Chapter 34
Chapter 34
Abba yace, “Koma ki ɗakko zani kizo ki goyashi akwai sanyin safiya”. Cike da kunya ta juya ta koma. babu jimawa ta dawo da zanin goyon a hannu. Maman Sadiq ce ta amshesa ta saka mata a baya dan har yanzu ba wani iya goyon tayi da ƙyauba. Kusanma wannan shine karo na uku kacal da zata goyashi. Dan mafi yawancin lokuta su ƴan biyune ke goyashi ko Maman Halima ko ita Maman Sadiq ɗin. Har Sadiq da Abdull goyamusu akeyi, ƴaƴan maman sakina ma sukan faki ido suzo su ɗaukesa saboda kusan shine ɗan ƙaramin yaro yanzu a gidan, sai yazan abin sha'awa ga kowa banda maman sakina da ko sau ɗaya bata taɓa ɗaukarsaba ma ita. Da ƙyar Maman Sadiq ta samu goyon yayi dai-dai tanata ma Zinneerah ɗin faɗa. Ita dai batace komaiba sai dariya takema a ranta wai mama ta dage da masifa akan ɗan aljanu, sai randa sukazo suka ɗauke abinsu taga yanda kowa zaiyi a gidan ai. Bayan fitar Abba da Maman Sadiq Zinneerah ta hau gyaran ɓangaren nasu kamar yanda ta saba, Sadiq kuma suka shige suna shirin makaranta dan an koma hutu. ★★★★ Haka rainon Little Abdull ya cigaba da gudana kusan kaso biyu a hannun Maman Sadiq da maman Halima ne. Kaso ɗaya kuwa Zinneerah na rabawa dasu Sadiq. A haka sukai arba'in yaron yay ɓulɓul masha ALLAH, ga ƙyawunsa na sake fitowa. Yaro gaba ɗaya bai ɗakko kamannin Zinneerah ba ta fuska sai halittar yatsunsa na ƙafa da hannu da abinda ba'a rasaba. Amma daga basuba kamanninsa daban da nata. Takan zauna ta dinga kallonsa da shiga dogon nazarin ko zata iya gano da wanda yake kamar. Amma sam bata iya hasaso komai ga kamannin nasa. Sosai jikinta ya warke, idanma baka saniba bazaka taɓa ɗauka cs akai mataba. Musamman da yazam bayan dawowarsu gida maman Sadiq da Maman Halima kulawa da gyara na musamman suke mata wanda ita bawani gane inda suka dosa take ba. Abinda kawai ta sani tanajin daɗin jikinta sosai balle yanzu barci take sosai tamkar kasa. Ga lafiyayyen abinci da take samu kuma ga kwanciyar hankali. Sam bata wani tunawa da Inna. Garama Babanta da Yaya Sa'a da Yaya Gajeje. Takanyi kuka a duk sanda sukazo mata ranta koda a boyene. Sai ko Khalipha da har yanzu yake maƙale a zuciyarta. Gashi yanzu Naziru ko gidan yazo baya mata maganarsa ma. Itako kunya ta hanata sake tambayarsa ko yanzu yana samunsa. Bayan tayi arba'in da kusan wata ɗaya Maman Sadiq taga zaman nata baida wani amfani. sai dai taci ta ɗanyi aikin gida ta kwanta barci. Samun Abba tai da shawara akan Zinneerah ɗin ta shiga wata islamiyya dake anan kusa da su ta ƴanmata, inda su Sakina ke zuwa da yamma. To sunayi da safe kuma zuwa ƙarfe ɗaya ga yaran da basa zuwa boko. “Eh shawaranki mai ƙyau ce Hauwa'u, nima kuma maganar fara karatunta dama yana raina. Na bartane kawai Abdul-Mutallaf ɗin ya ƙara ƙwari sannan. To amma tunda dai naga bama itace ke rainonsa ba gara ta fara islamiyyar kawai itama bokon sai a nema mata inda zai dace da ita dan nasan da wuya ace acan tayi karatunma”. Cikin gamsuwa da bayaninsa Maman Sadiq tace, “ALLAH ya saka da alkairi yaya, sai dai duk da bamu taɓa maganar karatu da itaba sai naga kamar taɗanyi acan, dan naga wasu lokutan idan su Abdull na Assignment haka takan saka musu baki harma tayi gyara a wani wajen”. “A'a ikon ALLAH, to kinga kiramin ita dai muji ta bakinta, kinga ai sai mu sami madafar kamawa ko”. Miƙewa tai tana amasa masa da to. Babu jimawa kuwa sai gasu sun dawo tare da Zinneerah. Bayan ta gaida