Chapter 112
Chapter 112
ta shafa tana murmushi. “Mamaki ko?”. Ta faɗa tana kamo hannunsa cikin nata. Cikin ɗacin murya yace, “Amma Granny yanz......” “Shiii” ta faɗa tana girgiza masa kanta alamar kar yace komai. Badan yasoba dole yay shiru yana binta da kallo. Barin wajen Zinneerah tayi dan kasancewarsa a wajen yasa taji ya cika mata fili kamar yanda takeji a duk sanda yana a waje. Handbag ɗin Hajiya iya ta ɗauka tabi bayan su Bahijja da har sun shige, barci da gajiyar da take ciki ya haddasama tafiyar tata sanyi sosai fiye da ko yaushe. Shigowar Khalipha ya sanya Ak dake binta da kallo juyawa ya dubesa. Murmushin ƙarfin hali Khalipha yayi da matsowa ya rungumesa yana jera masa kalmar “I'm sorry yayanmu”. Komai baice masaba, sai kansa kawai daya ɗan kaɗa yana miƙewa. “Dare yariga yayi nisa, yakamata ku kwanta ku rage gajiya”. Daga haka ya nufi ɗakinsa ransa duk babu daɗi da dawowar tasu, dan shi ba haka yaso ba. Ƴan gidan babu wanda yasan da dawowar ƴan london sai washe gari, a take suka rikice da murnar dawowar Granny, yayinda Baffah kuma keta mamaki, sai dai dariyar da yaga Huzaifa nayi suna magana da Khalipha ƙasa-ƙasa ya sashi fahimtar sune suka ƙulla komai. Uffan baiceba ya shiga layin ƴan murnar ganin hajiya iya shima. Sai da duk suka lafa da gaishe-gaishe da tambayar jiki sannan su Zinneerah suka fito suka gaida Baffah suma. Cike da jin daɗi da kulawa yake amsa, dan ƴan kwanakin da sukai acan harsun ƙara canja kala. Sai da kowa ya nutsa sannan Baffah ya samu zama da Granny shi da Mommy da hajiya iya keta murnar ganinta da kiranta autarta. Yanda Mommy ke nane da hajiya iya sai hakan ya birge Zinneerah har little ɗinta ya faɗo mata a rai da mamanta itama da baba. Murmushi tayi a zuciyarta tana mai begen ganinsu. Kamo hannunta Mommy tayi ta zaunar kusa da ita tana faɗin, “Masha ALLAHU, lallai yarona ya iya zaɓe, dan ɗiyar tawa kam badaga nanba”. Kunyace ta kama Zinneerah duk da bata fahimci inda zancen na Mommy ya dosaba. Sai kuma can gefen zuciyarta ke raya mata ko dai Moos'ab ya faɗa musu wani abune?. Sosai gabanta ya faɗi, taɗan saci kallon Khalipha dake ƙoƙarin fita zuciyarta na bugawa da sauri-sauri. Bata gama kammala tunanintaba ta miƙe ganin kowa ya fice a yaran sai ita kaɗai. Itama ficewa tai tabar su Granny dan taga alamar magana zasuyi. Kayan barcine wando da riga a jikinta, sai dai ta ɗora hijjab mai hannu a sama kalar pink mai haske daya kai mata har gwiwa, gashi ya ɗau guga dan da zatai salla ta cirosa ta saka. Fitowarta dai-dai da shigowar AK ɗauke da little a hannu, kamar daga sama taji muryar gudan jininta na ambaton, “Aunty! Aunty!”. Da sauri ta ɗago ta kalli hanyar shigowar duk da zuciyarta bata yarda da abinda tajin ba. Cikin sa'a kuwa sai a kan little daketa zillo daga jikin AK alamar zaizo wajenta. Shiko yaƙi sakinsa sai ma kafeta yay da idanu kai tsaye hankalinsa kwance. A hankali ta motsa laɓɓanta wajen ambaton “Little” da mamaki shimfiɗe a saman fuskarta. Ga wani bugawa da ƙirjinta keyi saboda matsanancin kamannin yaron nata da Yayansu da suke ƙara bayyana kansu a koda yaushe. Musamman yau da fuskarsu ke gab da juna kuma little ɗin tamkar ya ƙara girma da wayo. Duk yanda taso ɗaga ƙafarta zuwa garesu ta amshi little ɗin ta kasa, haka ta cigaba da tsayuwa harshi ya fara takowa a hankali yana nufota. Tsitt falon yayi kowa ya zuba musu idanu ƙasa-ƙasa, musamman su Mas'ood da sukasan mike tsakani yanzun. Su Jamal dai yanda