Chapter 85
Chapter 85
daga nan. Shima ƙaramar dariyar yayi yana ɗagota. “Uhm kinga barni naje mu gaisa dasu Granny inada meeting 11am”. Duk da zuciyarta ta sosu da zancensa sai ta daure ta kanne, koba komai anci mata lokaci ai tunda gashi lokacinta sai ta raba dasu. Da basa gidan kuwa itace zata kasance da shi har lokacin fitar tasa ta cika. A tare suka fito dan tayi alƙawarin sai dai suci lokacin nasu tare itama dan bazata barmusu ba. A dining suka iske su Hajiya iyan zasuyi zaman karyawa da abincin da Khalipha yaje ya sayo. Mai aikin Farah kuma ta shirya musu shi a dining tamkar a gidan aka girka shi. Khalipha na daga tsaye bayan Granny suna magana dan shi fita zaiyi. Juyowa yay saboda jin ƙamshin turaren yayan nasu da takun sa da baya ɓoyuwa ga duk wanda ya sanshi. “Barka da asuba Yayanmu”. Ya faɗa dai-dai suna ƙarasowa wajen. Hannunsa AK ya kamo cikin nasa yana faɗin, “Halan yanzu ka tashi kake kiran asuba likita?”. Fuskar Khalipha da murmushi yace, “Ai ni harma fita nayi naga gari Yayanmu, kai nedai nake tunanin yanzun ka tashi shiyyasa na faɗa”. Kafin AK ɗin yace wani abu Granny dake kallonsu cike dajin daɗi da sha'awar yanda shaƙuwarsu take wanzuwa cikin ƙanƙanin lokaci tace, “Ni nama zata yau bazai fitaba ganin har wannan lokacin bai fitoba. Bayan kuma nasansa shi baya saɓa lokaci”. Kallonsa ya maida ga Hajiya Iyan tare da jan kujerar kusa da ita ya zauna. “Yau meeting kawai nake da shi Granny shiyyasa na koma barci bayan sallar asuba. Ina fatan kin tashi lafiya?”. “Lafiya lau na tashi, sai dai waɗanan akkunayen da suka cikani da surutu jiya”. “Ai kece kika gayyatosu”. Ya bata amsa idonsa na sauka akan Zinneerah dake facing kujerar daya zauna. Tun zuwansa wajen tai ƙasa da kanta tana juya cokalin hannunta cikin abincin da sam ba daɗi yake mataba, wai a hakanma sai da Khalipha ya zaɓo musu wanda yasan zasu iyaci suji daɗinsa tunda ba sabawa sukai da abincin nan ba. Janye idanun yayi cike da basarwa yana ɗaukar tea ɗin Hajiya iya ya fara sha. Hakanne ya bama Jamal damar fara gaidashi. Sai Meenal ma ta gaisheshi. Itama Bahijja haka. Zinneerah ce ƙarshen gaishesan batare data yarda ta kalli inda yakeba. Dukansu amsa musu yay kamar yanda ya saba cike da rashin sakewa. Hakan da yayi yayma Farah dake bayansa tsaye daɗi, tai wani ƙasaitaccan murmushi da ɗora hannunta kan kafaɗarsa tana sake matsowa jikinsa. Cike da yanga da ƙasaita tace, “Za kaci wani abune anan ɗin?”. “No, shayin Granny kawai ya isheni”. Daga haka ya maida hankalinsa kan hajiya iya ya fara magana ƙasa-ƙasa batare da kowansu yaji mi yake faɗa ba. Hakan kuma sai ya soki zuciyar Farah tabar wajen fuska a haɗe. Khalipha ya danne dariyarsa da ƙyar yana binta da kallo, tana gab da shigewa yace, “Kunga nikam bara na wuce school zanyi latti”. Ɗagowa AK yayi ya dubesa. “No ka jira na kammala mu wuce tare kusa da school ɗinku zanje nima”. “Okay thanks you Yayanmu”. Khalipha ya faɗa yana jan kujerar data rage ta dining ɗin ya zauna. Farah ko dake ƙoƙarin shigewa