Chapter 27
Chapter 27
kallo kamar ya canza mashi,alhalin ko kadan ma bashi yake kallo ba,in zaka tirkeshi bazai iya cewa ga abu da yake kallo ba,tsabar tunanine kawai,zuwa lokacin ya sausauta fuskarsa kodan mutanen da zai hadu dasu amman ba dan yabar jin wanan ciwon cikin ran saba,babu wanda yayi magana dashi ko saud'aya saidai hannu dayake anfani dashi wajen maganar,ko kuma fuskarsa da zai canza ma salo alamun dai bayar da ansar maganar da ake mashi. KO kadan baison magana da kowa abunda yake damunsa kadai ya ishesa,koda suka isa hotel din mutanen suka kai mashi kayansa har room din da suka kama mashin,sannan suka tbayai yana bukatar wani abu yayi masu nuni da coffee kawai yake so.har wanda yaba umurnin coffen ya juya sai yadawo don yasan idan yazo irin wannan time d'in yana buk'atar mutuniyar tashi cikin ladabi yace"sir what of win?" Idanunsa daya kalla yasa yayi saurin kauda kai,shikuma cikin fushi yace"I said only coffee." Aguje yafita don sun san hali yanzu zai ci uban mutun babu wasa. Zubewa yayi kan gafo yana kallon sama ko combus dinsa bai samu damar cirewa ba,ya runtse ido yana juya kai don kan nashi har ciwo yake masa,cikin wata irin so cool vioce yace"banzar yarinya kawai,win din zan sha ke nayi maki fyaden bayan na gama bulbula maki ita cikin ciki,wawuya kawai........zuwaan kuma wani killer smile ya kubce masah ni kaina saida yaban mamaki,saboda yadda yayi masifar fiddo masa duk kanin madarar kyansa cikin wani sauti yake magana kamar mai rad'a. "Da Idonta kamar nawa,dakin sake kinsha ta sai uwarki ko ubanki ya yankaki,kafin kisanar dashi inda kika samota mts!yarinya yar mitsila ta samun rud'ani cikin kai." Maganganun malik ne suka fara masa jeran giya,akwai maganar daya fad'a data sashi cikin shakku. _Abdoul idan kasake wani abu yasamu yar mutane zaka sha mamaki na don wlh zan cire sanayya nayi maka rashin mutuncin da baka tab'a tunani ba_ "Me Malik yake nufi?meya had'asa da wannan yarinyar......" Runtse idon sa ya sake yi wata maganar tasake shigarsa kenan.........aka turo k'ofar dakin mutumen daya zo dazun tambayarsa abunda zaisha. Cikin ladabi yace"sir.......bai bari ya idasa ba yace"drop it inside" Yaje ya ajiye ya fita ya barsa. Mirginawa yayi ya yi rubda ciki yana sauke numfashi yana jiyo muryar Malik cikin kunnensa. _yarinya tana iyakar kokarinta duk don kai duk don kadawo cikin hayyacinka,kagane daidai da ba daidai ba.amman naga alamar so kake ka nakasta yarinyar mutane._ Tashi yayi zaune dafe da kanshi da yake tsananta ciwo. "Mekenan,ina bukatar nazari ina bukatar sanin komi kar tunani ya tarwatsamun k'walwa." Wata xuciyar tace kaida kullum kake neman abunda zai kawo maka mutuwa aida kacigaba da tunanin. Mik'ewa yayi yana jan tsaki kamar da wani yake magana cikin jin haushi yace"to ina ruwanki yanzu kuma na canza ra,ayi." (đđwlh Alfah ya zare) Wannan daren saida Alfah yayi da gaske kafin bacci ya iya surarsa,don yana da tarin tambayoyi bila adadin da yake bukatar amsar su.amakare ya tashi wajen six sannan yayi salla yana jin haushin rashin yinta akan lokaci ba. Bayan ya yi sallar wayarsa ya dauka ya soma kiran malik wanda jiya bai samu damar kiran sa ba ya gaya mashi ya iso lfy. Malik baccin sa ma yake don shi tun biyar daidai yayi sallar sa kuma cikin jam,i ya samu ladarsa full 27. Ihun wayar yakeji daker yabude ido ya lalubota don jiya bai samu kwamciya da wuri ba saboda aikin da yasha kan computer don yau karfe goma inya fita zuwa company shida dawowa gida kuma sai six. "Sai yanzu ka kirani yallabai" Cewar malik dake kwance cikin lumtsetsiyar katifarsa. Abdoul kamar baya so