Chapter 173
Chapter 173
da ita zaman asibiti. Kwanakinta shidda a asibitin a wata safiya ta wayi gari da naƙuda. Sai dai fa tamkar cikin little jini ya ɓalle mata ga haihuwar shiru. Hankalin AK da kowama ya tashi, hakan yasa Dr Mahmud ya bada shawarar kawai ai mata cs kafin ta jigata ƙarfinta ya ƙare. Babu wani jayayya AK ya amince. Zuciyarsa fal tausayin halin da take ciki. Yayinda yake rayawa a ransa ko wannan tashin hankali da ta shiga a wancan karon na haihuwar little ya isa hana su Farah zaman lafiya da jin daɗi. Shikam sai yanzuma yake ganin matsalar da sukaita fuskanta na rashin jin daɗin rayuwar aurensu kullum faɗa da fitina shi da Farah ko wannan halin da suka zama sanadin jefa yarinyarnan ya isa su rasa farin cikin rayuwar aurensu ai. Dan Dr Mahmud ya tabbatar masa da haka tasha irin wannan wahalar a wancan karon ma. Alhmdllh an yi mata cs aka ciro ƴaƴa biyu mace da namiji. Zokaga murna wajen kowa. Shikam AK duk da yana murna da samuwar tasu hankalinsa nakan matarsa. sai da yaji tabbacin kasancewarta cikin ƙoshin lafiya sannan hankalinsa ya ɗan kwanta harya amshi jariransa ƙyawawa masu lafiya yana mai jerama UBANGIJI godiya daya bashi ƙyautarsu ta silar da ALLAH ya halatta masa bayan ya cire tsammani daga hakan. Inna daketa samun sauƙi tana zaune dan yanzu takan ɗan motsa jikin aka sanar mata da haihuwar Zinneerah. Hawaye kawai su Sa'a sukaga tanayi amma batace komaiba. Hakan yasa suka gagara fahintar na minene? Na daɗine kona nadama? Kona baƙin cikin har yanzu?. Oho masu karfin ajin ma basusan tanai ba. Dan cikin ƙanƙanin lokaci Shirawa suka cika asibitin domin taya Yayansu murna da samun wannan ƙaruwa. Waɗanda basa kusa kam irinsu Khalipha da Adilah tuni hotunan babes ya isa ga wayoyunsu. Addu'a dai kam sun shata kamar yanda Zinneerah ma keshan tata na fatan samun lafiya. dan kowa bai gantaba itakam har AK ɗin sai da daddare. Shima ya samu tanata barci. Ya ƙureta da ido cike da tausayi da ƙauna dan dukta rame sosai fiyema da lokacin da cikin na jikinta. Sumbatar goshinta yayi da hannunta yana mai jera mata addu'ar samun lafiya. Sauran ƴan uwa kuwa da abokan arziƙi basu sami ganintaba sai washe gari, zuwa sannan ta farka Alhmdllhi. Kuma tana gane kowa da amsama kowa gaisuwarsa. Lokacin da taga ƴan jinjirayenta da farin cikin dake shinfiɗe a fuskar AK murmushi ta dinga zubawa itama. a ranta tana musu addu'a. A fili kuwa sai ta dinga nuna alkunya su Hajiya iya na mata dariya. Sai dai har cikin ransu hakan da tai ya musu daɗi, dan yaran yanzu daba kawaici garemu akan ƴaƴaba koda na farine balle na biyu. Sai dai kuma wata sabuwa. wannan karonma tamkar haihuwar little ruwan nono ya zamarwa yaran damuwa. Dan da sun sha cikinsu duk sai yake kumbura suyita kuka. Ga namijin da son abinci tamkar ubansa. Hankalin AK ya tashi matuƙa da hakan. Amma da Dr Mahmud ya sanar masa haka dama sukasha fama akan little sai yaɗan sami nutsuwa. Yanzuma magunguna suka haɗa mata. Amma sai Mahma tace wanann al'amari kamar bana asibiti ba. Yanada nasaba da jinnu sai an dage sosai ma Zinneerah ɗin. Kowa yasha mamaki, amma sanin wacece ita a wannan fanin yasa duk suka amince. Itace da kanta ta fara harhaɗama Zinneerah magungunan gargajiya ta fara amfani dasu, tace insha ALLAH komai zai daidaita. Kwananta takwas a asibitin aka sallameta, Alhmdllhi zuwa yau kuma yara sunsha nono kuma babu wani matsala data biyo baya. Hakan ya saka kowa farin ciki dajin daɗi. AK yaga amfanin