Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 94

Chapter 94

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,279 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

zakiyya saita ringa nuna maki kulawa da miji,shi namiji dakike gani yana son tarairaya wajen matarsa musamman ma irin mazajenku,naga abun naki yana neman wuce misali,saikace ba wayyaya ba kinsanshi ya sanki batun yau kuke tare ba,idan kikai sake yadda yakeda farinjini zakiji asalansa.inasonki sosai ina maki kallon danake wa su ni,ima da zakiyya.kiyi koyi dasu yadda suke yi dani kema kidaukan kamar mamanki zanfi jin dadi.nima abunda uwa zata fadama yarta dan gyara zamantakewarta zan gaya maki don inasonki da Abdoul,kuma ina ganin yadda yanmata suke kara kaina akanshi bazanso hankalin yayi wajen wata ba bacin ke gaki,kisaki jikinki kinuna mashi soyayyar dakike mai da yadda kike kewarshi hakan zai dauke hankalinsa da tunanin kinbar sonshi,don haka zanba zakiyya amanar kula mun da lamarinku in naji sabanin yadda nakeso zan bata dake" Sadda kai tayi tana murmushi tace"mami shine fa yake wani dixgani wai nace bana sonsa,kuma wlh niba haka bane" Me zakiyya xatai ba dariya ba ita da ni ima mami tayi masu dakuwa"kunga naku kason,zakuyi mun shiru koko" Rage dariyar sukai zakiyya na boyewa tana yin abunta.mami ta jiyo ga fiyah tace"dayace haka aiba biye mashi zakiyi ba,alokacin saiki nuna mashin kina sonsa din bawai kitayashi nuna hakin ko in kula ba,don haka zagewa zakiyi kizama jaruma yadda zaiyyi alfahari dake kibar wanan sanyi sanyin bana sonshi" Daga kai tayi tana murmushi. Xakiyya tace"zamushiga lesson time to time ko amaryar yaya Abdoul" Harararta nai ina dauke kai. Taya mamin shirya kayansu muka cigaba dayi tana janmu da fira don nasake dasu,kuma nai kokarin yin hakan ina biyesu muna hira da dariya,har time na dora sanwa yayi nida zakiyya muka shiga kitchen din bayadda mami batai ba akan mufito zatayi amman muka kiya. Abinci mai lafiya muka sarrafa dan danan sai kamshi,mami da ni,ima na cewa sun kagara suji sunfara xubashi cikin cikinsu,haka suka yini cikin farin ciki suna farantawa junansu,Abdoul baidawo da rana ba malik ne kawai sai su Abbi,don yana ta son maido kasuwancinsa london mami tace karya tattago wannan aikin yayi hkr ya bude sabon reshi anan,yake mata bayanin kudin dazayyi asara kafin yafara samun nasara,kuma ahalin yanxu idan yace zai kashe wadannan kudin karshe dole ya saida wancen company na nigeria. Wannan hirar tasu Abbi yaji saiya saka baki yace"yabarwa malik wancen kasuwancin yayi mashi alkawarin bashi duk kudin dayakeso ya bude wani anan london,don yace bazai cigaba da zaman Nigeria ba saidai yaringa xuwa yaa gaidasu,kuma basu takura mashi ba. Hakan yasa yanzu yaketa fafutukar ganin ya samun wurin dazai tsira sabon company,sannan har ya saje bude wani store din saboda anan baifi sati ba,amman kayan nan sunfi nacan kyau da quality dan danan kuma dayake hannunsa yana da sa,a saiga customers daga ko ina ana dibar kaya har daga Nigeria anke xuwa.shiyasa yafara zaman busy. Karfe shidda nayi ya dawo gida lokacin har su mami sun fito daga cikin gidan shikadai ake jira. "Mami har na yi wanka infito ko" Harararsa tai tace "lokacin jirginmu ya jima da tashi idan azaka samu rakamu ba kayi xamanka matarka ma saita tayaka zama" Kallona yayi ina makale da hannun mamin murmushi yayi yana shafa kai yace "aa meyayi zafi kushiga muje su Abbi nacan munyi waya dasu" Malik yaga fiyah na niyar shiga wajen da mami ta zauna yayi dariya yace"hajiya fito ga mijiki can kiketa likemata dake za,a koma ne" Dariya sukeyi shida zakiyya,ahankali ta fito tana cewa"mami kimasu magana" Itama murmushin tai tace"kyalesu zangyara masu zama" Kamar wadda kwai ya fashewa aciki haka ta isa wajen motar ta shiga,sannan