Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 23

Chapter 23

Makauniyar Kaddara Book 1 Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

ta hayayyaƙoma Uwargidan nasu..... “Yaya! Yaya! Ƴar ayi jikan nasaba”. Muryar mai-gidan dake shigowa ta katse masifar Sauden ta koma ƙunƙuni ciki-ciki. Baibi takantaba sai uwargidan tashi dake masa sannu ya duba. “Mike faruwa kuma daga dawowarku Binta?”. “Babufa komai Alhaji, fitinace irin ta Saude da baƙarewa take a gidan nan ba. Kawai dan Maman Sadiq bata fito ba shine take tsogumin batazo ta ɗora abinciba wai lokacin kaima yara makaranta ya kusa”. Ɗan tsaki yayi yana girgiza kansa. Yace, “Ina ita Hauwa'un take?”. “Tana ɗakinta, inaga dai akwai abinda ke damuntane, dan tunda muka baro asibitin naga yanayinta ya canja, na bartane muzo gida taɗan huta dama ko wani abune ya tada hankalinta acan ɗin tunda wajene bana daɗin rai ba”. Baice komaiba ya nufi ɗakin Maman Sadiq ɗin, wadda duk tanajin mi'ake a tsakar gidan amma taƙi yin ko tari dan abinda ya isheta ya girmi fitinar Saude. Labulen ya ɗaga yana dubanta daga bakin ƙofar, yitai kamar bata gansaba, hakanne yasa ya shigo ciki yana faɗin, “Hauwa'u lafiyarki kuwa”. Juyowa tai ta kallesa tamkar yanzune tasan da zuwansa. Tace, “Ashe ka shigo? ALLAH yasa dai lafiya?”. “Ai ke za'a tambaya ko lafiya Hauwa'u? Mike faruwa ne?”. Tamkar jira take ya tambayeta sai ga hawaye sharrr. Zumbur ya miƙe daga ɗan zaman da yay a hannun kujera yace, “Subahanallahi, wai mike faruwa ne? Ko wani abun ya faru acan inda kukaje dubiyan?”. Hawayen ta share, tace, “Lallai Alhaji akwai matsala wlhy, dan ALLAH inason na sake komawa asibitin nan yanzun”. “Ki koma asibiti kuma? Akan wane dalili to?. Kimin bayanin dazan gane mana”. Wasu hawayen ta sake sharewa. Muryarta na rawar tahowar sabon kuka tace, “Alhaji yarinyarnan da mukaje dubawa wadda Nazirun ya kaɗe wlhy kamar Zinneerah, kai inamji a jikina itace duk da kuwa rabon dana ganta tun tana ƙarama”. Shima kansa da mamaki yace, “Zinneerah dai tamu dake a Danya?”. Cike da ɗanjin nauyinsa ta gyaɗa kanta, dan shi mutumne mai kara, duk da ɗan uwantane dama can, auren zumincine akai musu bayan aurenta ya mutu, ya sota tun tana budurwa ALLAH baiyi zata zama matarsaba a lokacin sai da ta fito yace shifa yana sota har yanzun. Da farko taso ta tirje dangi sukai mata caa akan rashin dacewar hakan. Dan kowa yasan irin son da ya nuna mata. Haka dole ta haƙura akayi aka kawota nan Kano gidansa dan dama can anan yake zaune shi shekara da shekaru, to gashi yanzun har ALLAH ya azurtasu da ƴaƴa uku duk maza. Tana kuma samun kulawa da soyayyar mijinta mai tsafta da saka kwanciyar hankali, ga Uwargidanta mutuniyar kirki, Saude ce dai sai a hankali, dan dama tun farko fitinar Sauden tasata son zamewa daga auren nasa..... “Wai tunanin mi kuma kika tafi haka ne?”. Kallonsa tai da sauri tana sauke ajiyar zuciya. Ya ɗan girgiza kansa kawai yana miƙewa. “Kinga ki kwantar da hankalinki tunda dai tana asibitin babu inda zataje, bara na kira Nazirun anjima yazo sai mu koma insha ALLAH dan wannan ba al'amarin da za'ai wasa bane”. Cikin jin daɗi tace, “To Yaya ALLAH ya saka da alkairi”. “Saboda ƴarki ce ke kaɗai kikemin godiya kenan?”