Chapter 138
Chapter 138
Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* _________________________ *Page 54* ...........Duk yanda taso dojewa a baya doleneta ta yarda suka shigo sashen nata a tare, kusan duk sai da suka ɗago suka kallesu jin sassanyar muryarsa na sallama. Bayansa ta koma ta maƙale saboda kunya da taji na iyayenta da ƴan uwanta. Gani take kamar kowa zai gane abinda ya faru kafin su shigo, Aunty Salima ce ta bashi kujerar da take zaune. Babu musu ya zauna yana musu sannu da zuwa fuskarsa a ɗan sake. Cikin mutunta juna sukai gaisa. Yana musu godiya suna masa, tare da jera musu addu'oin zaman lafiya mai ɗorewa na har abada da zuri'a mai albarka da nagarta. Gwaggo Maryama ce tai masa bayanin kowa a wajen da matsayinsa wajen Zinneerah, ya ƙara musu godiya yana ambaton masha ALLAH. Kafin ya miƙe bayan suma su Meenal sun gaishesa. Sai da yazo saitin Zinneerah dake tsaye yay magana ƙasa-ƙasa yana raɓata ya wuce. “Ki sameni idan sun tashi tafiya”. Binsa da kallo kawai tai ta gefen ido dan ya riga ya shige bai bata damar amsa masaba. Hankalinta ta maida akan ƴan uwanta dake yabonsa da sake jera masa addu'an fatan alkairi. Ita dai uffan bataceba sai zama data sakeyi. Sun ɗan ƙara taɓa hira kafin su mike domin ganin ɗaki. Lungu da saƙo babu inda basu shigaba, Sa'a nata santi da ƙarajin daɗin sauyin rayuwa da ƴar uwarta ta samu. Hakama Yaya Gajeje bakinta yaƙi rufuwa dan farin ciki. Karima da Atine kam dai anata naɗar rahoton da za'a kaima Inna fuska a taɓe. Babu wanda ya damu dasu, dan ƴan ɗan-musan ma dasu Gwaggo Laritu sai faman yabawa sukeyi abinsu. Bayan sun gama zagayensu sukai haramar tafiya, maganar cewa ta sameshi yasata cewa su jirata tana zuwa. Duk da ranta cike yake da fargabar abinda ya faru ɗazun ga kunyarsa haka dole ta nufi sashen nasa again. Yanzu kam bata tsaya knocking ba sallama kawai tayi da murɗa kofar ta shiga, yana tsaye alamar shirin fita yake ta shigo bayan ya amsa mata sallamarta da bata izini. Kanta a ƙasa saɓanin shi da yake kallonta kai tsaye, yanda batai magana ba shima baiyiba, sai ma ya ɗauke kansa daga kallon nata yana ƙoƙarin tattare takardun daya baza a falon. Ganin haka yasata faɗin, “Yayanmu zasu wuce”. Bai amsataba sai da ya gama abinda yakeyi, ƙananun ledoji guda biyu dake a saman kujera ya nuna mata, “Ki bama Gwaggo Maryam ɗaya taba ƴan ɗan-musa, ɗayan ki bama Gwaggo ta danya nasune suma”. Ɗaukata tai tana kaiwa tsuggune. “ALLAH ya saka da alkairi ya ƙara arziƙi mai albarka da amfani, ya cigaba da baka kariya a dukan al'amuranka”. Har cikin ransa yaji daɗi da farin cikin wannan addu'a tata, dan haka yay ɗan murmushi yana amsa mata da “Amin, nagode”. Kamar yanda ya bata umarni haka ta aikata, aiki suka shiga godiya da masa addu'a harta rakosu harabar gidan ita da su Meenal. Kasancewar motocin da zasu wuce dasu suna ta waje yasata jan birki iya nan tana hawaye. Rungumeta Sa'a tayi itama tana hawayen, dan harga ALLAH tanason Zinneerah. jitake kamar karsu rabu a yanzu, amma yaya zasuyi da ƙaddarar aure sai haƙuri. Tanaji tana gani suka wuce su Bahijja suka tafi rakasu har waje. Jikin bango ta lafe hawaye na cigaba da sakko mata, ɗan kwana ukun can da taje tayi a Danya sam ba isarta sukai ba, musamman da ayanzu baba ya samu ƴancin kansa daga hannun Inna, sai taji inama tana a zaman gidan ne har yanzu. Dawowar su Bahijja ya sata share hawayenta suka koma ciki suna mata tsiya ƙasa-ƙasa gudun kar Yayansu yaji. Ita dai hararsu kawai tayi dan basusan yaya takejinta bane. Da taimakonsu ta gyara falon, suna ƙoƙarin dasa zaman hira AK ya shigo. Tsit sukai daga dariyar zancen Meenal dake basu labarin abinda wata innarsu datazo daga bauchi tayi a sashen Granny yau da safe. “Ku baku wuce ba?”