu zuciyarsa fes da farin ciki. Inda yake little ya nufa ita kuma ta nema waje ta zauna. Ya ɗan jima a falon suna maganar jikin Inna daya fara lekawa tana barci dasu Yaya Gajeje kafin ya basu yaran da musu sallama ya fice, bayan ya jefeta da wani kallon duk randa na kamaki. Murmushi mai sanyi kawai tai masa da rakashi da addu'a. Shima daga nan sashen Farah ya shiga inda ya samu su Mammah na karyawa. Sun gaisa nanma yaɗan zauna suka taɓa hira sannan yay musu sallama yabar little anan ya fice. ★★★ Daga ranar Zinneerah bata sake masa zancen Farah ba har ALLAH yasa sukai arba'in. A randa tai arba'in ɗin kuma su Mammah ke shirin tafiya katsina duba su Farah daga can su wuce london. Gaba ɗaya Zinneerah sai ta shiga damuwa. Dan zamansu a gidan ba ƙaramar shaƙuwace ta shiga tsakaninsu ba. Ganin shine zai kaisu katsinar ta sake daurewar masa zancen dawowar Farah sai ya balbaleta da faɗa, duk da tasan bayason wargi bata taɓa ganin fushinsa irin yau ba. Ita kuma yanda yake mata ihu akai yasata fara kuka. Suna haka Mammah ta shigo falon. Saurin share hawaye Zinneerah tayi tana ƙaƙaro murmushi da yima Mammah ɗin dake binsu da kallo sannu. Daga haka ta zame ta gudu ta barsu, dan tasan tunda Mammah din ta shigo nan da kanta magana zatayi da shi. Da kallo tabi Zinneerah harta fice kafin ta maida ga AK dake ta wani bata fuska. “Abdul-Mutallab mi kaima yarinyarnan?”. Guntun tsaki yaja yana murza goshinsa. “Mizan mata kuwa Mammah, itace da neman fitina kawai”. Shiru Mammah tai tana kallonsa cike da nazari, sai kuma taɗan girgiza kanta da cewa, “Fitina kamar ya? Ai kowa Yasan Zinneerah bata da kwaramniya, dan nidai a zamanmu gidan nan banga wani abun ashsha daga garetaba sai dai ajizanci irin na ɗan adama kawai. Amma yarinya mai kawaici da kunya ga haƙuri. Sai dai idan kai ne da laifin tunda sarai na san halinka bawai baƙona bane. Miya haɗaku?”.. “Nifa Mammah babu abinda nai mata. Kawai ta isheni da zancen Farah ne”. Kallonsa kawai Mammah keyi dan maganar yanayintane da faɗa sosai. Ta sauke numfashi da gyara zamanta. “Abdul-Mutallab nasan Farah mai laifine tabbas, amma karka manta harda gudunmawarmu, kuma maganarta da yarinyarnan take maka tasan kantane. Dan wannan haline irin na mutanen ƙwarai da sake tabbatar maka ita mai tarbiyyace da hangen nesa. Ni bazance dole ka dawo da Farah gidankaba, amma zan baka shawarar ka daina ƙuntata yarinyarnan akan abinda ba laifinta bane saima alkairi da takeson ɗoraka akai. Ita rayuwa komai ɗan haƙuri ne ai. idan akai haƙurin sai komai ya zama labari wataran”. Shi dai kansa na ƙasa baice mata komaiba harta gama zancen Farah da Zinneerah ta ɗakko abinda ya shafesu sannan ya tsoma baki. Duk da Zinneerah tasan su Mahma basu rasa komai na rayuwaba sai da ta shirya musu tsaraba domin girmamawa. Musamman turarurrukan khumrah dana wuta da a koda yaushe
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182