Chapter 59
Chapter 59
makaranta. Kasancewar dama bata fara aikin da wuriba sai gashi har Hajiya iya ta shigo domin sallar magrib bata kammalaba. Sai kusan sha ɗaya ta gama lokacin hajiya iya ta jima dayin barci mai cike da mafarkin yaron da Safiyya ta kawo musu a hoto, takan dai tashi tai salla idan lokaci yayi. Su meenal kuma sunɗan lekota, sanin hajiya iya idan ta kwanta batason surutu yasa suka fice suka barta ita kaɗai ta cigaba da aikinta. A falo kuwa hirarsu suka cigaba dayi bayan tasowar hajiya iya. Dan duk sun barma kansu cewar kamannine kawai da akan samu a rayuwa tsakanin wani da wani koda babu alaƙar jini saboda hikimar UBANGIJI. Basu wani jimaba suka fice duk da Moos'ab yaso ganin Zinneerah kafin ya wuce ɗin. Rashin samuwar hakan ya sakashi haƙura kawai. Tun daga wannan ranar babu wanda ya sake tada zance akan hoton yaro, sai dai abin na nan maƙale a zuciyar Hajiya Iya ta kasa mantawa. Tanason yin maganar kuma wata zuciya na kwaɓarta akan kamannine kawai. Idan kuma tace zata kawoma zuciyarta wani tunani daban ya zata alaƙanta al'amarin ma to. Hakan yasata tsuke bakinta ta barma ranta komai kawai. kwanaki sun cigaba da shurawa a hankali sai ga Khalipha da Adnan na cika kwanaki goma da zuwa. Ko kaɗan Zinneerah ta kasa sabawa da kasancewar sa a gidan duk da a kwanakin nan bai cika zamaba kullum suna hanyar Jigawa gonar da zaiyi noman shinkafa. Sukan fitama kafin su su fito, wani lokacin kuma sai sunyi barci suke dawowa. Wannan dalilin yasa takanyi kwanaki uku biyu ma bata sakashi a idontaba har Khalipha ɗin da take marmarin gani a ko yaushe. A kwanakin nan daya ɗauka gaba ɗaya hidimar gyaran ɗakinsa ta dawo kan Zinneerah. Kullum ita yake cewa taje ta gyara masa ɗaki. Bata damuba dan dama ta rigada ta saba. Idan ta ganshi tsoro na matuƙar kamata, dan kullum abubuwan daya dangancesa suna sake danganta kansu da abinda sam ta kasa gaskatawa. A randa suka cika kwanaki goma sha uku a gidan basuje gona ba, amma duk da haka babu wanda ya sakashi a ido sai yamma. Yana ɗakinsa yana harkokinsa na business a lap-top. Zinneerah, Meenal, Bahijja sai Jamal na zaune a falon hajiya iya Yah Khalipha ya shigo. duk sannu sukai masa ya amsa yana zama kujerar dake facing ɗin Zinneerah da Bahijja. Cikin kafe Zinneerah ɗin da idanu ya miƙa mata ledar hannunsa yana murmushi. “Ƙanwata yau dai ga wayarki na cika alƙawari”. Kafinma ta kai ga yunƙurawa amsar wayar Jamal yay azamar zuwa ya amsa yana washe baki. A take suka rufi akan wayar suna tayata murna duk da ba irin tasu Meenal ɗin bace ba, amma itama ta haɗu. Tasowa Zinneerah tai tsam inda yake takai tsigunne kanta a ƙasa tana faɗin, “Nagode sosai Yah Khalipha, ALLAH ya ƙara buɗi mai albarka”. Kansa ya jinjina mata yana sake faɗaɗa murmushinsa. Sai kuma ya miƙe ya fice zuciyarsa na bashi ƙwarin gwiwa akan yau ya tunkareta da zancen nan. Dan yauɗin kawai ke garesa Yah Adnan yace nanda kwanaki huɗu idan ALLAH ya kaimu maybe zasu wuce Abuja. Daga can kuma bazasu dawo Kano ba London zasu koma zaiyi wasu uzirinsa kafin ya dawo akan zancen auren su Ni'ima da ayanzu haka an tsaida rana da kuma maganar Company da yake tunanin buɗew na shinkafa. Binsa da Kallo Zinneerah tayi ƙwalla na cika mata idanu, sai kuma ta miƙe tsaye tana murmushi saboda wani abu data tuna. Idanuntane suka sauka akan Yah Adnan dake tsaye bakin ƙofarsa da waya a kunne yayi wani kicin-kicin da fuska............