. Ya faɗa idonsa akan Zinneerah. Meenal ce tai ƙarfin halin bashi amsa. “Yayanmu muna nan sai anjima, dan ƴan bauchi ma zasu zo suyi muku sallama”. Baice komaiba sai kallon agogon hannunsa da yayi ya sake duban Zinneerah. “Ni zan fita, Khalipha zaizo da mai gyaran ruwa dake fita ta baya, idan sun gama ki ɗauka masa kuɗi a ɗaki saman bedside drawer”. Kanta ta gyaɗa masa da cewa “to” idanunta a ƙasa. Daga haka shima ya juya ya fita a binsa suna masa a dawo lafiya. Sai da suka tabbatar da fitar motarsa a gidan sannan bakin su Meenal ya buɗe. Suka sheƙe da dariya suna tafawa da faɗin, “Soyayya ruwan zuma. Abin mamaki Yayanmu da auta a gado ɗaya”. Hararsu kawai Zinneerah tayi ta ɗauke kanta. Bahijja ta kamo hannunta murya ƙasa tace, “Tawan dan ALLAH da gaske ɗaki ɗaya kuka kwana da Yayanmu a gidan nan?”. “Ya ilahi”. Zinneerah ta faɗa tana zaro idanu, sai kuma ta rankwashi kan Bahijjan da faɗin, “Kirasa a waya ki tambayesa mana, wai yaushe kuka lalace haka ne?”. “Karkiga laifinmu, tunda kema jiya Yayanmu ya lalataki a gado muma gara dai ku guntsa mana kafin a kaimu dan wlhy nima aure nakeso”. Cewar Meenal tana wani karya jiki. Bahijja tai zaram tana faɗin, “Haɗa dani ƴar uwa”. Kallonsu kawai Zinneerah take baki buɗe, suko ko'a jikinsu. A haka su Jamal suka shigo suka samesu ɗauke da abincin rana, yanzu kam a sake suka shigo dan sunsan sun baro boss a can gidan. ___________________★ A ɓangaren su Farah kam lafiya lau ta farka yau, sai dai tunda ta tashi hawaye basubar sauka mata a idanu ba, sai faman sambatu take akan dan ALLAH suce mata mafarki take bada gaske AK yayi aure ba. Da farko daga Mammah har Mahma lallashinta sukeyi, ganin abun nata bana ƙare bane yasa Mahma fara mata masifa. “Ke dan ALLAH kin ishemu haka nan, ba'irin wannan ranar ake hanngo mikiba ana nuna miki hanya kina kaucewa. Ni bansan wane irin rashin hankali ke damunku ku yaran yanzu da bakwa aiki da tunaninku ba. Abinda kawai kuka ɗauka idan namiji na sonku dolene ya cigaba da sonku, kun manta ita soyayya ado ce a cikin aure, a duk lokacin da ɗiya mace ta kasa toshe ƙofofi da ramukan ginshiƙan aurenta adon soyayya zai disashe. Duk yanda zakiso miji ki nuna ƙin danginsa rayuwar aurenki na cikin matsala koda kuwa su suna nuna miki basa son nakine ƙiri-ƙiri a gabansa. Koda shike kawo miki sukar danginsa ki faɗi alkairi da tausar zuciyarsa karki yarda ki tofa mara daɗi. Kiyi haƙuri da halayensa ku kashe ku rufe a ɗakinku dan kai ƙarar miji ga iyayenki ko nashi na zubar miki da kima, ke hatta ƙawayenki kikace ke kullum ƴar fallasa asirin gidankice da niyyar neman shawara to kina cikin kwan gaba kwan baya kuwa a garesa da zubar muku da kimar aurenku. Domin shi aure ibada ne ba komai ake samu hundred percent a cikinsa ba. Dole yau ayi dariya gobe kuka, jibi rabi da rabi tsakanin ɓacin rai da farin ciki. Sannan duk son da namiji ke miki kika nuna zaƙewa da yawa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182