Abba sai yake tambayarta ajinta nawa a makaranta?. Duk da a bazata tambayar tazo mata sai gashi ta saki murmushin da ya basu mamaki. Kanta tsaye cike da zumuɗi tace, “Abba nayi jsce ma ai”. “Ikon ALLAH, to to Alhmdllh. Ashe ɗiyar tawama ƴar boko ce bamu da labari. Amma gaskiya naji daɗin hakan sosai, kuma na yaba ƙoƙarin babanki anan....” Cikin suɓutar baki tace, “Lah Abba ai bama shine ya sakaniba. Inagama Baba fa baisan ina zuwa makarantaba, dan shifa babu ruwansa dani a gidan. Ni saima nayi kwana hudu biyar ban gansaba wani lokacin”. Duk idanu suka zuba mata, a ransu kuma cike suke da zumudi da jin daɗin yanda ta fara sakin jiki da faɗa musu abinda ke ranta. Maman Sadiq ce tace, “To wani guri yake zuwa da har kike kwanaki baki gansaba?”. “A'a mama, yana nan a gidan, kawai dai bansan miyasaba shi bayason ganina ne wani lokacin, wani lokacin kuma daga sallar asuba idan ya fita bai dawowa sai munyi barci”. Babu wanda ya iya magana tsakanin Maman Sadiq da Alhaji. Maman Sadiq dai rayawa take a ranta yaushe al'amarin baban ya taɓarɓare haka kuma?. Dan tasanshi a da mutumne tsayayye akan iyalansa da gidansa. Dan ko talla wannan bai yarda yaronsa ya fita ba. Duk inda akai sallar isha'i kuwa yana gidansa, bazai sake fitaba sai asuba. Da an idar da salla zai dawo gida ya karya sai rana ta haska zai fita kasuwa wajen sana'ar sai da dankalinsa ɗanye da makani....... Tambayar da Alhaji ya jefama zinneerah ce ta katse tunanin Maman Sadiq ɗin ta maida hankalinta garesu. “Karki damu yarinyata, haka rayuwa take kullum cikin tsere-tsere da jarabawa. To amma wanene ya kaiki makarantar?”. Kunyar wanda zata ambata ɗin ya sakata jan lokaci kafin ta bashi amsa. “Abba Babawo ne ya kaini kafin ya koma yace Yaya Karima yake so”. Duk da a dunƙule tai maganar kasancewarsu manya masu hangen nesa sai duk suka gano inda ta dosa kai tsaye. “ALLAH ya saka masa da alkairi”. Abba ya faɗa dajin daɗi. Amin sukace ita da maman Sadiq. Daga haka Abba ya sallameta suka cigaba da tattaunawa shi da matarsa. “Hauwa'u kinga fa'idar shiru da mukai mata akan son sanin bayanta ko? Ina mai tabbatar miki inhar zamu cigaba da binta a haka harma abinda bamuyi zatoba sai munji daga gareta wataran. Kinsan shi yaro tamkar dabba yake, mai kula dashi da mai sake masa shi yake sakewa da shi shima. Dan haka ki sake nutsuwa wajen fahimtarta a hankaki komai da muke buƙata zai fito. Domin a fahimtar danai mata rashin samun sake a inda ta baro ya sakata kasancewa shiru-shiru kamar mara wayo. Amma ras take kuma tanada kwaramniya, sai a hankali zakiga ta hau bisa hanya da ƙyau”. Murmushi maman Sadiq tayi har haƙoranta na bayyana. “Maganarka haka yake Yaya. Dan yanda ma zakaji tana faman shagali dasu Sadiq idan na barsu su kaɗai ya isa tabbatarwa. Idan kaji bakinta cauy-cauy baka taɓa cewa itace ke zuba zance”. Dariya shima Abban ya sakeyi. “Ahaf kaɗanma kenan. Bayan takurar data taso a can harda cikin yaron nan ya sake dankwafe dukkannin kuzarinta da karsashi. Amma zata ware tsaf ta bama kowa mamaki. Naga alamar kuma tanason karatu ma sosai, dan jin daɗinsa ya sakata bamu labarin abinda bamu tambayetaba ma”. Haka suka cigaba da hirarsu cike da fahimta dajin daɗi. Yayinda Zinneerah kecan tana tsallen murna zata koma makaranta. Harda ɗaukar Little dake barcinsa ta hau masa rawa. Aiko ya farka ya birkuce mata kuma.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182