Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 85

Chapter 85

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,273 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

gefe suna magana akan matsalar data faru uncle yana bada shawara da fadar yadda yadace.................haka aka bar mama wajenta yesmin zataje ta shigar mata exam don yau suke ta karshe tana adduar Allah yasa ta iya ansa mata question din daidai,don bata san me za,a tambaya ba.duk yadda baban yaso magana da mama kiyawa tai saidai ta kauda kai kurin dole suka wuce gida suka kyaleta.dalha ne zai kawo mata kalacinta,Anty jamila tace zataje tayo wanka sai tadawo tataya mamar zama. ************* Duk inda hankulan iyalan Alh muazzam yake yakai kololuwar tashi,don kuwa ga Abdoul nan kwance gamar gawa baya numfashi,likitoci ukune kanshi suna bakin kokarinsu amman Abbi gani yake basu yin komi zarya yake bakin kofar dakin yana leke ta glass din kofar,daga can kuma mami ce dasu ni,ima zakiyya da malik kuka kurin suke,malik ne keta kokarin nuna dauriya.........dadyne ya iso shima cikin damuwa yake tambayar abi abunda yake faruwa kasa mashi bayani yayi yana kwalla,malik ne tace "dady duk ta kare yaje gidan su safiyya ne babanta ya korai kokuma kai tsaye yayi mashi iyaka da ita,abunda zai ita jefashi cikin wannan halin kenan don Abdoul yana ma safiyya soyayya mai zafi,rasata kamar yana barazanar shina rasa tashi rayuwar don gaskita cikin kwanakin nan inaganin canji sosai tare dashi,alamun sunriga sun daidaita da ita yarinyar gaskiya abunda nake zaton zai jefa shi cikin wannan yanayin kena" Xunbur Abbi yatashi zaifice dady yarikoshi "ina zaka?badai koma wa zakai ba duk irin abunda ya gaya mana rannan" Kamar abbi zai kuka yace"Abdullahi ina son rayuwar dana shekara nawa bana tare dashi,sai lokacin da komi ya wuce kuma wata matsalar xata shigo,zanje karo na uku na sake rokonsa kome yake son nai mashi inhar zaibarsu su auri juna wlh zan mashi,koda cewa yayi inkwanta ya bita kaina" Ficewa yayi dadyn ya bi bayansa don yana iya cewa acikin wannan halin zaija mota. ************** ***************** Fiyah cikin kwana uku tatashi ta samu sauki,ta dauki hkr ta sama xuciyarta amman fa ta rage walwala sosai da sosai don saita yini cikin daki bata fito ba idan ba wani abun xatai ba,zaka samu kowa tsakar gida amman ita tana daki babu yadda mama batai ba,babu irin lallashin da batai ba amman fiyah ta kasa dawowa daidai,abunda ya taba yesmin da mamar kenan shi kanshi baban yanajin babu dadi,shiyasa yaketa kokarin jawota jikinsa ko zata sake saidai murmushi kurin duk maganar da zakai mata idan har ba yazame mata dole ba bazakaji muryarta ba.tun Anty jamila na fushi da ita harta sauko tana jan yar uwartata jiki,jalal kau ko kallon inda yake batai ko ya mata magana uffan bata ce mashi.ana cikin haka aka saka ranar yesmin da muhseen alokacinne baba ya kira fiyah dakinsa da safe bayan angama karyawa. "Uwata kinsan dai nine mahaifinki ko,kuma kinsan irin son danake maki bazan yi abunda zai cutar dake ba,duk abunda zanyi inayine don martabarki da kimarki yanzu ma wata alfarma nakeso daga gareki" Dagowa tai tana kallonsa da fararen idanunta fuskarta ta saki daka kalleta kasan tana cikin damuwa don har wata irin rama tai. "Baba ni banace kayimun ba daidai bane,kawai inakokarin ganin na manta da komi zan dawo daidai kuma komi kake son yankewa akaina baba basai ka nemi alfarmata ba kana da ikon yanke hukuncin duk da ka ga dama akan rayuwata" Wani tausayinta yaji ya dirar mashi har kwalla ta cika idonsa "shikenan uwata Allah yayi maki albarka Allah ya albarkaci rayuwarki,wanine keson aurenki harna bashi dama ya turo iyayensa don harna yanke hukuncin saka rana guda keda yar uwarki,nan da wata uku idan Allah ya kaimu" Wani