suka dauki hanyar filin jirgi. "Sannu da dawowa" Ta furta mashi hankalinsa yana kan titi. "Na zaci ai bakiga shigowata ba,meyasa kikeson canza dabi,arki kokuma ince kikeson juya alakarmu,na dauka kina sona ina sonki akai mana aure amman yanzu kina nuna cewar kamar tilastaki akai bakiso,kina behaving like wata yar ruga kinsan muhimmancin aure kinsan girman miji kinsan hakkinsa kinsan komi akan dawainiyar gidan aure,ke dalubar ilimice kila ma zaki fini sani akan wannan fagen why kike haka" Duk saitaji ta muzanta tabbas abunda ya fada hakane,ni kaina ina mamakin yadda nake mashi bacin irin yadda nakejin sonsa cikin raina,amman sainake ganin ai shine ya fara nuna mun haka. "Kayi hkr ganinai daga gareka" "Shine saiki biyemun?SOFIYYA! idan kina ganin antakuraki aurena dake why bazaki sanar dani ba." Gabanta yafadi sosai muryarta kamar zatai kuka tace" meyakawo wannan maganar" "Taya bazan kawota ba bacin kina nuna man bakisona baki damu dani ba" Muryarta tayi rauni sosai tace"wlh ni ba haka bane idan da kasan halin dana shiga danake shirin rasaka bazakace mun bana sonka ba,plss kabar cewa haka." Yaji dadin maganarta sosai har hakan yakusa nuna ga fuskarshi,amman sai ya dake don tasan cewar ba wasa take ba kuma baya son yadda take tafiyar dashi. "Taya Zan sani tunda ba ganinki nake ba,kuma ai bazan tabbatar ba tun yanzu dakika samenin sai kike nuna mun halin ko inkula,idan hakan ta cigaba da faruwa zuciyata zata karkata xuwa wani wajen,tunda ke kin nuna bakisona" Baiyyi mamakin jin shashshekar kukanta ba don yasan zatayi sarkin kukace ai,muryar tana rawa tace"wlh ba haka nake nufi ba,don Allah kayi hkr wlh na damu dakai daidai da second baka taba barin xuciyata ba,ina son.............shiru tai ta duke tana kuka son ranta. Murmushi take yanajin wani irin dadi yana dawainiya dashi,abunda yadade yana jira wadannan kalaman daga bakinta,kullum sai jamashi rai take vata fada ba saida taji wuta uffan baice mata ba har suka isa filin jirgin,goge fuskarta tai sosai don kar agane duk da haka daka kalleta kasan tayi kuka. Bata jira ya bude mata ba ta fito ta wuce wajensu mami,bankwana suka shigayi dasu sunajin kamar karsu tai mami tace "diyata waye ya taba man ke" Rungume mamin tai tana fashewa dakuka don abun biyu ya hade mata bata son mamin ta tafi ga kuma kalaman sa daya gaya mata masu kona xuciya. "Mami bashi bane ya sani kuka" Gaba daya dariya suka saka masu harda su Abbi da dady,murmushi mamin tai tace"mekika mashi" Bazata iyacewa ba dole ta gilla karya. "Cewafa yayi inkikatai zairinga gasa man aya ga hannu" Dariya kurin suke masu shikanshi Abdul din dariyar yayi abun ma saiya bashi sha,awa takuma burgeshi yadda take kukan shagwabar. Kiransa mami tai tace"xonan son" Takowa yayi ya iso ta dagoni daga kafadarta ta kama hannuna ta saka cikin nashi ta dan sha mur. "Ko kwarzane nagani jikinta saika gaya masu,don haka ka kulamun da diyata." Rike hannun yayi gam yana jawoni gefen kafadarsa yace"insha Allah karkisha damuwa saikinyi mamakinta kince menake bata idan kika ganta." "Haka nakeson ji kaima malik ka kulaman da diyata banason inga ta rame ko kadan ta rike hannunsu ta saka masu albarka sannan suka sake bankwana,ni,ima tana cewa"Anty zakiyya Anty safiyyah kuyomun tsarabar babies kafin kudawo" Dungure mata kai mami tai suna dariya har suka shige jirgin,malik yace"kinjito abunda qanwarki tace" Gaba tai tabarshi tana cewa"abunda ma wanda zaibayar da babyn baishirya ba waya sani ko tsorona yake" Ta fada tana darita biyota yayi dagudu itama ta karasa cikin mota da sauri don tasan sauran idan ya kamata, Yace"insha Allah shigar farko zan xuba twins shiga ta biyu kuma triple shiga ta uku.........rufe mashi baki tai tana bashi hkr suna dariya

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});