✍ *_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 *_★ MADUBIN ZUCIYA_*💖 *_★ DALAAL_*💝 *_★ UBAYD MALEEK_*💓 *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇 0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafarma iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* __________________________ *_ina 'yan uwa musulmai masu kishin addinin islama???_* *_maza ku matso ga wani aikin lada ya samu_* *_Ɗanku kuma dan uwanku kuma qaninku wato ABDURRAHMAN, yaro mai hazaqa, ƙwazo da tarin baiwa, gami da kwadayin haddace littafin Allah mai tsarki, ya bude YOUTUBE CHANNEL nashi na qashin kansa, ku tallafa masa ta hanyar shiga wannan shudin rubutun ku danna masa subscribe, ba abunda xai rageku dashi saima samun dimbin lada dalilin KARFAFA MASA GWIWA, MUN GODE 🙏🏽🙏🏽🙏🏽_* 👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽 https://youtu.be/WWIGq5Jbtb0 _______________________ *Page 22* .........Cikin sauri ta haɗe murmushinta dayin diri-diri na alamar rikicewa. Dan wani irin kallo da take kasa fassarawa a duk sanda yay matashi ya watso mata yanzuma ya ɗauke kansa fuskarsa na ƙara tsukewa fiye da yanda ya fito. Sum-sum ta juya gasu Bahijja da suma sukai tsitt daga ihun da sukeyi na murnar wayarta zata zauna yace, “Haɗomin black tea yanzun nan”. Daga haka ya juya ya koma ɗakinsa. Da sauri duk suka kalli Zinneerah da itama kallonsu take. Meenal tace, “Wlhy ki tashi kafin yace kin ɓata masa lokaci”. A take idon Zinneerah ya fara tara ƙwalla. Dan wannan shine karo na farko da ya sakata irin wannan aikin bayan gyaran ɗakinsa. Bahijja tace, “Kinsan mi zakiyi?” Zinneerah ta girgiza mata kai da sauri. “Kije kima Baba Rahi magana ta haɗa miki, dan tafi kowa sanin abinda yakeso a nan gidan bayan Granny. ALLAH yasa basu tafi ba, tunda ba gani yayba ki fiske abinki ki kai masa kawai a rabu lafiya. Dan shi inhar ya sakaka abu bakayi dai-dai yanda ya buƙataba ka shiga uku”. Jin abinda Bahijjan ta faɗa ɗinne ya sake tsurar mata da ciki, amma shawarar saka Baba Rahi ta haɗa matan ya sata jin sassauci. Da sauri ta miƙe zuwa kitchen, sai dai wayam babu baba Rahi a ciki. Tai saurin kallon agogon dake a kitchen ɗin wanda ya bata tabbacin Baba Rahi ta wuce gida dan ba'a nan take kwanaba daman. A take ƙwallan da take maƙalewa suka silalo mata. Jiki a sanyaye ta ɗiba kayan ƙamshi tasa a turmin ƙarfensu ɗan ƙarami ta hau dakawa. Cikin ƙanƙanin lokaci ta gama dafa shayin daketa uban ƙamshi a kicin ɗin, sai dai duk wannan ƙamshin nasa dazai iya saka mai kallo buƙatar sha ita a tsorace take. Ƙaramin flask ta samu ta juye tare da ɗorawa a tire ta saka kofuna biyu da mitsilin bowl data zuba suga a ciki ta ɗakko ta fito tana karanto addu'ar nasara a cikin ranta. Bata iske kowa a falonba su Jamal sun gudu, hakanne ya sake ɗarsa mata tsoro a cikin rai ta nufi ɗakin tamkar an daddoke mata gwiyawu. Sai da tai sallama kusan sau huɗu
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182