wannan sani na Mahma da yaketa ƙorafi akansa tunda gashi ta bama matarsa magani an kuma dace. A randa aka sallamesun ranar Mammah ta iso Nigeria, zokaga murna wajenta datai tozali da ƴan jikokinta. Su Adilah ma an iso daga Lagos suda tawagar Mommy. hakama Gwaggo Maryama. Inna ma da aka sallamota nan AK yace a kawo ta huta sosai kafin a maidata Danya. Kai tsaye gidan hajiya iya aka wuce da Zinneerah, za'ai suna acan sannan su koma gidansu su cigaba da jego kuma. Yara sunci sunayen Hajiya Iya da Baffah. *_Ameenatu & Kabeer_* za'ake kiransu (Amaan & Anam). AK ya zata Mammah zatai fushi, sai yaji batace komaiba. Yaji daɗin hakan, dan koba komai ya yarda ta dawo hankalinta yanzu kam. (An zinni sai muce ALLAH ya raya keda yayanmu angon jego). AK dai bason bidi'a yakeba. Dan haka aka shirya ƙwarya-ƙwaryar liyafa anan harabar gidan akaci akasha kowa ya godema ALLAH. Ƴan Danya, ƴan ɗanmusa ƴan bauchi sun cika gida dam domin taya murna. Hakama mai jego da jarirai sunsha ƙyau harsun gaji masha ALLAH. Kowa ka gani sai son barka. Amare ma da yawansu suna maƙale da cikkuna kanana sai fatan suma ALLAH ya saukesu lafiya. Kwana biyu da suna AK ya takura dole su Zinneerah suka tattaro suka dawo gidansu, aranar kuma ƴan danya da ƴan ɗanmusa suka koma. Suma ƴan bauchi washe gari suka kama gabansu sai kuna wata ta taso. Zinneerah tayi farin cikin kasancewar gidan cike da jama'a. Dan kuwa Ga mahma ga Mammah da suka koma sashen Farah suka zauna. Ga kuma Mama Ai, ga Yaya Gajeje da Inna. karima ma maƙalewa tai taƙi bin ƴan suna. Sai Tinene da Atine ne suka koma da amaryar baba. Ganin al'amura komai ya daidaita jikinta yayi sauƙi kamar ba yankata akaiba Alhmdllh yasata ƙudirin tunkarar AK da batun dawowar Farah gida. Dan itako tama fi son ta dawo hakanan tunda dai tasan zuwa yanzu ta horu. Dan su Meenal suna bata labari da sukaje da Granny kwanaki duba Farah ɗin abin gwanin ban tausayi. Duk sun fita hayyacinsu ita da Zakiyyan dan horo mai tsanani maimartaba yasa aketa musu batare da sanin kowa ba. Idan ka gansu bazaka taɓa ɗauka su din bane ƴan gayu ƴan ƙwalisa masuji da naira a bankuna. Suna zaune a falonta na farko ita da Yaya Gajeje da Karima, Yaya Gajeje tana shirya ƴan biyu da akaima wankan safe. Zinneerah ma tayi nata dan tana cikin kwalliyarta tamkar ba jego takeba. Har Karima na tsokanarta da tacigaba da kashe ɗauri baban ƴan biyu ya lallaɓo a samo gambo kafin arba'i. “Ya ilahi, dan ALLAH Yaya Karima barmin baki, ina ni ina wani gambo ana zaune ƙalau”. Dariya suka sanya mata, suna cikin dariyarne Mama A'i ta shigo riƙe da hannun Little dake kuka wai ya faɗi. Dubansu duk suka maida garesu, Karima na kamo hannun little ɗin da faɗin, “Yaya akaine Abdul?”. “Faɗuwa yayi, ya shigo da gudu yaci karo da kujera”. Mama A'i ta bama Karima amsa. Baki Zinneerah ta taɓe tana miƙama Yaya Gajeje pampas da za'a sakama Anam. Tace, “Maganinsa kenan, shidai a rayuwarsa yayi gudu, bansan daɗin mi yakeji ba sai kace wani ɗan ƙwallo”. Yaya gajeje ta katseta da faɗin, “Ai tsautsayi dai baya wuce ranarsa, sannu kaji Abdul ka daina gudu wannan gidan naku dake cike da kayan santsinnan, ni kaina babba idan ina tafiya wlhy a hankali nakeyi dan ji nake kamar zan faɗi”. Dariya Karima da A'i sukayi, Zinneerah taɗan murmusa da zancen Yaya Gajejen tana maida hankalinta ga little. “To gudun mi kakeyi?”. Baki ya tura gaba yana makalewa bayan Karima.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182