. Ƙasa tai da kanta tana murmushi. “A'a kayi haƙuri bankai canba”. Fita yay yana murmushin shima. Saude dake laɓe a jikin Window ɗinta tana irga mintunan shigarsa ɗakin taja tsaki ganin ya fito yana murmushi. Afili tace, “Shegiya munafika, zanyi maganinki a gidannan wlhy. Oho ita dai maman sadiq bama tasan tanaiba, dan bayar fitar maigidan fitowatai ta ƙara gawayi a wuta ta ɗora ruwan abinci, dan dama tunkan su fita tayi miya shiyyasa bata damu da tsegumin Sauden ba ashe. ★★★★ A asibiti kam shiru-shiru Khalipha bai dawoba har lokacin yin barcin ranar Zinneerah yayi tasha magani ta kwanta. Bata tashiq farkawaba sai bayan sallar la'asar. Ganin lokaci yaja ya sata miƙewa aɗan harzance ta shiga toilet ɗin dake a ɗakin. Alwala tayo ta fito, bayan idar da sallar ne Salima ta shigo dan bata abinci kamar yanda Khalipha ya rataya mata alhakin yin hakan ga Zinneerah. Itako bala'in son da takema Khalipha yasa bata iya ƙetare buƙatarsa a rayuwarta, shiyyasa take bama Zinneerah kulawa sosai dan duk zatonta yanada alaƙa da zinneerah ɗinne musamman dataga an kawo zinneerah ɗin ɗaki na musamman ita kaɗai an ajiye. Zinneerah na tsaka dacin abincinne Salima na mata hira tana ɗan murmushi sukaji sallamar Khalipha bayan yayi ɗan knocking. Saurin jan hijjab Zinneerah tai ta saka, Salima ma ta gyara zamanta dana ƙaramin hijjab ɗinta tana amsawa. Shine ya fara shigowa ɗakin tamkar ɗazun, sai Naziru biye da shi, wani da suke tsananin kama da Nazirun na bayansu, sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci ya girmi Nasiru ɗin dan ba yaro bane. Sai matan ɗazun biye da su a baya, amma banda matar Naziru. Matar ɗazun da taji suna kira da Maman Sadiq ta ƙaraso gaban gadon sosai batare da tama saniba. Hannu takai bisa kumatun Zinneerah jikinta na wata irin tsuma da karkarwa. Ko shekara dubu tai bataga wannan halittarba tayi imani da ALLAH randa suka haɗu saita gane abarta. Tunda tabar ƙauyen Danya cikin gushewar hankali dana tunani har zuwa yau ɗinnan bata daina kwana da mafarkintaba da tashi da tunaninta kuma. Ta kai ƙasa durƙushe hawaye na silalo mata a kumatu. Tabar ƴarta da ƙarancin shekaru hannun kishiya mai ƙarancin imani dana tausayi badan ranta yasoba, sai dan anfi ƙarfinta kawai. Yau kuma sai gata a inda bata taɓa zatoba ko tsammani a shekarun girma.... “Zinneerah!”. Ta ambata da wani irin rawar murya dana harshe. Ganin Zinneerah ta kasa magana sai kallonta kawai da takeyine kamar ɗazun ya saka Naziru faɗin, “Maman Sadiq ki kwantar da hankalinki, insha ALLAHU itace ma”. Idanunta da hawaye ke kwarara ta ɗago ta kallesa, taɗan saki murmushin ƙafin hali tana miƙewa tsaye sosai. “Nasiru indai har yanzu ba ƙwaƙwalwata ce bata gama dai-daitaba to wannan kam Zinneerah ce, dan naji hakan a jikina duk da kuwa bata amsa sunan dana kirata da shi ba”. Maman Halima da sukazo tare yanzunma ta matso gaban gadon itama ta zauna kusa da Zinneerah da alamu suka nuna tamkar bata a cikin hayyacinta. Sai da ta riƙe mata hannune tai firgigit alamun ta dawo cikin hayyacinta. Ƙasa tai da kanta saboda wani irin bugu da ƙirjinta ke mata ainun, Maman Halima ta katse shirun ɗakin da faɗin, “Ƴammata minene sunanki?”. Babu wanda yay tsammanin zata amsa. Sai ji sukai a bazata tace, “Zinneerah”. Wata irin nannauyar ajiyar zuciya maman Sadiq ta sauke, yayinda ɗunbin mamaki ya kashe Khalipha da Naziru, musamman da suka tuna randa sukaita ƙwaƙwar jin sunan nata amma tai musu shiru.. “Masha ALLAH Zinneerah daga ina kike? Ina nufin a wane anguwa iyayenki suke?”. Shiru kamar bazata amsa ba yanzu. Sai kuma zuwa can tace, “Ba'anan nake ba”. Cike da zumuɗi maman Sadiq tace, “Daga wane gari kike?”. Ɗagowa tai tana kallonta na tsawon kusan mintuna biyu, sai kuma ta maida kanta ƙasa tana sauke ajiyar zuciya. Cikin suɓutar bakin da bata shiryaba tace, “Danya”. Gani kawai sukai maman sadiq ta zube kan kujerar roban dake a gaban gadon ta fashe da kuka tana faɗin, “Wlhy itace, Zinneerah tace”. A yanda tai maganarne ya sakasu jin wani irin tausayinta

Table of Contents

Chapters

182 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182