ɗakin jin zancen nasu ya sakata dakatawa. Kamar zata juyo sai kuma mita tuna oho mata ta cigaba da tafiya harta shige ɗakinta tana taunar lip ɗinta na ƙasa da ƙarfi. Sosai zamansa shi da Khalipha a wajen ya saka Zinneerah shiga takura, garama Khalipha tana ɗan sakewa da shi. Amma wannan shugaban tsare gidan da ƙasaitar gaba ɗaya tare mata iska yake idan yana a waje. Sai dai kuma takan tsinci kanta cikin jin daɗi dan tana kallon little ɗinta tattare da shi. Yanzunma murmushi ta sake a bazata saboda faɗo mata a rai da Little yayi, dan hutun nan na kwanaki huɗu da tayi ba ƙaramin shaƙuwace ta sake shiga tsakaninta da yaron ba. Har takai tanajin kamar ta ɗakkosa su taho tare. AK da sarai yaga murmushin nata ya ɗan kafeta da kallon sakanni a kaikaice ya ɗauke kansa, a ransa kuwa tambaya yake komi ya bata suga?. Baida mai bashi amsa dan haka ya miƙe dayin ɗan hugging Hajiya iya ta gefe ya sumbaci hannunta daya kamo. “Kimin addu'ar cin nasara, dan zamane mai muhimmanci zanje Granny”. Ya ƙare maganar idanunsa na faɗawa cikin na Zinneerah data ɗago a bazata. Yanda ya juya idanun da wani salo ya sakata saurin maida nata ƙasa ta risinar zuciyarta na matuƙar harbawa. Kasancewar babu wanda ya lura da abinda ya faru suka rakashi da addu'ar samun nasara harsu Jamal. Zinneerah dai akan laɓɓa ta fisgo tata addu'ar da ƙyar ta furta. Hayanr fita ya nufa yana saka rigar sanyinsa a saman suit ɗinsa fuska ɗauke da wani ɓoyayyan munafikin murmushi. Suna ficewa Zinneerah ta saki ajiyar zuciya. A take su Jamal duk suka kalleta. Hajiya iya kuwa ta saki wata ƴar dariyar data basu mamaki itama, sai dai koda suka maida dubansu gareta sai ta basar. Babu wanda ya sake magana dan dokace hakan ga Granny indai anacin abinci. Sai da suka gama ita dasu Bahijja suka gyara wajen domin taimakawa mai aikin da suke ganin kamar aikin gidan ya mata yawa saboda ƙaruwarsu. Yau ma dai hirarsu suka sha tare da kakarsu. Daga ƙarshe Zinneerah ta bama Hajiya iya tsarabar mmn sadiq tare da saƙon zungureriyar wasiƙa da batasan ta micece ba itama. Hasalima sai yanzu da ake buɗe kayan duk suka gani. Jamal ya ɗauka zai buɗe Hajiya iya ta girgiza masa kai da amsa. Babu musu ya bata. Koda ta amsa itama sai ta miƙe taje ta adanata dan tanaji a ranta abune mai muhimmanci a ciki mmn sadiq ɗin ta rubuto, dan dama ɗazun da sukai waya da Baffah yake sanar mata Abbansu Sadiq ya sanar masa yanason ya bashi lokaci zaije har gida suyi wata magana mai muhimmanci. Amma shi yanata juya abin a ransa da tunanin wace maganace haka? Shiyyasama ya sanar mata. To a yanzu ganin wannan wasiƙar ya sakata jin maganar da Abban zai faɗama Baffah lallai tanada alaƙa da takardar kenan. Wannan hasashen ya sakata adana takardar sai ta nutsu sannan ta duba dan itama tayi karatun boko duk da bamai tsaho bane a wancan lokacin iyakartama firamare aji biyar aka aurar da ita...............✍ *_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇 0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182