Yayan nasu ke kallon Zinneerah ɗinne da yanda tayi itama ya basu kala suka tsaya kallo dan son ganin mike shirin faruwa. Gab da ita ya tsaya, batare da yayi maganaba ya kamo hannunta ɗaya ya ɗaura na little akai. Kafin ya saki yaron gaba ɗaya gareta yana motsa laɓɓansa a hankali yanda ita kaɗai zata iya jinsa, itama ɗin sai da taimakon motsin laɓɓansa. “Sai na tsone wannan idanun”. Sosai taji wani irin shock saboda jin hannayensa da nata na neman sarƙewa waje guda lokacin da yake sake mata little, magarsa da yanayin da ta ji ya sata tura baki da ɗan juya kwayoyin idon dazai tsokale batare da tasan tayiba. Leɓensa na ƙasa ya wani cije ganin yanda ta tura baki ga idanunta sun fara tara ƙwalla suna wani farfar. Ya saki wani munafikin murmushi da ya nema sakata sakin little ɗin ƙasa yana ja da baya. Da wani irin slow tafiya ya raɓata ya wuce ƙamshin turarensa na sake bugun hancinta. Babu shiri ta ƙanƙame little jin zai suɓuce mata. Suko su Saifudden suka shiga sunne kawuna ƙasa suna dariyar shaƙiyanci ƙasa-ƙasa. Su Bahijja kuma da basusan dawan garinba bakuna suka saki cike da mamaki da al'ajabin abinda Yayan nasu yayi yanzun, amma ya fiske ya wucesu tamkar baisan da zamansu a wajen ba. Yana shigewa ɗakin Hajiya iya su Mas'ood suka shiga tafawa da juna. Khalipha yay ƙasa da kansa yana sakin murmushi da ƙoƙarin kauda komai dake ransa dan yasan dai ta ƙare. Koda ace ya furtama Zinneerah so Yayansu ya nuna yanaso wlhy zai iya sadaukar masa. Ballema ALLAH ya soshi bai taɓa koda nuna mataba duk da kuwa tun sanda ya haɗu da ita a gidan tai caraf da zuciyarsa. Dan bazai saka haɗuwarsu ta farko a lissafi ba, saboda kallon matar aure yake mata. Duk abinda yay mata kuma tausayine a wancan lokacin ba so ba. Moos'ab ma dai daurewa yake matuƙa wajen danne komai, dan yayi alƙawarin koda yaƙi sai ya cire Zinneerah a ransa ta koma matsayin matar Yaya da ƙanwarsa har cikin zuciya. Zinneerah kam ƙanƙame little tayi a jikinta da sauri mamakin abinda Yayansu yayi na neman kasheta da ranta. Ta bisa da kallo harya shige ɗakin hajiya iya ko waiwayosu baiyiba. “Aunty!!” little ya faɗa da ƙarfi cikin kunnenta yana bubbuga mata kafaɗa. Babu shiri ta juyo garesa tana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Sai kuma ta saki murmushi da lakace hancin little ɗin tana faɗin, “Haba bawan ALLAH kashemin dodon kune zakayi ne? Waya kawoka nan?”. Bata da mai bata amsa. Danshi little ma dariyarsa ya saki maiban sha'awa saboda lakace masa hanci da tayi, ya kwanta a kafaɗarta yana zagayo hannunsa ɗaya a wuyanta zuwa ɗayar kafaɗarta. Hannunta ta ɗora akan gadon bayansa tana shafawa a hankali da murmushi, murya ƙasa-ƙasa tace, “I miss you my heart, ALLAH ya albarkaci rayuwarka, ya baka kariya a kowanne sakan na agogo”. A ɗakin hajiya iya kuwa koda AK ya shiga tararwa yay su Baffah na magana. Baffah na zayyanema Hajiya iyan yanda sukai da Mammah. Gaishesu yayi, duk suka amsa masa da kulawa. ya yunƙura da nufin fitowa ya basu waje Hajiya iya ta dakatar dashi ranta a ɓace dajin abinda Mammah tazo tayi. Komawa yayi ya zauna kansa a ƙasa dan yaƙi yarda ya kalli kowansu, bayason suga damuwar dake kwance a cikin idanunsa. Cikin kaushin murya Hajiya iya tace, “Ina maka murna da samun yarinyar ƙwarai kamar Zinneerah moddibo, itama kuma ina tayata murna da samunka matsayin miji. duk da har yanzu zuciyata ta gaza hasaso ko tunanin ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182