yake amsa shi "Ya kake?" Murmushi malik yayi yace "yarda kake to,ina tambayarka kana sharewa." Numfashi ya sauke yace"na sauka ban da caji,and kaina naciwo shiyasa na kwanta da wuri." Jinjina kai malik yake yana jin duk sauran baccin yana fita daga idonsa,wani dadi ya kama malik,indane Alfah bazai iya masa magana har haka ba zaidai kirashi cikin shan k'anshi kalma guda zai furta mashi ataikaice cewa"na iso ba saika korani ba." Amma yanzu har yana gaya mashi halin da yake ciki.cikin jin dadi yace "don Allah karka wuce kwanakin da kace don gidan yayi man girma." Maimakon yaji ya gwalesa ko yaja tsaki ya kashe wayar sai yaji sab'anin hakan........."bazan wuce ba kilan ma kwana uku ya wadatar ka kula da kanka zanje yanzu na idasa abunda zanyi nafita." Ya kashe wayar baijira me malik din zaice ba,shikanshi Alfah ya jimabyana kallon kansa ga mirrow,mamakinsa yake yadda ya canza daga jiya zuwa yau,shikansa baisan meyasa maganganun yarinyar sukai tasiri har haka cikin ransa ba,amman yazayyi ba umurnin kansa bane na zuciyar sa ne. Mrs bb ce Mom muhssen [9/17, 3:37 PM] Fauziya Madaki: đđđđđđđ *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* đ żď¸.........21 Cikin kwana kin da yayi Australia jinshi yake daban,saboda yadda duk d'abi arsa suke son juyewa sukoma wasu kala dabam,tunda yazo sau d'aya yasha mutuniyarsa,itama kuma baita zauna ba saboda rashin bawa kansa hutu da ishashshem bacci yasa masassara ta kamashi,randa yashata kwana yayi yana amai jikinsa kamar an masa dukan bala,i........daga lokacin bai sake nemanta ba yana son yasha amman daya kai bakinsa kalaman yarinyar da ko sunanta bai sani ba suke dawo mashi ras,kamar lokacin take sanar dashi su. Fiyah kau saida tayi jinyar kwana uku bata je ko ina ba,da yake juma,a ne kurin ba taje makaranta ba sauran kwanakin anshiga weekend ne. Baba ya wartsake ya koma hidindumun sa na yauda kullum,ya fita batun Alh muazzam don yanzu zaman lafiya yafie mashi komi da kuma zama cikin iyalinsa,tunda yagane cewar inhar baka dashi to kau kaine wulakantacce,ko da kuwa kwana kake masallaci kana sallah.duniyarce ta lalace anzo wani zamani da saidai ace innalillahi wa inna ilaihir raju,un. Feea kuwa tana can tan fama da dakon soyayyar Abdoul,ga shirye shiryen bikin Abbanta babu abunda akafasa,don kamar baitab'a aure ba haka yakeji komi na gidansa an sakeshi......har lokacin kuma mominsu bata dawo ba. B'angaren fiyah da Malik kuwa suna waya sosai don duk rana zai kirata da safe suyi kusan minty talatin suna waya,sannan yakira da rana ya kuma kira da daddare,shakuwa ta shiga tsakanin su sosai fiyah ta sake dashi har idan bai nemeta ba tana kan gaba wajen nemansa.........ana gobe Abdoul zai dawo Anty jamila ta haihu ansamu baby girl. Fiyah ta shirya kayanta itace yar zaman bakwai,har rigima sukai da yesmin akan ita zata fiyah tace"keda kin cika lalacin tsiya me zaki tsinana mata dallah matsa mun." Mama tace"Ato nidai ai bazan tura ku kudu ka ba kamar wata wadda bata da hankali,kume ke safiyyah ai ga makaranta da hkr kikai tunda ita ta gama zaman banza take." Silalewa kasa tayi tana dirje dirjen kafafu don yau rigimar takeji bilhaki da gaskiya "wallahi mama dama nasan saikin kware mun baya,kullin saikin nuna ni baki goyon bayana tsakani da Allah nida nake babba ai ni zakice intai." Yesmin tace"kiyi hkr Adda wlh ni daman janki nake don inji me zakice." Ta fada tana dariya mama na taya ta kallonsu take tama kasa cewa komi mama tace"kinji kunya wlh safiyyah kullum ke bakida wani girma saina jiki." Ranar da daddare bayan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101