irin bugawa kirjinta yayi dan danan kanta ya sara damn ciwo yake,daker take jawi numfashinta ta dake sosai tace"Allah ya sa haa shine mafi alkairi baba" Tatashi tafice tabarsa yana binta da kallo,mamace ta shigo cikin tashin hankali take kallon baban "mekake shirin yi babansu?waikai bakajin digon tausayin yarinyarnan shin wace irin xuciya ce dakai babansu,inajin yaron nan har yau yana asibiti karshe dole aka fitar dashi kasar waje,duk da haka bazaka tausaya masu ba.har gida iyayensa suka zo suna magiya da roko amman vanji kace masu komi ba,gaskiya idan ka aurar da safiyya ga wani ba wannan yaron ba ka cutar dasu,kadaina ganin bata maka gardama Allah kadai yasan kuncin da kasasu baka tunanin Allah ya tambayeka.................ya i sheki nace ya isheki hakanan,ke zaki gaya mun abunda zanyi inace nima yatace,gaya maki kai ba nasonta?kinfini sanin daidai da ba daidai ba?to kinga daman kyaleki nake akan wannan abun,tunda akafara maganar nan kiketa mun wasu halaye marasa dadi safiyya dai yata ce kuma nine nakeda alhakin zaba mata miji wanda yake daidai da rayuwarta,don haka wannan yazama na karshe inajin kinji me nace" Ya saka hularsa ya fice yabar gidan. Tunda mma tazo gidan nan matsayin matarsa magana kwatan kwacin irin wannan mai zafi da daga murya baitaba mata ba,duk sabaninsu zasuyi abu su surufe sushirya babu wanda ya sani,kuma kullum suna cikin fahimtar juna daba juna uxiri,amman saigashi yazu da girmansu suke irin abunda baidace ba,har yaransu sunaji. Kukan da mama ta manta batai ba shine take yi,suma can fiyah da yesmin kukan suke,don basu tabajin irin haka da iyayen nasu ba. Fiyah naji nagani aka shiga shirye shiryen bikinsu itada yesmin,tun tana kuka tana damuwa tana kuncin,har ta shanye tazo ta zama kamar abun baya damunta,gidan koda yaushe da mutane yanuwan mama dana baba ana hidimar hada gara su cincin da dublan da alkaki da sauransu,shiyasa ma bata zama gidan tana gidan inna balaraba wajen hasana,ko tatai wajen feea. Wannan kenan...... Tunda akaga ciwon Abdoul ya gagari likitocin na Abbi yayi visa suka tai suduka can Australia wajen dr Abdoul din da yataba dubashi,don sunce xuciyarsace ke ciwo duk sanda zata halba dole zai sume saboda bata da isassar lafiya. Kuka kau mami sun shashi har idonsu ya kekashe,zakiyya tuni ta nemi fushin da take dashi ta rasa kullum suna cikin yi masa addua Allah ya tashi kafadarsa,sai ya zamana malik ne dan lallashi da nasiha da ban baki acikin sati ukun da sukai Australia sabo da fahimta ya shiga tsakanin zakiyya da malik,saboda shi ya ansa zai auri zakiyyarne don ya saukakama Abdoul matsala don tabbas yasan zai sabi fiyah akan zakiyya,shiyasa shikuma yaga yadace asamu mai lallashinta mai tausaya mata,don zakiyya ta cancanci wadannan abubuwan tarasa mahaifiyarta ta rasa masoyinta da tayi shekaru aru aru tana dakon sosan,amman zamanta da malik akai akai yana yawan yi mata nasiha da jawo hankalinta yana nuna mata cewar komi na rayuwa dan hkr ne,kuma duk abunda karasa arayuwarka ka dauka hakan alkairine,Allah yafimu sanin daidai da ba daidai ba,yana duba mana abunda zai zama alkairi arayuwarmu bisa ga wanda muka kwallafa rai. Komi yafaru da bawa dama can rubutaccene kariga karubuto abunka tun cikin ciki,shiyasa kafi son duk abunda kagani to ka godema Allah kayarda da wannan kaddarar don yarda da kaddara mai kyau ko marar kyau imanine...........da haka malik ya jawo hankalinta kanshi,duk da sudukan babu maijin son wani amman akwai kulawa da fahimta tsakaninsu,haka mami ma take yawan yiwa zakiyyar nasiha akan rayuwa da kuma alakarta da malik,don tagaya mata muddin ta rasa shi ba fata take mata ba samun irinsa zaiyyi wuya. Ansamu cigaba ta bangaren lafiyar abdoul don

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});